Aminiya:
2025-07-31@22:23:35 GMT

NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya

Published: 29th, April 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Rahotanni suna nuna cewa farashin shinkafa, ɗaya daga cikin nau’ukan abincin da ’yan Najeriya suka fi ci, ya karye a wasu sassan ƙasar.

Sauyin farashin ya sa ana tambayoyi — shin me ya haifar da wannan sauyi? Kuma me hakan ke iya haifarwa a rayuwar talaka?

NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki” DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

A kan wannan sauyi da dalilansa ne shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farashin shinkafa karyewa Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani

Gwamnatin Jihar Jigawa ta horas da Malaman makarantun sakandare kimanin dubu 20 ilimin fasahar sadarwar zamani (digital).

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawaga daga Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta ƙasa (NITDA) da Cibiyar Zaman Lafiya ƙarƙashin jagorancin Farfesa Hauwa Ibrahim da take Amurka, a ziyarar ban girma da suka kai a gidan gwamnati da ke Dutse.

Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah

Ya ce: “Mun gabatar da cibiya ta dijital don malamai, don sadarwa da kuma kula da ilmantarwa a matakin farko, mun sanya hannu kan haɗin gwiwa na shekaru biyar tare da NewGlobe don ƙarfafa ƙa’idojin rubutu da ƙididdiga ta amfani da kayan aikin dijital.

“Don haka shirin ku ya yi daidai da gyare-gyaren da muke da su kuma yana ƙara ƙimar ilimi matuƙa.” In ji Namadi.

Gwamna Namadi ya kuma nanata ƙudirin gwamnatin Jigawa na ɗorewar shirin, yana mai cewa, “Ina tabbatar muku: Za mu mallaki wannan shiri, za mu ci gaba da faɗaɗa shi, Kwamishinoninmu na ilimi a matakin farko da kuma na manyan makarantu za su sa ido a kansa.”

Darakta mai riƙon ƙwarya na dijital a Hukumar NITDA, Dokta Ahmed Tambuwal ya bayyana hangen nesa na ƙasa da ke jagorantar shirin.

“Muna nan a matsayin wani ɓangare na Hukumarmu ta NITDA na ci gaba da sadaukar da kai don aiwatar da ajandar Sabuwar Najeriya na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.”

“Babban ginshiƙi na wannan ajandar ita ce rarraba tattalin arzikin Najeriya ta hanyar fasahar dijital.”

Tambuwal ya bayyana cewa, NITDA tana ci gaba wajen cimma buri na kashi 70% na ilimin zamani a shekarar 2027, yana mai jaddada buƙatar haɗin gwiwa don cimma burin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya