Gaza: Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Asabar
Published: 26th, April 2025 GMT
Jiragen yakin HKi sun kai hare-hare da safiyar yau Asabar a birnin Gaza da hakan ya yi sanadiyyar samun shahidai da dama.
Mutane 4 sun yi shahada a harin na jiragen ‘yan sahayoniyar akan wani gida dake unguwar “al-Sabrah’ a kudancin birnin Gaza.
Haka nan kuma jiragen yakin na HKI sun kai wani harin da asubahin yau Asabar akan wani gidan da yake a sansanin ‘yan hijira da “Mukhayyam-Shati’i.
Majiyar Falasdinawa ta kuma ambaci cewa, da asubahin yau Asabar sojojin HKI sun tarwatsa wasu gidaje a yankunan da suke gabashin birnin Kudus.
Dama a jiya Juma’a jiragen yakin HKI sun kai hari akan wata makaranta da take kunshe da ‘yan hijira na Yarmuk dake tsakiyar birnin Gaza wanda shi ma ya yi sanadiyyar shahadar mutane 3.
A tsakiyar yankin na Gaza kuwa, manyan bindigogin HKI sun kai hare-hare a gabashin sansanin ‘al-Nusairat”.
A jiya kadai, Falasdinawa 48 ne su ka yi shahada a wasu hare-hare biyu da ‘yan sahayoniyar su ka kai wa gidaje biyu a yankunan “Murtaji” da “al-fakhari” dake cikin garin “Khan-Yunusu” a kudancin zirin Gaza.
A efe daya, sojojin HKI suna ci gaba da tilastawa Falasdinawan yin hijira daga yankunan “Turkiman, da Jadid da suke a Arewacin unguwar Zaytun.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
Ambaliya sanadiyyar wani mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya ta yi ajalin mutane 30 a Arewacin China, lamarin da ya tilasta kwashe mutane fiye da 80,000 zuwa Beijing, babban birnin kasar.
Jaridar Beijing Daily ta ruwaito cewa ruwan saman ya haddasa rufe hanyoyi da dama da kuma katsewar lantarki a kauyuka sama da 130 yayin da jami’an agaji ke ci gaba da aikin ceto.
Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a AlkaleriA jiya Litinin ce Shugaban China, Xi Jinping ya ba da umarnin daukar matakan gaggauwa a yankunan da ke fuskantar hadarin ambaliya sakamakon mamakon ruwan da ake hasashen za a ci gaba da tafkawa.
Xi Jimping ya bukaci mahukuntan yankunan da ke fuskantar hadarin ambaliyar da su gaggauta samar da tsare-tsare domin kubutar da jama’a.
A yanzu haka ana hasashen samun saukar mamakon ruwan sama har zuwa gobe Laraba a wasu yankuna sama da 10 na China.
Tuni dai mahukunta suka sanar da bayar da tallafin kudi yuan miliyan 550 — kwatankwacin dalar Amurka miliyan 76.7 ga yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa.
Gwamnatin kasar ta ce ta ware yuan miliyan 200 — kwatankwacin dalar Amurka miliyan 27.86 musamman ga birnin Beijing, inda ruwan sama kamar da bakin kwarya ya kashe akalla mutane 30 tare da haddasa barna mai yawa.
Bayanai sun ce ambaliyar ruwan ta kuma shafi lardunan Hebei, da Liaoning, da kuma Shandong, lamarin da ya haifar da asara mai yawa da asarar dukiya.