Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
Published: 30th, April 2025 GMT
Gwamnatin kasar Saudiya ta yi allawadai da HKI a kissan da take wa falasdinawa a Gaza, a jiya talata a gaban kutun ICJ. Saudiya ta bayyana cewa gwamnatin HKI ta sabawa dokokin kasa da kasa da dama a kissan kiyashin da take yi a Gaza.
Wakilin kasar a gaban kotun Muhammad Saud Al-Nasser, ya kara da cewa, HKI ta ci gaba ta sabawa wadannan dokoki, amma kuma bata da dalilan saba masu.
Banda kissan kiyashin da take yi a Gaza, Al-Nasser ya ce HKI ta maida Gaza kofai, ta rusa mafi yawan gine-ginen yankin, sannan ta hana shigowar abinci da ruwa da magunguna zuwa yankin, wadanda ko wane daya daga cikinsu take hakkin bil’adama ne wanda yake kaiwa ga laifin yaki.
Gwamnatin Saudiya ta gabatar da wannan jawabin ne a rana ta biyu da bude zaman da kotun ta ICJ tayi don tattaunwa da kuma jin ra’ayin kasashe dangane da take hakkin bi’adaman da HKI take yi a Gaza. A halin yanzu fiye da kwamaki 50 kenan da gwamnatin HKI ta ke hana shigowar abinci da magunguna da kuma bukatun falasdinawa zuwa yankin.
Har’ila yau kotun ta girka wannan zaman ne don tattauna yadda HKI take mu’amala da umurnin ta danganda take hakkin bil’adama a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
Zanga-zanga ta ɓarke a yankin Numan da ke Jihar Adamawa, kan zargin sojoji da kashe wasu mata a garin Lamurde.
Mata sun fito zanga-zangar ne sakamakon rikicin da ya ɓarke tsakanin kabilu Bachama da Chobo.
An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello TurjiA lokacin zanga-zangar an ruwaito cewar mata bakwai ne suka mutu sannan wasu 11 suka jikkata.
Shaidu sun ce sojoji sun buɗe musu wuta yayin da suke tare hanya, suna zargin rundunar da goyon bayan wata ƙabila.
Sai dai rundunar Sojin Najeriya ta musanta wannan zargi.
Ta ce dakarun sun yi artabu ne da wasu ‘yan bindiga a yankin, kuma ta ce mutuwar wasu mata biyu ya faru ne sakamakon buɗe wuta da ‘yan bindigar suka yi, ba wai sojoji suka harbe su ba.
Gwamnatin Jihar Adamawa, ta ayyana dokar hana fita na awa 24 a Lamurde domin daidaita al’amura da zaman lafiya.
A Numan, matan da suka sanya riga ɗauke da launin baƙi ne suka fara zanga-zangar a manyan tituna, inda suke neman yi wa waɗanda aka kashe adalci.
An riga an binne wasu daga cikin waɗanda suka rasu, lamarin da ya ƙara haifar da damuwa a tsakanin al’ummar yankin.
Ɗan Majalisa mai wakiltar yankin, Kwamoti Laori, ya yi Allah-wadai da kisan, inda ya ce ya kamata a gudanar da bincike mai zurfi.
Ya buƙaci hukumomin tsaro da su ɗauki matakin da ya dace, tare da tabbatar da zaman lafiya ba tare da tauye haƙƙin ɗan Adam ba.
Mazauna yankin sun ce rigimar ta jefa mutane cikin tsoro, wanda hakan ya sa da dama suka tsare daga gidajensu.
Shugabannin al’umma a yankin, sun yi kira da a yi sulhu domin kaucewa ƙarin tashin hankali.