Aminiya:
2025-11-27@09:33:24 GMT

Damfarar CBEX: Mutum 8 da EFCC ke nema ruwa a jallo

Published: 26th, April 2025 GMT

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya EFCC, ta ayyana neman wasu jami’an CBEX waɗanda take zargi da hannu a damfarar ’yan kasar miliyoyin kuɗaɗe a wani tsarin zuba kuɗi.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da EFCC ta wallafa a shafinta ranar Juma’a.

An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin Musulmi

Sanarwar ta ambato EFCCn tana zargin mutanen takwas da yaudarar jama’a su zuba kuɗi don samun riba – daga bisani suka tsere da kuɗaɗensu.

Hukumar ta bayyana sunayen mutanen da Seyi Oloyede da Emmanuel Uko da Adefowora Oluwanisola da Adefowora Abiodun Olaonipekun.

Sauran sun waɗanda ta ce ’yan ƙasashen waje ne sun haɗa da Johnson Otieno da Israel Mbaluka da Joseph Kabera da kuma Serah Michiro.

“Muna son sanar da al’umma cewa muna neman waɗannan mutane ruwa a-jallo saboda zargin damfarar mutane a wani tsarin zuba kuɗi na intanet wanda ake kira CBEX,” in ji EFCC.

Hakan na zuwa ne bayan da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bai wa jami’an EFCC ɗin damar kame da kuma tsare mutanen da aka samu da hannu wajen yaɗa tsarin na CBEX.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro

Gwamnatin Najeriya ta ce Amurka ta amince za ta ƙara faɗaɗa haɗin gwiwar tsaro tsakaninsu, wanda ya haɗa da samar da karin bayanan sirri, makamai da sauran kayan yaƙi, domin ƙarfafa yaƙi da ’yan ta’adda da ƙungiyoyin masu tayar da kayar baya a ƙasar.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mashawarci na Musamman ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan Bayar da Bayanai da Tsara Dabaru, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Litinin.

Atiku ya karɓi katin jam’iyyar ADC a hukumance Jarumin fina-finan Indiya Dharmendra ya rasu

Wannan dai ya biyo bayan jerin tattaunawa da aka gudanar a Washington tsakanin manyan jami’an Najeriya da na Amurka, domin zurfafa dangantakar tsaro da ƙulla sabbin hanyoyin haɗin gwiwa.

Tawagar Najeriya ƙarƙashin jagorancin mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ta gana da jami’an majalisar dokokin Amurka, Fadar White House, ma’aikatar harkokin waje, da hukumomin tsaro na ƙasar.

A cikin tawagar akwai Antoni Janar na Tarayya, Lateef Fagbemi; Shugaban Ma’aikatan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Shugaban Leƙen Asirin Tsaro, Laftanar Janar Emmanuel Undiandeye; da Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, tare da wasu wakilai daga ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro.

A yayin ganawar, tawagar Najeriya ta ƙaryata zargin da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi na cewa ana kashe Kiristoci a ƙasar, tana mai cewa matsalolin tsaron ƙasar babu wanda suka ƙyale domin kuwa suna shafar al’ummomi daban-daban ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.

Zargin na Trump ya haifar da ƙalubale da dama a cikin ƙasar, inda hannayen jari suka zube, baya ga ta’azzarar matsalolin da ake gani a ’yan kwanakin nan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Ga Zanga-Zangar Lumana
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • Matsalolin Tsaro A Yankunan Bakin Ruwa A Kasar Siriya Ya Kai Zanga-Zangar Lumana
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro
  • Najeriya Ta Cimma Sabon Tsarin Hadin Gwiwa Kan Sha’anin Tsaro da Amurka