Gwamnatin kasar Saudiya ta yi allawadai da HKI a kissan da take wa falasdinawa a Gaza, a jiya talata a gaban kutun ICJ. Saudiya ta bayyana cewa gwamnatin HKI ta sabawa dokokin kasa da kasa da dama a kissan kiyashin da take yi a Gaza.

Wakilin kasar a gaban kotun Muhammad Saud Al-Nasser, ya kara da cewa, HKI ta ci gaba ta sabawa wadannan dokoki, amma kuma bata da dalilan saba masu.

Banda kissan kiyashin da take yi a Gaza, Al-Nasser ya ce HKI ta maida Gaza kofai, ta rusa mafi yawan gine-ginen yankin, sannan ta hana shigowar abinci da ruwa da magunguna zuwa yankin, wadanda ko wane daya daga cikinsu take hakkin bil’adama ne wanda yake kaiwa ga laifin yaki.

Gwamnatin Saudiya ta gabatar da wannan jawabin ne a rana ta biyu da bude zaman da kotun ta ICJ tayi don tattaunwa da kuma jin ra’ayin kasashe dangane da take hakkin bi’adaman da HKI take yi a Gaza. A halin yanzu fiye da kwamaki 50 kenan da gwamnatin HKI ta ke hana shigowar abinci da magunguna da kuma bukatun falasdinawa zuwa yankin.

Har’ila yau kotun ta girka wannan zaman ne don tattauna yadda HKI take mu’amala da umurnin ta danganda take hakkin bil’adama a Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine

Shugaban kasar Amurka Donal Trump yayi watis da kasashen turai a tattaunawar dawo da zaman lafiya a Ukraine, wanda hakain ya sa kasashen rauni a cikin al-amuran kasar ta Ukraine.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa a wani taro mai muhimmanci wanda Volodimir Zelesky shugaban kasar Ukraine ya yi da Firai ministan kasar Burtania Keir Starmer, da Emmanuel Macron na kasar Faransa da kuma Friedrich Merz chancellor na kasar Jamus Zelesky ya kasa fada masu gaskiyar abinda Amurka take shiri na zaman lafiya a kasar ta Ukraine.

Labarin ya kara da cewa, kasashen turai sun kashe biliyoyin Euro a yakin Ukraine kuma suna ci gaba da kashewa yakin Ukraine da Rasha kudade, amm Donal Trump na Amurka ya waresu a tattaunawan da yake yi da Rasha kan yadda tsagaita budewa juna wuta ko kuma zaman lafiya tsakaninin kasashen biyu zai kasan ce.

Natron shuwagabannin kasashen uku da Zelesky a London ya maida hankali kan ‘karin hanyoyin takurawa kasar Rasha, sai dai shuwagabannin basu bada sabbin shawarori ba. Kakakin gwamnatin kasar Burtania ya bayyana cewa kasashen uku duk sun amince da wannan wata marhala ce mai muhimmanci a yakin na Ukraine, kuma zasu ci gaba da takurawa kasar Rasha.

Trump ya fadawa SkyNews kan cewa Zelesky baya tunani  mai zurfi a cikin lamarin kasarsa. Ya kuma bayyana cewa shugaba Putin bai da wata matsala a shawarar da ya gabatar. Sai dai kuma dansa Cosner y ace, babansa yana iya janyewa daga tattaunawar gaba daya idan ya ga Zeleskiya ba ashirye yake ya tsaida yaki a kasarsa ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya: Jirgin Sojojin Kasar Yana Kan Hanyarsa Ta Zuwa Portugal, Amma Ta Sauka A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan  Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko  Da  ‘Yan Ta’adda December 9, 2025  Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025  Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF  A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  • Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan