Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma Francis
Published: 27th, April 2025 GMT
Dubun dubatar mutane mabiya Addinin Kirista ne suka yi cikar ƙwari a jana’izar ƙarshe da ake yi wa jagoran ɗarikar Katolika, Fafaroma Francis, a cikin yanayi na matakan tsaro.
Hukumomi a birnin Roma sun tsaurara matakan tsaro a ciki da wajen St. Peter’s Square na Fadar Vatican, inda ake gudanar da jana’izar Fararoma Francis.
Tun da sanyin safiya dubun dubatar jama’a suka yi wa dandalin cikar ƙwari domin samun damar yi wa Fafaroma Francis ganin ƙarshen a jana’izar da ke zama guda a cikin mafi girma a duniya.
Mutum dubu 400 sun halarci jana’izarAƙalla mutum 400,000 ne suka halarci jana’izar Fafaroma Francis a dandalin St Peter’s da ke Vatican.
Haka kuma sun ga lokacin da aka ɗauki gawarsa zuwa wajen da aka binne shi a cocin Santa Maria, a cewar Ministan Harkokin Cikin Gidan Italiya.
“Mun yi ƙiyasi cewa mutane 400,000 ne tsakanin waɗanda suka halarci dandalin St Peter’s da kuma waɗanda suka tsaya kan tituna suka kalli jana’izar,” in ji Matteo Piantedosi.
Shugabannin duniya da suka halarci jana’izarShugabannin manyan kasashen duniya ciki har da na Faransa da Amurka da wasu jagororin gwamnatoci ciki har da na Jamus da Burtaniya da fitattun sarakunan duniya irinsu na Jordan, duk sun halarci jana’izar.
Shugaba Putin bai samu halartar jana’izar ba, amma kuma takwaransa na Ukraine Volodymyr Zelensky ya halarta dandalin na St. Peter’s don yi wa Fafaroma Francis ganin karshe.
Daga cikin fitattu a dandalin St Peter da safiyar ranar Asabar akwai Yarima William na Birtaniya da shugaban Amurka Donald Trump da wanda ya gada, Joe Biden da Firaiministan Birtaniya, Sir Keir Starmer da kuma shugaban Faransa Emmanuel Macron.
Jana’izar na zuwa ne bayan kammala yi wa gawar Fafaroma ganin bankwana na tsawon kwanaki da wasu dubban mabiya ɗarikar ta Katolika suka yi a cikin yanayi na juyayi da alhini.
Fafaroma na farko da aka binne a wajen Vatican cikin shekaru 100Fadar Vatican ta tabbatar da cewa an binne Fafaroma Francis a cocin Santa Maria Maggiore.
“Fafaroma Francis shi ne mutum na farko cikin shekara 100 da aka binne a wajen Vatican, kuma an binne shi a asirce, inda makusantansa suka yi masa gaisuwar ban-girma,” a cewar sanarwar da fadar ta fitar.
Shi ne Fafaroma na farko tun bayan Leo XIII, wanda ya mutu a 1903 — da aka a binne a wajen Vatican.
Kowane lokaci idan ya koma birnin Rome daga balaguro, ya sha ziyartar Santa Maria Maggiore.
Cocin dai yana wajen Vatican da ke tsakiyar birnin Rome.
Mutumin farko daga Latin Amurka da ya zama FafaromaƊan ƙasar Argentina, wanda ya yi jagorancin majami’ar Katolika tsawon shekaru 12, ya mutu ne a ranar Litinin da ta gabata yana da shekaru 88, bayan fama da mutuwar ɓarin jiki da bugun zuciya.
Kiraye-kirayen zaman lafiyaFrancis ya sha yin kiraye-kirayen kawo ƙarshen rikice-rikicen duniya a zamanin jagorancinsa, kuma jana’izarsa ta bai wa shugaba Trump na Amurka, wanda yake koƙarin kawo ƙarshen yaƙin Rasha da Ukraine damar ganawa da takwaransa na Ukraine, Volodymyr Zelenskiy a cikin majami’ar Saint Peter Basilica.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fadar Vatican Fafaroma Francis halarci jana izar Fafaroma Francis a wajen Vatican a jana izar
এছাড়াও পড়ুন:
MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP), ta ayyana Najeriya ɗaya daga cikin jerin ƙasashen da za su fuskanci matsananciyar yunwa.
Ta kuma yi gargaɗin cewa ƙarin mutane a duniya na iya fuskantar yunwa saboda ƙarancin kuɗin tallafi.
Rahoton da Hukumar Abinci da Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO) da WFP suka fitar, ya nuna cewa rikice-rikice da tashin hankali ne ke jawo matsananciyar yunwa a ƙasashen da ke cikin hatsari.
DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPPRahoton ya bayyana ƙasashen Haiti, Mali, Falasdinu, Sudan ta Kudu, Sudan da Yemen a matsayin waɗanda ke cikin mafi munin hali inda jama’a ke fuskantar barazanar yunwa mai tsanani.
Haka kuma, Afghanistan, Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo, Myanmar, Najeriya, Somaliya da Siriya sun shiga jerin ƙasashe masu matuƙar damuwa.
Rahoton ya kuma ambaci Burkina Faso, Chadi, Kenya da kuma yanayin ’yan gudun hijirar Rohingya a Bangladesh.
Darakta Janar na WFP, Cindy McCain, ta ce, “Muna fuskantar matsalar yunwa da za a iya kauce mata gaba ɗaya, amma idan ba a ɗauki mataki ba, hakan zai haifar da ƙarin rikici da rashin kwanciyar hankali.”
Rahoton, ya ce kuɗin agajin jin-ƙai yana raguwa sosai, inda aka samu dala biliyan 10.5 kacal daga cikin dala biliyan 29 da ake buƙata don taimaka wa waɗanda ke cikin hatsari.
Saboda ƙarancin kuɗi, WFP ta rage tallafa wa ’yan gudun hijira da waɗanda aka raba da muhallinsu, sannan ta dakatar da shirye-shiryen ciyar da ɗalibai a wasu ƙasashe.
Hukumar FAO kuma ta yi gargaɗin cewa harkar noma na cikin hatsari, wanda shi ne ginshiƙin samar da abinci da hana matsalolin yunwa sake faruwa.
An bayyana cewa tallafi ake buƙata don samar da iri da kula da dabbobi kafin lokacin shuka ko wani sabon rikici ya sake ɓarkewa.