Aminiya:
2025-12-12@05:06:24 GMT

Damfarar CBEX: Mutum 8 da EFCC ke nema ruwa a jallo

Published: 26th, April 2025 GMT

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya EFCC, ta ayyana neman wasu jami’an CBEX waɗanda take zargi da hannu a damfarar ’yan kasar miliyoyin kuɗaɗe a wani tsarin zuba kuɗi.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da EFCC ta wallafa a shafinta ranar Juma’a.

An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin Musulmi

Sanarwar ta ambato EFCCn tana zargin mutanen takwas da yaudarar jama’a su zuba kuɗi don samun riba – daga bisani suka tsere da kuɗaɗensu.

Hukumar ta bayyana sunayen mutanen da Seyi Oloyede da Emmanuel Uko da Adefowora Oluwanisola da Adefowora Abiodun Olaonipekun.

Sauran sun waɗanda ta ce ’yan ƙasashen waje ne sun haɗa da Johnson Otieno da Israel Mbaluka da Joseph Kabera da kuma Serah Michiro.

“Muna son sanar da al’umma cewa muna neman waɗannan mutane ruwa a-jallo saboda zargin damfarar mutane a wani tsarin zuba kuɗi na intanet wanda ake kira CBEX,” in ji EFCC.

Hakan na zuwa ne bayan da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bai wa jami’an EFCC ɗin damar kame da kuma tsare mutanen da aka samu da hannu wajen yaɗa tsarin na CBEX.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara

এছাড়াও পড়ুন:

Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe

Wani mutum ya mutu, wasu da dama kuma sun jikkata lokacin da wata tirela ta yi karo da wata mota ƙirar akori kura Mitsubishi Canter a Damagum da misalin ƙarfe 12:50 na tsakar dare a ranar Laraba.

Kamar yadda kakakin rundunar ‘Yan sanda Jihar Yobe, SP Dungus Abdulkareem ya ce tirelar, mai lambar rajista MUS 791 XH, wacce Aliyu Muhammad, mai shekara 30, daga Azare, ƙaramar hukumar Katagum, Jihar Bauchi ke tuƙawa tana tafiya daga Damaturu zuwa Legas lokacin da motar ta kufcewa direban ta afka wa motar da ke gabanta.

Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige

Motar, mai mutane 18 da ke ciki da lamba AA 641 PKM, wadda Usman Muhammad, mai shekara 40 daga ƙauyen Yaskawel ne ke tuƙa ta.

Mai magana da yawun rundunar ya ce, an tabbatar da mutuwar fasinja ɗaya, Ɗahiru Maikuɗi mai shekara 40, daga ƙauyen Yaskawel, a babban asibitin Damagum yayin da wasu da dama suka jikkata.

A cewar rundunar, an tura waɗanda abin ya shafa shida zuwa asibitin Koyarwa da ke Damaturu don ƙarin kula da lafiyar su.

Hatsarin ya haifar da zanga-zanga daga matasan Damagum waɗanda suka koka game da yawan haɗurra a kan babbar hanyar Damaturu zuuwa Potiskum, musamman kusa da Damagum inda ake harkokin kasuwanci da zirga-zirgar masu sufuri a ƙasa ke ƙaruwa musamman a ranakun Lahadi da Laraba.

Jami’an ‘yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zangar don hana cin zarafin da ake yi wa mutane.

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, Emmanuel Ado ya yi wa iyalan wanda ya rasu ta’azɗiyar rashin mamacin ya jajantawa waɗanda suka jikkata yayin wannan hatsari  yana mai umurtar Jami’in ‘yan sandan yankin da ya yi aiki tare da ƙaramar hukumar kan matakan kariya na dogon lokaci.

Ya gargaɗi masu ababen hawa game da yin gudun wuce ƙima kuma ya yi kira da a bi ƙa’idodin zirga-zirga sosai, yana mai gargaɗin cewa, waɗanda suka karya doka za su fuskanci hukunci.

Kwamishinan ya kuma shawarci mazauna yankin da su guji yin harkokin kasuwanci kusa da babbar hanyar don rage ƙarin faruwar haɗurra.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi AkanDoron Ruwa
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”