Leadership News Hausa:
2025-04-30@19:44:05 GMT

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

Published: 27th, April 2025 GMT

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

Kazalika, a cikin daukacin gwamnatin tarayya da kuma na jihohin kasar, an tsara yadda za su dakile kalubalen da fannin aikin noma da kuma yadda za a sama wa manoman kasar sauki, bunkasa rayuwar mazauna karkara da kuma habaka tattalin arzikin kasar.

 

Akasarin manufar aikin na SAPZ shi ne, domin inganta aikin noma a karkara, maimakon fitar da amfanin gona kamar irin su Rogo, Shinkafa, Tumatir da kuma Koko zuwa birane ko kuma kasar waje, za a tanadar da kayan aiki a yankunan da aka tsara za su amfana da shirin, domin manoman yankin su samu ribar da ta kamata.

 

Daya daga cikin manyan matsalolin da ake samu a Nijeriya ita ce, gibin da ake samu a bangaren aikin noma domin samun riba.

 

Amma a wadannan yankunan da za a gudanar da aikin, za a samar da masana’antun sarrafa amfanin gona, kayan adana amfanin gona, wutar lantarki mai dorewa, tituna da kuma cibiyoyin bayar da horo.

 

Nijeriya dai, ta shafe shekaru tana fama da karancin abinci, asarar da manoma ke tabkawa bayan sun yi girbi da kuma matsalar rashin aikin yi a tsanakin ‘yan kasar.

 

Har ila yau, aikin zai kuma samar da damar fitar da amfanin gona zuwa ketare, wanda hakan zai samar wa da Nijeriya biloyin Nairori.

 

Ta hanyar aikin na SAPZ, Nijeriya za ta iya samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar, rage asarar da ake fuskanta duk shekara, bayan girbe amfanin gona da kudinsu ya kai kimanin Naira tiriliyan 3.5, samar da ingantacce wajen adana amfanin gona, samar da cibiyoyin bayar da horo ga manoma da kuma cike gibin da ake da shi a kasuwannin kasar.

 

Kashi na farko na aikin, an kaddamar da shi ne, a 2022, ta hanyar ware dala miliyan 538, wanda kuma za a wanzar da shi a cikin akalla sama da shekaru biyar.

 

Aikin na Bankin AfDB, zai samar da dala miliyan 210, inda kuma Bankin IsDB da IFAD, za su samar da dala miliyan 310, sai kuma gwamnatin tarayya da za ta samar da dala miliyan 18.05.

 

Jihohin Da Za Su Amfana Da Aikin:

Jihon da za su amfana da aikin su ne; Kaduna, Kano, Kwara, Kuros Riba, Imo, Ogun, Oyo, sai kuma Abuja.

 

A yanzu dai, Shugaban Bankin AfDB, Akinwunmi Adesina da kuma Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ne, ke jagorantar aikin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: dala miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani

Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Duk wani harin wuce gona da iri kan Iran zai fuskanci mayar da martani daidai da shi cikin gaggawa

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa Iran na da kwarin gwiwa kan iya dakile duk wani yunkuri da wasu bangarorin ke yi na kawo cikas ga manufofinta na ketare.

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Rudun gwamnatin yahudawan sahayoniyya, wadda take ganin za ta iya gindaya wa Iran abin da ya kamata ko kuma bai kamata ba, rudun tunani ne da ya yi nesa da hakikanin gaskiya, ta yadda bai cancanci mayar da martani ba.

Araqchi ya kara da cewa: “Duk da haka, jajircewar Netanyahu wani abin lura ne, a yayin da yake kokarin neman bayyana wa Shugaba Trump abin da zai iya ko kuma ba zai iya yi a diflomasiyyarsa da Iran ba!”

Ministan harkokin wajen ya yi nuni da cewa: “Abokanan Netanyahu a cikin tawagar Biden da ta gaza – wadanda suka kitsa makarkashiyar hana cimma yarjejeniya da Iran – suna kokarin nuna zaman tattaunawar da ake yi ba na kai tsaye ba da gwamnatin Trump a matsayin wani kuskure ne kuma tamkar hoton sauran yarjejeniyar nukiliya ce da aka gudanar.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu