Aminiya:
2025-07-23@23:44:02 GMT

Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47

Published: 29th, April 2025 GMT

Wani saurayi ya wallafa wani labarinsa a kafar sada zumunta ta Reddit tare da yin nadama, inda ya ce matar da suke soyayya ta faɗa masa cewa, an haife ta ne a shekarar 1998, har sai da ya duba bayanan fasfo dinta.

A wani lamari mai ban al’ajabi da ban tsoro, matashin ɗan shekara 26 ya girgiza bayan ya gano cewa, matar da yake soyayya da ita da nufin aure, bayan shafe shekaru huɗu suna tare tana da shekara 47, ba 27 ba, kamar yadda ta yi iƙirari.

An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok

Saurayin ya tafi shafin Reddit don ya wallafa labarinsa na nadama, inda ya ce, matar ta sha gaya masa cewa, an haife ta ne a watan Afrilun 1998, amma ya gano an haife ta a 1977 shekara 48 ke nan.

Saurayin ya rubuta a cikin shafin intanet cewa, “ina soyayya tare da budurwata har tsawon shekaru 4, kuma koyaushe tana ikirarin an haife ta a watan Afrilu ‘1998, amma na gano a ainihin lokacin da aka haife ta shi ne 1977.

Saurayin ya ce, ba shi da wani dalili na yin shakku, domin matar ta yi kama da ’yar shekara 27, ba wanda ya taba tunanin ta kusa 50 ba, amma ya yarda cewa akwai wasu alamomi a tsawon tafiyar soyayyar.

“Akwai wasu alamomi a lokacin da muke tare, amma na zabi in yi watsi da su tunda ba ni da gogewa kan gano ainihin (wannan ita ce alakar soyayya ta ta farko mai tsawo),” in ji shi, inda ya kara da cewa, matar ta damu da kamanninta, kuma duk kawayenta sun fi shekara 27 sosai.

“Duk lokacin da na nemi ta nuna min wasu takardu kamar fasfo sai ta ƙi nuna min, ta ba da uzuri na banza da kokarin kauce wa batun.”

A yayin binciken, saurayin ya kuma sami hoton gwajin ciki, wanda ’yan watanni kafin su hadu kuma su fara soyayya.

Kafofin sada zumunta na zamani sun mayar da martani kan batun, yayin da sakonni suka yi ta yaduwa, daruruwan mutane sun sharhi, inda akasari ke fada wa mutumin ya kawo karshen dangantakarsa da matar da aka gina ta bisa karya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: budurwa Saurayi Shekaru

এছাড়াও পড়ুন:

Asibitin ATBUTH za ta fara gwajin rigakafin zazzaɓin Lassa

Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓarkewa (ATBUTH) da ke Bauchi zai fara gwajin rigakafin cutar zazzabin Lassa.

Wannan shiri na da nufin tabbatar da ingancin rigakafin, kuma wani ɓangare ne na babban shiri mai kasashe da yawa mai suna “Background Rates of Adverse Events for Vaccine Evaluation in Africa (BRAVE).”

ATBUTH na daga cikin cibiyoyin kiwon lafiya huɗu a Najeriya da aka zaɓa don wannan aikin na tsawon shekaru uku (tare da yiwuwar ƙarin shekaru biyu don sa ido). Sauran su ne Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya (Owo) da Babban Asibitin Irrua da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Benin.

Wannan shiri, wanda Gidauniyar Ƙasa da Ƙasa kan Cututtukan Masu Saurin Yaɗuwa a Najeriya (IFAIN) ke gudanarwa tare da haɗin gwiwar Global Vaccine Data Network, zai tantance yanayin kiwon lafiya na yau da kullun a cikin al’umma kafin a gabatar da rigakafin.

Bayanan farkon za su taimaka wajen gano duk wani mummunan tasiri da zai iya faruwa bayan an ba da rigakafin.

A cewar Farfesa Yusuf Jibrin Bara, Babban Daraktan Kula da Lafiya na ATBUTH, wannan aikin yana nuna ci gaban binciken Najeriya.

Dokta Bernard Ebruke, Daraktan IFAIN na Bincike a Najeriya, ya jaddada cewa aikin BRAVE zai ƙarfafa tsarin sa ido da tattara bayanai don tabbatar da lafiyar rigakafi.

Aikin zai tattara bayanai daga marasa lafiya da suka haɗa da yara, mata masu juna biyu da masu jego, da kuma sassan kula da manya na ATBUTH, tare da mayar da hankali kan yanayin da ke da alaƙa da zazzabin Lassa da kuma rigakafin nan gaba.

Wannan zai samar da mahimman bayanai kan yawan cututtuka a Jihar Bauchi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Kamfanonin lantarki ya zu katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Asibitin ATBUTH za ta fara gwajin rigakafin zazzaɓin Lassa
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Libya Ta Tasa Keyar Baƙin Haure Yan Kasar Sudan 700 Zuwa Kasarsu
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin