Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Bayyana Cewa: Atisayen Sojojin Iran Ya Fayyace Karfinsu
Published: 26th, January 2025 GMT
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta kasar Iran ya bayyana cewa: Atisayen sojin mai take “‘Manzon Allah Mai Girma na 19” ya bayyana ƙarfin sojojin Iran
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran, Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Atisayen “Manzon Allah Mai Girma na 19” a cikin ruwan Tekun Fasha ya bayyana Alamar da ƙarfin sojojin Iran suke da shi.
Mohammad Baqir Qalibaf ya bayyana haka ne a yayin zaman majalisar shawarar Musulunci a yau Lahadi: Atisayen “Manzon Allah Mai Girma na 19″ na sojojin ruwa da ke karkashin dakarun kare juyin juya halin Musulunci suka yi a cikin ruwan tekun Fasha, da kuma makaman tsaro da aka mika wa sojojin kasa na sojojin Iran, wanda a lokacin aka yaye shamakin wasu sabbin gagaruman nasarori na tsaro da aka samu a Iran, da suke bayyana wasu sabbin nasarorin da Iran ta samu a fagen kere-kere, a bangare na karfin sojojin Iran.
Qalibaf ya jaddada cewa: Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta sanar da bin diddigin matsayar Jamhuriyar Musulunci ta Iran kan manufofin harkokin wajen kasar bisa tsarin manufofin da Jagoran juyin juya halin Musulunci ya tsara, kuma nauyi na karshe yana kan ministan harkokin wajen kasar, kuma dole ne ya kasance mai bin diddigin ayyukan da ya yi a gaban Majalisar Shawarar Musulunci da kuma al’ummar kasa, karkashin tsarin dabarun aiki da ya ba da tabbacin aiwatar da tattalin arziki da yin watsi da ayyukan da suke hatsari na zahiri.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
Abbas ya kuma jaddada bukatar da dauki matakai, kan aukuwar sauyin yanayi, musamman duba da matsalar talauci da kuma ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro, da kasar nan, ke fuskanta.
Bugu da kari, Hukumar kula da ‘yan cirani ta duniya wato IOM ta sanar da cewa, gurbata muhalli da robobin da aka sarrafa zuke haifarwa, suna taka gudunmwa, wajen aukuwar dumamar yanayi da kuma gurbata muhalli.
A cewar Hukumar, matsalar na kuma lalata kasar noma da lalata hanyoyin ruwa, tare da kuma tilasta alumma, tashi daga matsugunan su, zuwa wasu gurare, domin su ci gaba da gudanar da rayuwarsu.
Hakazalika, a cikin wasu rahotanni da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, sun bayyana cewa, a fadin duniya, ana yin amfani da Lidojin da suka kai, yawan miliyan 500 a duk shekara, wanda kusan tan miliyan 13, suke kwarara zuwa cikin Tekuna, a duk shekara.
Ana kuma yin amfani da Gangunan Mai miliyan 17, da aka sarrafa, aka kuma zuba a cikin Gangunan, inda kuma a fadin duniya, mutane ke sayen Kwalaben Man da suka kai miliyan daya.
An kiyasata cewa, a duk shekara, daobboin da ke rayuwa a cikin Tekuna guda 100,000 ne, irin wadannan Robobin da aka zuba a cikin Tekunan, suke hallaka su.
Bugu da kari, wasu bincike da aka gudanar, sun nuna cewa, Ruwan sha da ake sarrafawa a sanya a cikin Robobin Shan Ruwa, sun kai kaso 90 a cikin dari, inda kuma Ruwan da ake samu daga Fanfuna, suka ke da kaso 83 a ckin dari, wadanda kuma suke dauke da sanadaran microplastic, da ke makalewa, a cikin Robobin, inda wannan sanadarin, ke shafar kiwon lafiyar bil Adama.
A Nijeriya za a iya cewa, kalubalen na muhalli sun kasance iri-iri, musamman duba da annobar ambaliyar ruwan sama da kasar ke fuskanta a duk lokacin damina da Fari da gurrbatar muhalli da kuma rashin samar da kyakyawan tsarin zubar da shara, musamman na bolar Robobin da aka gama amfani da su.
Misali, a ranar 28 na watan Mayun 2025, garin Mokwa, da ke a jihar Neja, an fuskanci, mummunar ambaliyar ruwan sama, inda jami’ai suka sanar da cewa, sama da mutane 200 da iftila’in ya aukwa, suka rasu tare da kuma bacewar mutane da yawansu ya kai sama da 1,000, wasu 121 suka samu raunuka, gidaje 2,000 suka lalace.
Irin wannan iftila’in na Mokwa, na daya daga cikin rin wadanda suka auku a shekarun baya a wasu sannan kasar.
Ana nan, muma mun goyi bayan furucin da Ministar Kula da Jindadi da Walwalar Mata Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim ta yi, na ciwar kalubalen na gurbatar muhlaii, na janyo tarwatsa alumomin kasar, daga matsugunan su, musamman duba da yadda iftila’in, yafi shafar mata da yara.
Batun da ake yi na samar da wadataccen abincin a kasar, zai kasance ne tamkar wani mafarki, matukar mahukutna kasar, ba su yi gaggawar daukar matakan da suka kamata, kan batun na gurbatar muhalli, a kasar ba.
Domin samar da tsarin rage zubar da bola, musamman ta Robobi a kasar Gwamnatin Tarayya ta gabatar da wani tsari na NPPWM.
Sai dai, wannan tsarin ya hadu da cikas, musamman duba da cewa, wanzar da tsarin daga bangaren Gwamnatin, ba ta mayar da hankali akansa ba, inda sai dai kawai, daidaikun ‘yan kasar ne a kashin kansu suke ci gaba da tsaftace guraren da ake jibge bola, musamman a birane da wasu guraren.
Shugabar Babban Majalisi a Majalisar Dinkin Duniya Maria Fernanda Espinosa Garcés, ta bayar da shawarar cewa, batun na gurbar muhalli, abu ne, da ya wajaba a sake tunani akai.
A daukacin jihohi 36 na kasar, Legas da Ekiti ne kawai, suka dauki matakan da suka kamata, kan kare gurbatar muhalli, a jihohinsu.
Kazalika, a matakin Majalisa, Shugaban Kwamiti kan Yada Labarai da Kula da Hudda da Jama’a Hon. Akin Rotimi ya shelanta cewa, daga cikin kudurori 899 da Majalisar ta gabatar a cikin shekaru biyu, guda 27 ne kacal, Majalisar ta mayar da hankali kan na kula da muhalli.
Sai dai, an ruwaito cewa, wani Majalisar na kan kokrin samar da wasu tsare-tsare na yakar yawan amfani da Robobin barkatai a kasar, musamman a biranen kasar.
A ra’ayin wannan Jaridar, muna goyon bayan cewa, ba zai yuwa a bar Nijeriya a baya, wajen shiga cikin kokarin da ake yi, a fadin duniya, na yakar gurbata muhalli ba.
Ya zama wajbi, bikin na wannan shekarar, ya kasance mataki na farko, na yakar gurbata muhalli, ba wai kawai tatsuniya ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp