Damfarar CBEX: Mutum 8 da EFCC ke nema ruwa a jallo
Published: 26th, April 2025 GMT
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya EFCC, ta ayyana neman wasu jami’an CBEX waɗanda take zargi da hannu a damfarar ’yan kasar miliyoyin kuɗaɗe a wani tsarin zuba kuɗi.
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da EFCC ta wallafa a shafinta ranar Juma’a.
An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin MusulmiSanarwar ta ambato EFCCn tana zargin mutanen takwas da yaudarar jama’a su zuba kuɗi don samun riba – daga bisani suka tsere da kuɗaɗensu.
Hukumar ta bayyana sunayen mutanen da Seyi Oloyede da Emmanuel Uko da Adefowora Oluwanisola da Adefowora Abiodun Olaonipekun.
Sauran sun waɗanda ta ce ’yan ƙasashen waje ne sun haɗa da Johnson Otieno da Israel Mbaluka da Joseph Kabera da kuma Serah Michiro.
“Muna son sanar da al’umma cewa muna neman waɗannan mutane ruwa a-jallo saboda zargin damfarar mutane a wani tsarin zuba kuɗi na intanet wanda ake kira CBEX,” in ji EFCC.
Hakan na zuwa ne bayan da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bai wa jami’an EFCC ɗin damar kame da kuma tsare mutanen da aka samu da hannu wajen yaɗa tsarin na CBEX.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara
এছাড়াও পড়ুন:
Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka
Shugaban Amurka Donald Trump, ya bayyana cewa yana shirin daina karɓar mutane daga “ƙasashe masu tasowa” gaba ɗaya, ciki har da Afirka, Asiya da sauransu.
Ya bayyana haka ne yayin wani taro da ya gudana a fadar shugaban Amurka.
Ƙasar Japan ta fara sayar da i njin da ke yi wa mutane wankaA cewarsa, tsohon tsarin shige da fice na Amurka yana rage ƙarfin tsaron ƙasa kuma yana matsa wa makarantun gwamnati, asibitoci, da sauran hidimomin jama’a.
Trump ya ce yawan baƙin haure a Amurka ya kai mutane miliyan 53, sannan ya yi zargin cewa mutane daga ƙasashen da ke fama da rikice-rikice, laifuka, da miyagun ƙungiyoyi suna ta zuwa ƙasar.
Ya ce shigowar baƙi ya kawo rabuwar kawuna da matsaloli a Amurka.
Haka kuma ya yi zargin cewa masu katin zama ’yan ƙasar da ke da tsarin ƙaramin albashi na rikice-rikice.
Ya batar da misali da Jihar Minnesota, yana inda ’yan gudun hijira daga Somaliya suka cika ta
Ya ce “ci gaban ƙasa ya lalace,” amma ya bayyana matakan da zai ɗauka.
Ya kuma ce zai soke shiga ƙasar ba bisa ƙa’ida ba wanda gwamnatin Biden ta bari ke faruwa.
Trump, ya ce burinsa shi ne rage yawan waɗanda yake ganin ba su da tasiri mai kyau ko kuma suna kawo matsala a ƙasar.
Ya ce “mayar da mutane ƙasashensu” shi ne kawai mafita mai ɗorewa.
Wannan sanarwa na zuwa ne bayan harin da aka kai a Washington, D.C, inda aka yi wa sojoji biyu rauni.
Hukumomi a ƙasar sun ce mutumin da ake zargi da kai harin, ya shiga Amurka a 2021 bayan ya taimaka wa sojojin ƙasar a Afghanistan, kuma an ba shi mafaka.