Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
Published: 30th, April 2025 GMT
Tsoffin ma’aikatan Hukumar Shirya Jarabawar (NECO), da suka yi ritaya na neman a biya su haƙƙoƙinsu da suke bin bashi.
Shugaban ƙungiyar tsofffin ma’aikatan, Dokta Abdullahi Rotimi Williams ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar da hedikwatar kungiyar a Minna, babban birnin Neja.
Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta NijeriyaShugaban ya kuma koka kan yadda gwamnatin Nijeriya ta maida ritaya abin fargaba a wurin ma’aikata saboda tarin ƙalubalen da ke biyo bayan hakan, musamman maƙalewar haƙƙoƙinsu.
“Da yawa tsoron ritaya ake yi yanzu. Don haka wannan ƙungiyar za ta taimaka wajen rage waɗannan matsalolin.
“Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne na lafiya. Don haka ina roƙon shugaban hukumar da ya tabbatar cewa daga yanzu an kammala shirye-shiryen da suka kamata kafin ma’aikacin NECO ya yi ritaya.”
Ya kuma ce duk da jagororin hukumar na yanzu sun biya wasu daga cikin haƙƙoƙin nasu, ba a kai ga biyan alawus ɗin ƙarin girma ba, da na tafiye-tafiye ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta haramta liƙa hotuna ko rubutu marasa ma’ana a A-Daidaita-Sahu
Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano ta sanar da haramta rubuce-rubuce ko liƙa hotuna “marasa ma’ana” ko na batsa a kan baburan A-Saidaita-Sahu a fadin jihar.
Wannan mataki, wanda Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha ya jagoranta, yana da nufin tabbatar da ɗa’a da kuma tabbatar da cewa abubuwan da ake nunawa a bainar jama’a sun dace da ƙa’idojin hukumar.
A cewar Abdullahi Sani Sulaiman, Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, an ɗauki wannan mataki ne a sakamakon ƙorafe-ƙorafen al’ummaar Kano game da yadda masu A-Daidaita-Sahu sahu ke ado da hotuna da rubuce-rubuce masu ban haushi a bainar jama’a.
Abba El-Mustapha ya jaddada cewa dokar da ta kafa Hukumar ta ba ta cikakken iko don sa ido da gurfanar da masu laifi. Don tabbatar da bin doka, El-Mustapha ya jagoranci wata tawaga ta musamman a wani gangamin wayar da kai zuwa manyan tituna a Kano, ciki har da Titin Maiduguri, Titin Zaria, da Titin Sani Marshal.
Mai neman aiki ya suma bayan matarsa ta haifi ’yan uku Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMAA yayin aikin, ya nanata cewa hukumar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda aka samu da laifin karya ka’idojinta, ba tare da la’akari da matsayinsa ba.
El-Mustapha ya ƙara da cewa, bisa ga umarnin hukumar, duk wani aikin adabi ko na fasaha dole ne a miƙa shi ga Hukumar ta tantance shi kafin a fitar da shi ga jama’a.
Ya yi kira ga al’umma da su ba hukumar cikakken goyon baya da haɗin kai don ci gaban Jihar Kano.
Wannan sabon mataki ya biyo bayan wani shiri na wayar da kai da aka yi a baya inda hukumar ta tattauna da fiye da masu adaidaita sahu 20, inda ta yi musu gargaɗi game da sabbin dokokin. Hukumar ta bayyana cewa sabuwar dokar ta fara aiki cikakke.