Aminiya:
2025-11-17@22:53:48 GMT

Damfarar CBEX: Mutum 8 da EFCC ke nema ruwa a jallo

Published: 26th, April 2025 GMT

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya EFCC, ta ayyana neman wasu jami’an CBEX waɗanda take zargi da hannu a damfarar ’yan kasar miliyoyin kuɗaɗe a wani tsarin zuba kuɗi.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da EFCC ta wallafa a shafinta ranar Juma’a.

An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin Musulmi

Sanarwar ta ambato EFCCn tana zargin mutanen takwas da yaudarar jama’a su zuba kuɗi don samun riba – daga bisani suka tsere da kuɗaɗensu.

Hukumar ta bayyana sunayen mutanen da Seyi Oloyede da Emmanuel Uko da Adefowora Oluwanisola da Adefowora Abiodun Olaonipekun.

Sauran sun waɗanda ta ce ’yan ƙasashen waje ne sun haɗa da Johnson Otieno da Israel Mbaluka da Joseph Kabera da kuma Serah Michiro.

“Muna son sanar da al’umma cewa muna neman waɗannan mutane ruwa a-jallo saboda zargin damfarar mutane a wani tsarin zuba kuɗi na intanet wanda ake kira CBEX,” in ji EFCC.

Hakan na zuwa ne bayan da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bai wa jami’an EFCC ɗin damar kame da kuma tsare mutanen da aka samu da hannu wajen yaɗa tsarin na CBEX.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara

এছাড়াও পড়ুন:

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

“A shekaru goma da suka gabata, ayyukan ta`addanci da tashe-tashen hankula daga masu tsattsauran ra`ayi ya haifar da mummunan koma bayan tattalin arziki da na zamantakewar alummomin dake shiyyar, halin da daliban irin wadannan makarantu suke ciki yana bukatar kulawar gaggawa daga kungiyar ta ECOWAS, abin takaici irin wadannan makarantun allo suna daukar dalibai masu yawan gaske kuma akasari kananan yara daga shiyyar, to amma kuma ba a bai wa makarantun da daliban kulawar da ta kamata, wannan ta sanya kungiyoyin `yan ta`adda ke samun kofar kusantar su domin kwadaita musu shiga cikin kungiyoyin.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe November 16, 2025 Labarai NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji November 16, 2025 Nazari Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna? November 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NELFUND ya raba wa ɗalibai tallafin karatu na Naira Biliyan 116 
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
  • Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
  •  An Amince Da  Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin
  • A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS
  • Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA
  • Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda, sun kama mutum 94
  • Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
  • ’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi