Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
Published: 30th, April 2025 GMT
Gwamnatin kasar Saudiya ta yi allawadai da HKI a kissan da take wa falasdinawa a Gaza, a jiya talata a gaban kutun ICJ. Saudiya ta bayyana cewa gwamnatin HKI ta sabawa dokokin kasa da kasa da dama a kissan kiyashin da take yi a Gaza.
Wakilin kasar a gaban kotun Muhammad Saud Al-Nasser, ya kara da cewa, HKI ta ci gaba ta sabawa wadannan dokoki, amma kuma bata da dalilan saba masu.
Banda kissan kiyashin da take yi a Gaza, Al-Nasser ya ce HKI ta maida Gaza kofai, ta rusa mafi yawan gine-ginen yankin, sannan ta hana shigowar abinci da ruwa da magunguna zuwa yankin, wadanda ko wane daya daga cikinsu take hakkin bil’adama ne wanda yake kaiwa ga laifin yaki.
Gwamnatin Saudiya ta gabatar da wannan jawabin ne a rana ta biyu da bude zaman da kotun ta ICJ tayi don tattaunwa da kuma jin ra’ayin kasashe dangane da take hakkin bi’adaman da HKI take yi a Gaza. A halin yanzu fiye da kwamaki 50 kenan da gwamnatin HKI ta ke hana shigowar abinci da magunguna da kuma bukatun falasdinawa zuwa yankin.
Har’ila yau kotun ta girka wannan zaman ne don tattauna yadda HKI take mu’amala da umurnin ta danganda take hakkin bil’adama a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka
Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), ta yi alƙawarin kare dimokuraɗiyya da kuma inganta tsaro a yankin Yammacin Afirka.
Wannan alƙawarin na zuwa ne a dai-dai lokacin da yankin ke fuskantar matsalolin tsaro da na juyin mulki.
Yadda aka yi bikin naɗa Rarara sarkin wakar ƙasar Hausa a Daura Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a KanoAn yanke wannan shawara ne a taron shugabannin ƙasashen ECOWAS karo na 68, wanda aka gudanar a Abuja a ranar Lahadi.
Shugaba Bola Tinubu, wanda Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya wakilta, ya yi kira ga ƙasashen ECOWAS da su zauna lafiya tare da haɗa kai.
Ya yi gargaɗi ncewa ƙungiyar tana samun rauni idan ƙasashe suka rabu.
Ya ce ƙasashen Yammacin Afirka ba wai waje ɗaya suka haɗa ba, face suna da tarihi, al’adu da gwagwarmaya iri ɗaya da ta haɗa su.
Shugaba Tinubu, ya bayyana cewa duk da cewa rashin jituwa na iya faruwa tsakanin ƙasashe, bai kamata hakan ya karya zumunci da makomar ƙasashen yankin ba.
Ya zayyano matsalolin da yankin ke fuskanta, kamar ta’addanci, rikice-rikice, tsattsauran ra’ayi, juyin mulki, laifukan ƙetare iyaka, yawaitar makamai, barazana a Intanet, sauyin yanayi, ƙarancin abinci da sauransu.
Ya ce waɗannan matsaloli ba su da iyaka, kuma ƙasa ɗaya ba za ta iya magance su ba.
Tinubu ya tarbi shugabannin ECOWAS zuwa Abuja, inda ya yi fatan taron zai ƙara amincewa da juna, ƙarfafa haɗin kai, tare da sake ɗora ECOWAS bisa ginshiƙan adalci da makoma ɗaya.
A yayin taron, ECOWAS ta kuma mayar da hankali kan bunƙasar tattalin arziƙi ta hanyar kamfanoni masu zaman kansu.
Shugaban Hukumar ECOWAS, Dokta Omar Alieu Touray, ya sanar da kafa Majalisar Kasuwanci ta ECOWAS.
An naɗa fitaccen ɗan kasuwan Najeriya, Alhaji Aliko Dangote, a matsayin shugaban farko na wannan majalisa.
Shugaban ƙasar Saliyo kuma Shugaban ECOWAS, Julius Maada Bio, ya bayyana taron a matsayin mai muhimmanci.
Ya ce yankin Yammacin Afirka na fuskantar manyan ƙalubale na tsaro, dimokuraɗiyya da tattalin arziƙi, kuma shawarwarin da za a yanke za su shafi sama da mutum miliyan 400.
Ya kuma bayyana cewa an yi murnar cikar ECOWAS shekaru 50 da kafuwa.