Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma Francis
Published: 27th, April 2025 GMT
Dubun dubatar mutane mabiya Addinin Kirista ne suka yi cikar ƙwari a jana’izar ƙarshe da ake yi wa jagoran ɗarikar Katolika, Fafaroma Francis, a cikin yanayi na matakan tsaro.
Hukumomi a birnin Roma sun tsaurara matakan tsaro a ciki da wajen St. Peter’s Square na Fadar Vatican, inda ake gudanar da jana’izar Fararoma Francis.
Tun da sanyin safiya dubun dubatar jama’a suka yi wa dandalin cikar ƙwari domin samun damar yi wa Fafaroma Francis ganin ƙarshen a jana’izar da ke zama guda a cikin mafi girma a duniya.
Mutum dubu 400 sun halarci jana’izarAƙalla mutum 400,000 ne suka halarci jana’izar Fafaroma Francis a dandalin St Peter’s da ke Vatican.
Haka kuma sun ga lokacin da aka ɗauki gawarsa zuwa wajen da aka binne shi a cocin Santa Maria, a cewar Ministan Harkokin Cikin Gidan Italiya.
“Mun yi ƙiyasi cewa mutane 400,000 ne tsakanin waɗanda suka halarci dandalin St Peter’s da kuma waɗanda suka tsaya kan tituna suka kalli jana’izar,” in ji Matteo Piantedosi.
Shugabannin duniya da suka halarci jana’izarShugabannin manyan kasashen duniya ciki har da na Faransa da Amurka da wasu jagororin gwamnatoci ciki har da na Jamus da Burtaniya da fitattun sarakunan duniya irinsu na Jordan, duk sun halarci jana’izar.
Shugaba Putin bai samu halartar jana’izar ba, amma kuma takwaransa na Ukraine Volodymyr Zelensky ya halarta dandalin na St. Peter’s don yi wa Fafaroma Francis ganin karshe.
Daga cikin fitattu a dandalin St Peter da safiyar ranar Asabar akwai Yarima William na Birtaniya da shugaban Amurka Donald Trump da wanda ya gada, Joe Biden da Firaiministan Birtaniya, Sir Keir Starmer da kuma shugaban Faransa Emmanuel Macron.
Jana’izar na zuwa ne bayan kammala yi wa gawar Fafaroma ganin bankwana na tsawon kwanaki da wasu dubban mabiya ɗarikar ta Katolika suka yi a cikin yanayi na juyayi da alhini.
Fafaroma na farko da aka binne a wajen Vatican cikin shekaru 100Fadar Vatican ta tabbatar da cewa an binne Fafaroma Francis a cocin Santa Maria Maggiore.
“Fafaroma Francis shi ne mutum na farko cikin shekara 100 da aka binne a wajen Vatican, kuma an binne shi a asirce, inda makusantansa suka yi masa gaisuwar ban-girma,” a cewar sanarwar da fadar ta fitar.
Shi ne Fafaroma na farko tun bayan Leo XIII, wanda ya mutu a 1903 — da aka a binne a wajen Vatican.
Kowane lokaci idan ya koma birnin Rome daga balaguro, ya sha ziyartar Santa Maria Maggiore.
Cocin dai yana wajen Vatican da ke tsakiyar birnin Rome.
Mutumin farko daga Latin Amurka da ya zama FafaromaƊan ƙasar Argentina, wanda ya yi jagorancin majami’ar Katolika tsawon shekaru 12, ya mutu ne a ranar Litinin da ta gabata yana da shekaru 88, bayan fama da mutuwar ɓarin jiki da bugun zuciya.
Kiraye-kirayen zaman lafiyaFrancis ya sha yin kiraye-kirayen kawo ƙarshen rikice-rikicen duniya a zamanin jagorancinsa, kuma jana’izarsa ta bai wa shugaba Trump na Amurka, wanda yake koƙarin kawo ƙarshen yaƙin Rasha da Ukraine damar ganawa da takwaransa na Ukraine, Volodymyr Zelenskiy a cikin majami’ar Saint Peter Basilica.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fadar Vatican Fafaroma Francis halarci jana izar Fafaroma Francis a wajen Vatican a jana izar
এছাড়াও পড়ুন:
Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume
Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ce Najeriya na iya ajiye biliyoyin naira a duk shekara idan aka rungumi tsarin majalisa ta wucin gadi.
Yayin da yake magana a gidan talabijin na Channels ranar Alhamis, Ndume ya ce kuɗin da ake kashewa wajen kula da Majalisar Dokoki a tsarin zama kodayaushe ba zai dore ba, musamman a wannan lokaci da ƙasar ke fama da matsalolin kuɗi da tsaro.
An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra“Kudin gudanar da gwamnati ya yi yawa sosai. Idan ’yan majalisa suka zauna na wucin gadi, gwamnati za ta ajiye biliyoyi,” in ji shi.
Ya ce za a iya sauya akalar kuɗin zuwa bangaren tsaro da sauran muhimman abubuwan ƙasa.
Ndume ya danganta tsadar gudanar da gwamnati da manyan ƙalubale da ke hana ƙasar yin nasara wajen yaki da rashin tsaro.
Ya ce Najeriya ba za ta iya jure ɓarnar kashe kuɗi ba a yayin da ake fuskantar ta’addanci a Arewa maso Gabas, ’yan bindiga a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya, garkuwa da mutane, da kuma ƙaruwar laifuka.
A wani bangare na fafutukar rage kashe kuɗi, sanatan ya soki ci gaba da kasancewar ’yan sanda da ke tare da sanataci da sauran manyan mutane duk da umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an tsaro daga irin wannan aiki.
Aminiya ta rawaito cewa Shugaban Ƙasa ya umarci Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, da ya janye jami’an daga aikin kare manyan mutane ya kuma tura su zuwa fagen yaki da ta’addanci da samar da tsaro.
“Amma har yanzu, ’yan siyasa na tare da ’yan sanda,” in ji Ndume, yana kira ga Babban Sufeton da ya tabbatar da cikakken bin umarnin na shugaban ƙasa.
Ya bayyana cewa tura ’yan sanda daga aikin kare manyan mutane zuwa aikin al’umma da na fagen yaki zai ƙara inganta tsaron ƙasa fiye da ɗaure su ga mutum ɗaya.
Ndume ya ce tsarin tsaron ƙasa ya yi ƙunci kuma yana bukatar “haɗa hannaye wajen yin aiki,” yana mai jaddada cewa dubban jami’an suna makale wajen rakiyar ’yan siyasa da masu tasiri waɗanda za su iya rayuwa ba tare da irin wannan rakiyar ba.