Damfarar CBEX: Mutum 8 da EFCC ke nema ruwa a jallo
Published: 26th, April 2025 GMT
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya EFCC, ta ayyana neman wasu jami’an CBEX waɗanda take zargi da hannu a damfarar ’yan kasar miliyoyin kuɗaɗe a wani tsarin zuba kuɗi.
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da EFCC ta wallafa a shafinta ranar Juma’a.
An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin MusulmiSanarwar ta ambato EFCCn tana zargin mutanen takwas da yaudarar jama’a su zuba kuɗi don samun riba – daga bisani suka tsere da kuɗaɗensu.
Hukumar ta bayyana sunayen mutanen da Seyi Oloyede da Emmanuel Uko da Adefowora Oluwanisola da Adefowora Abiodun Olaonipekun.
Sauran sun waɗanda ta ce ’yan ƙasashen waje ne sun haɗa da Johnson Otieno da Israel Mbaluka da Joseph Kabera da kuma Serah Michiro.
“Muna son sanar da al’umma cewa muna neman waɗannan mutane ruwa a-jallo saboda zargin damfarar mutane a wani tsarin zuba kuɗi na intanet wanda ake kira CBEX,” in ji EFCC.
Hakan na zuwa ne bayan da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bai wa jami’an EFCC ɗin damar kame da kuma tsare mutanen da aka samu da hannu wajen yaɗa tsarin na CBEX.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Damfara
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta ce ta samu rahoton laifuka 25 na cin zarafin mata da ƙananan yara a Ƙananan Hukumomin Jakusko, Fika, Potiskum da Tarmuwa, inda aka kama mutum 28 da ake zargi da aikata laifukan.
Kakakin rundunar, SP Abdulkarim Dungus, ya ce an kama masu laifin ne cikin watanni uku da suka wuce, a wani yunƙuri na daƙile cin zarafin mata da yara a faɗin jihar.
Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyuDaga cikin waɗanda aka kama akwai wani matashi mai shekara 23, Yusuf Garba, da ake zargi yi wa wata yarinya mai shekaru biyar fyaɗe.
An kai yarinyar asibiti sannan ana ci gaba da bincike a kan lamarin.
A wani lamari daban, an yi wa wata yarinya mai shekara 16 fyaɗe yayin da ta ke dawowa gida daga bikin Maulidi a Babbangida.
’Yan sanda sun kama mutum biyu; Audu Ado (22) da Babangida Alhaji Dawaye, inda suka amsa laifin bibiyar yarinyar har suka yi mata rauni.
Dungus, ya ce waɗanda abin ya shafa na samun kulawa, yayin da ake ci gaba da bincike a ofishin SCID kafin gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Emmanuel Ado, ya la’anci waɗannan mummunan laifuka, inda ya bayyana cewa rundunar za ta gabatar da rahoton bincikenta kafkn gurfanar da waɗanda ake zargin.
Ya kuma shawarci iyaye, shugabannin al’umma da ƙungiyoyi su ƙara kula da yara tare da haɗa kai da ’yan sanda domin kare su.