Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
Published: 28th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta gano ma’aikatanta 240 da ke ƙarɓar albashi sau biyu a duk wata, da wasu 217 da ke amfani da lambar tantance asusun banki (BVN) guda ɗaya.
Wani mai magana da yawun gwamnati, Dakta Sulaiman Wali Sani, ya gaya wa manema labarai a ranar Lahadi cewa an gano wannan badaƙalar ce a yayin da ake tantance tsarin biyan albashin gwamnati.
Dr. Sani ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin biyan ma’aikata daidai kuma akan lokaci, kuma gano waɗannan matsalolin wani ɓangare ne na gyara al’amura.
Ya ce sun duba bayanan ma’aikata ta hanyar amfani da hotunan yatsa a matakin jiha da ƙananan hukumomi.
“Tsohuwar hanyar biyan mutane tana da matsaloli. Mun gano ma’aikata 240 suna karɓar albashi sau biyu kuma mutane 217 suna amfani da BVN ɗaya, wanda zai iya nufin akwai ma’aikatan bogi ko kuma mutane suna amfani da BVN na wani,” in ji Dakta Sani.
Ya kuma ce ma’aikata 1,335 ba su zo don a tantance su ba a tsawon fiye da watanni shida, wanda ya sa suke tunanin ko waɗannan mutanen da gaske suna aiki da gwamnati.
Alhaji Umar Idi, wanda ya duba biyan kuɗin ƙananan hukumomi, ya ce sun gano sunaye 247 da babu tabbaci a kansu. Waɗannan sun haɗa da mutanen da suka yi ritaya, waɗanda suka mutu, ko kuma waɗanda aka ci gaba da biyan su ba tare da izini ba bayan lokacin barinsu aiki.
“Daga cikin waɗannan ma’aikata 247, takwas ne kawai suka zo don tabbatar da cewa har yanzu suna aiki. Za a goge sauran sunaye 239, wanda zai rage wa gwamnati asarar naira miliyan 27 a duk wata,” in ji shi, yana mai cewa za a mayar da kuɗaɗen da aka samu ga asusun gwamnati.
Dakta Sani ya ce gwamnati ba ta ƙoƙarin hukunta kowa ba, kawai dai tana gyara tsarin ne don ma’aikata na gaske da ’yan fansho su ci gaba da karɓar haƙƙoƙinsu ba tare da wata matsala ko yanka ba bisa ƙa’ida ba.
“Tun lokacin da Gwamna Abba ya fara aiki, ya tabbatar da cewa ana biyan ma’aikatan gwamnati da ’yan fansho a kan lokaci, ba tare da ɓoyayyun cire-cire da aka riƙa yi a baya ba,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa yanzu da suke tsaftace tsarin biyan kuɗi, ma’aikata su yi tsammanin samun biyan kuɗi mafi inganci a gaba.
Gwamnati ta ce za ta ci gaba da magana da duk masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa an magance duk matsalolin kuma jama’a sun sake amincewa da ayyukan gwamnati.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Lambar BVN
এছাড়াও পড়ুন:
A yau sharhin namu zai yi muku Magana ne game amincewa da falasdinu a matsayin kasa da wasu kasashen turai suka yi a baya bayan nan ciki har da birtaniya da kasar Faransa, sai dai amincewa da kasar falasdinu ci gaba ne babba mai cike da tarihi amma haka
A yan kwanaki kin nan kasashen duniya sun fuskanci wani lamari mai jan hankali sosai, wanda ya jaddada hakkin falasdinu na kafa kasarsa mai cin gashin kai, hakika wannan lamari ya kai kololuwasa inda ya kai ga ranar litinin da ta gabata aka kira wani taro a gegen taron majalisar dinkin duniya karo na 80 domin bayyana nuna amincewa da warware rikicin falasdinu na kafa kasashen biyu masu cin gashin kansu,
Akwai abubuwa guda buyi masu gayar muhimmancin da suka sanya aka gudanar da taron kafa daula biyu, na farko hakika yazo a yan kwanaki kadan sanar da shimfida taswirar hanya na kafa kasar falasdinu mai cin gashin kai bisa iyakoyin da aka cimma a wata yuni shekara ta 67 wadda ke da babban birni a Qudus, wanda sama da kasshen 142 suka amince da shi wato kusan kaso uku bisa 4 na dukkan mambobin kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya,
Na biyu wannan ya zo a wani matsayin sauyi mai cike da tarihi game da matsayin kasashen turai kan batun falasdinu, wanda ya hada da amincewa da kasar falasdinu mai cin gashin kanta da kasashe fiye da goma suka yi, wanda suka hada da kasashen Birtaniya, Faransa, Canada, Austeralia da dai sauransu.
Da gaske ne wadannan kasashen guda 10 sun taba nuna amincewa da warware malasar ta hanyar kafa kasashe biyu, sai dai basu iya dukan kirji wajen amince da falasdinu a matsayin kasa ba.
Babu bukatar alumma falasdinu su amince da kowa domin tabbatar da hakkinsu na kafa kasa mai cin gashin kai, kamar yadda ya kasance a majalisar dinkin duniya, a shekara ta 1947, inda aka dauki matakin raba kasar falasdinu biyu daya ta yahudawa, daya kuma ta alummar falasdini a kuduri mai lamba 181, a fili yake alummar falasdinu sun ki amincewa da wannan kuduri saboda irin rashin adalcin da yake cikinsa kan hakkin faladinu mai cike da tarihi da baya bukatar a juya shi ko canzashi ta kowanne hali,
sai dai rashin amincewar ba zai rage komai daga cikin tabbatacen hakkinsu ba, wannan lamarin, wanda kwamitin tsaro ya tabbatar da shi a matsayinsa na wakilin majalisar dinkin duniya.
Lokacin da bn goriyon ya kaddamar da wannan shirin na kafa kasar Isra’ila, a shekar ta 1948 bisa dogaro da iyakokin da ya gindaya idan zaa raba yankin, haka yake gwamnatin sahyuniya bata ja da baya ba tun wancan lokacin wajen kokarin ganin ta ci gaba da mamaya da fadada ikonta a yankuna makwabtanta da karfin tsiya ba, bayan yake –yake da ta kaddamar wanda ya bata damar wuce iyakokin da aka gindaya kan batun raba kasa, sai dai majalisar dinkin duniya ba ta amince da wannan mamaya da take yi ba, kuma tana mu’amala da ita akan dole ta dawo da sauran yankunan da ta mamaye da karfi kuma ta bukaci ta fice daga wajen, domin ba wuri ne da ake jayayya akansa ba kamar yadda take ikirari a ko da yaushe,
Lokacin da kungiyar yantar da falasdinu a matsayinta ta wakiliyar alummar falasdini ita kadai tilo, ta yi watsi da manufofin gwagwarmaya da makamai tun a shekara ta 1988 ta kuma yanke shawarar yin sulhu ta hanyar lummana, sannan ta yi amfani da wannan mataki a aikaace sa’ilin da aka rattaba hannu kan yarjejeniyar Oslo a shekara ta 1993, sai dai kungiyar ba tayi aiki da kudurin raba kasa ba a matsayin wata doka don sasantawa da ake so, duk da tabbbatar da batun kafa falasdinu mai cin gashin kanta a kusan kashi 44 cikin dari na yankin falasdinu mai cike da tarihi, a maimakon haka ta amince da kudurin kwamitin sulhu mai lamba 44 a amtsayin abin da za’a dogra da shi a sasantawar,
Duk da yake cewa abin da ya hau kansu na hakkin amincewa da kafa kasar falasdinu mai cin gashin kai wanda ya kai kusan kaso 44 cikin dari na yankin falasdinu mai cike da tarihi, amma mai makon wannan ta amince da kudurin majalisar dinkin duniya mai lamba 242 , yana nufin amincewar da suka yi a baya a matsayin matsakaicin yankin na kasar falasdinu da ake so, wanda hakan ke nuna cewa yarjejeniyar da ta gabata ta gamsu da kashi biyar na yankin falasdinu mai cike da tarihi.
Wannan wani babban rangwame ne da ya kamata ya rudi gwanatin sahayuniya ta amince da shi cikin gaggawa, da kuma kokarin mayar da ita da gaske, sai dai hakan bai faru ba, kasa da shekaru biyu da fara aiki da yarjejeniyar Oslo aka kashe yitzhaj rabin sai masu tsatstsauran ra’ayi suka fara kasancewa su ne akan gaba sannu a hankali, har suka samu ikon sarrafa duk wasu manya a gwamnatin sahyuniya,
Daga nan ta yi iyakacin kokarinta na dakile yankurin kafa kasar falasdinu mai cin gashin kai, a matsayin matakin farko na kafa Isra’ila Babba bisa ga abinda littafi mai zarki na Attaura ya bayyana.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar RSF Ta Shigar Da Kara A Kotun ICC Kan Kisan Isra’ila A Gaza. October 1, 2025 Kasar Pakistan Tayi Gwajin Makami Mai Linzami Na Fatah 4 Cikin Nasara. October 1, 2025 A gobe Ne Ake Sa Ran Tawagar Agaji Ta Sumud Flotilla Za ta Isa Gaza. October 1, 2025 Iran Ta yi Kira Da A Gaggauta Kakabawa HKI Takunkumi October 1, 2025 A yau Najeriya ke bikin cika shekaru 65 da samun yancin kai October 1, 2025 Aragchi: Za’a Fara Tattaunawa Ta Karshe Dangane Da Shirin Snapback October 1, 2025 Tinubu: Na Gaji Rusashen Tattalin Arziki A Sanda Na Karbi Ikon Kasar October 1, 2025 Iran: Dakarun Ruwa Na Iran A Shirye Suke Su Shiga Yaki Da Kowa Don Kare Kasa October 1, 2025 Pezeshkiya: Aiki Ta Kasar China Yana Da Matukar Muhimmanci Musamman A Wannan Halin Da Ake Ciki October 1, 2025 Tawagar Jiragen ‘Assumud’: Yahudawan Isra’ila Sun Kai Mana Hare-Hare Da Safe October 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci