Aminiya:
2025-11-19@20:34:14 GMT

Damfarar CBEX: Mutum 8 da EFCC ke nema ruwa a jallo

Published: 26th, April 2025 GMT

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya EFCC, ta ayyana neman wasu jami’an CBEX waɗanda take zargi da hannu a damfarar ’yan kasar miliyoyin kuɗaɗe a wani tsarin zuba kuɗi.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da EFCC ta wallafa a shafinta ranar Juma’a.

An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin Musulmi

Sanarwar ta ambato EFCCn tana zargin mutanen takwas da yaudarar jama’a su zuba kuɗi don samun riba – daga bisani suka tsere da kuɗaɗensu.

Hukumar ta bayyana sunayen mutanen da Seyi Oloyede da Emmanuel Uko da Adefowora Oluwanisola da Adefowora Abiodun Olaonipekun.

Sauran sun waɗanda ta ce ’yan ƙasashen waje ne sun haɗa da Johnson Otieno da Israel Mbaluka da Joseph Kabera da kuma Serah Michiro.

“Muna son sanar da al’umma cewa muna neman waɗannan mutane ruwa a-jallo saboda zargin damfarar mutane a wani tsarin zuba kuɗi na intanet wanda ake kira CBEX,” in ji EFCC.

Hakan na zuwa ne bayan da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bai wa jami’an EFCC ɗin damar kame da kuma tsare mutanen da aka samu da hannu wajen yaɗa tsarin na CBEX.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi

Gwamna Ahmed Idris na Jihar Kebbi ya ba da tabbacin cewa jami’an tsaro za su ƙwato ’yan matan da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Kwalejin ’Yan Mata ta GGCSS Maga da ke Ƙaramar Hukumar Danko Wasu ta jihar cikin ƙoshin lafiya.

Gwamnan ya bayar da tabbacin ne a yayin ganawarsa da iyayen ɗaliban kaɗan bayan harin ’yan bindigar a ranar Litinin.

Aminiya ta ruwaito cewar da asubahin ranar ’yan bindiga suka kusta cikin harabar makarantar kwana ta ’yan mata ta GGCSS Maga, suka kwashe ɗalibai 25 daga ɗakin kwanansu zuwa cikin jeji.

Maharan da suka riƙa harbi a iska kafin su shiga harabar makarantar sun bindige Matakin Shugaban Makarantar, Malam Hassan Yakubu Makuku, wanda ya yi ƙoƙarin hana su tafiya da yaran.

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Tinubu ba ta shirya kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga ba — Amnesty Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas

A yayin ziyarar jaje da Gwamna Idris ya kai makarantar, bayan yanke ziyarar aiki da ya kai Abuja, ya ba wa iyayen ɗalibai tabbacin cewa gwamnatinsa da hukumomin tsaro za su yi dukkan abin da zai yiwu wajen ceto yaran.

Kana ya jaddada cewa za su ci ga da ƙoƙari wajen ganin bayan ayyukan ta’addanci a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama miji da mata kan zargin mallakar buhuna 360 na Tabar Wiwi
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
  • ‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’
  • Harin Isra’ila ya kashe mutum 15 a sansanin ‘yan gugun hijira na Falasdinawa a Lebanon
  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahada Sanadiyyar Harin Sojojin “Sahayoniya A Garin Bint-Jubail
  • GGCSS Maga: Halin da iyaye ke ciki bayan sace ’ya’yansu
  • Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
  • Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka
  • NELFUND ya raba wa ɗalibai tallafin karatu na Naira Biliyan 116 
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara