Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
Published: 28th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta gano ma’aikatanta 240 da ke ƙarɓar albashi sau biyu a duk wata, da wasu 217 da ke amfani da lambar tantance asusun banki (BVN) guda ɗaya.
Wani mai magana da yawun gwamnati, Dakta Sulaiman Wali Sani, ya gaya wa manema labarai a ranar Lahadi cewa an gano wannan badaƙalar ce a yayin da ake tantance tsarin biyan albashin gwamnati.
Dr. Sani ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin biyan ma’aikata daidai kuma akan lokaci, kuma gano waɗannan matsalolin wani ɓangare ne na gyara al’amura.
Ya ce sun duba bayanan ma’aikata ta hanyar amfani da hotunan yatsa a matakin jiha da ƙananan hukumomi.
“Tsohuwar hanyar biyan mutane tana da matsaloli. Mun gano ma’aikata 240 suna karɓar albashi sau biyu kuma mutane 217 suna amfani da BVN ɗaya, wanda zai iya nufin akwai ma’aikatan bogi ko kuma mutane suna amfani da BVN na wani,” in ji Dakta Sani.
Ya kuma ce ma’aikata 1,335 ba su zo don a tantance su ba a tsawon fiye da watanni shida, wanda ya sa suke tunanin ko waɗannan mutanen da gaske suna aiki da gwamnati.
Alhaji Umar Idi, wanda ya duba biyan kuɗin ƙananan hukumomi, ya ce sun gano sunaye 247 da babu tabbaci a kansu. Waɗannan sun haɗa da mutanen da suka yi ritaya, waɗanda suka mutu, ko kuma waɗanda aka ci gaba da biyan su ba tare da izini ba bayan lokacin barinsu aiki.
“Daga cikin waɗannan ma’aikata 247, takwas ne kawai suka zo don tabbatar da cewa har yanzu suna aiki. Za a goge sauran sunaye 239, wanda zai rage wa gwamnati asarar naira miliyan 27 a duk wata,” in ji shi, yana mai cewa za a mayar da kuɗaɗen da aka samu ga asusun gwamnati.
Dakta Sani ya ce gwamnati ba ta ƙoƙarin hukunta kowa ba, kawai dai tana gyara tsarin ne don ma’aikata na gaske da ’yan fansho su ci gaba da karɓar haƙƙoƙinsu ba tare da wata matsala ko yanka ba bisa ƙa’ida ba.
“Tun lokacin da Gwamna Abba ya fara aiki, ya tabbatar da cewa ana biyan ma’aikatan gwamnati da ’yan fansho a kan lokaci, ba tare da ɓoyayyun cire-cire da aka riƙa yi a baya ba,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa yanzu da suke tsaftace tsarin biyan kuɗi, ma’aikata su yi tsammanin samun biyan kuɗi mafi inganci a gaba.
Gwamnati ta ce za ta ci gaba da magana da duk masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa an magance duk matsalolin kuma jama’a sun sake amincewa da ayyukan gwamnati.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Lambar BVN
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
Jaridar Daily Trust da gidan talabijin na Trust TV, dukkansu mallakar kamfanin Media Trust, a bana ma sun sake yin fice bayan ’yan jaridansu suka lashe kyautar binciken kwakwaf ta Wole Soyinka ta bana.
’Yan jaridar na Daily Trust da Trust TV, Afeez Hanafi da Muslim Muhammad Yusuf, sun lashe gasar ne a matsayin zakaru a rukunin rahoton jarida da kuma na talabijin mafi daraja a bana a Najeriya.
Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a SakkwatoHanafi ya lashe rukuni na rubutu bisa labarinsa mai taken: “Bincike: Dan jarida ya samu ayyuka biyu da takardun bogi na Oluwole.”
Wanda ya zo na biyu da na uku a rukunin na rubutu su ne Kingsley Jeremiah da Ann Godwin, dukkansu daga jaridar The Guardian.
Sai dai kamar yadda aka saba, babu wanda ya lashe kyautar a rukuni na rediyo, kuma babu wanda ya fito a matsayin na biyu ko na uku.
A rukuni na yanar gizo, Theophilus Adeokun na National Record ya lashe gaba ɗaya da labarinsa mai taken: “Dangote, a neman makamashi mai arha, yana zubar da guba cikin kogunan Binuwai.”
Wanda ya yi na biyu shi ne Kunle Adebajo daga HumAngle, yayin da Isah Ismaila, shi ma daga HumAngle din ya zo na uku.
A rukunin hoto kuwa, Elliot Ovadje na jaridar Punch ya fito a matsayin zakara, sannan shi ɗin ne ya sake fitowa a matsayin na biyu da na uku.
A bangaren girmamawa, tsohon Alkalin Kotun Ƙoli, Justice Ayo Salami, ya samu kyautar mai rajin kare hakkin dan Adam, yayin da fitaccen marubuci kuma mawaki, Odia Ofeimun, ya samu kyautar kwarewa a aikin jarida.
Tun kafin gabatar da kyaututtuka, shugabar alkalai ta shekarar 2025, Abigail Ogwezzy‑Ndisika, a jawabinta ta ce an samu shigar da rubuce‑rubuce 180, amma aka tace su zuwa 129.
Ta jaddada abubuwan da aka yi amfani da su wajen tantance kowanne rubutu da suka hada da jarumta, zurfi, daidaito, tasiri da kuma jajircewa ga muradun jama’a.
“Mun yi wannan aikin ne daban‑daban kuma ba tare da katsalandan ba, ta amfani da wasu ka’idoji da suka shafi rufe batutuwan cin hanci, take hakkin ɗan adam, laifuka da ayyukan ɓoye, da kuma kyawawan hanyoyin binciken jarida,” in ji ta.
Marubucin da aka saka wa gasar sunansa kuma mai lambar yabo ta Nobel, Wole Soyinka, ya taya dukkan wadanda suka samu kyautar murna, yana mai gargadin kada su yi sakaci.
“Wasu daga cikin jaruman da za su ceci wannan ƙasa za a same su a cikin kafafen yada labarai. Amma a lokaci guda, dole ne in roƙi kafafen yada labarai su yi dada takatsantsan, su yi bincike mai zurfi kan abin da suke wallafawa. Akwai labarai masu yawa da ake wallafawa da ba daidai ba ne,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga jaridun da su inganta rahotanninsu, yana nuna damuwa kan yawan labaran karyar da ke yawo a kafafen sada zumunta.