Aminiya:
2025-06-15@16:30:25 GMT

An kashe sojoji 12 a barikin Nijar

Published: 27th, April 2025 GMT

An kashe sojoji 12 a yankin Tillaberi na yammacin ƙasar mai iyaka da Mali da Burkina Faso, yankin da ke zama tungar masu iƙirarin jihadi da ’yan ina da kisa masu nasaba da ’yan ƙungiyoyin al Qaeda da IS.

Ma’aikatar tsaron Nijar ta sanar da cewa an yi wa dakarunta na bataliyar ko-ta-kwana mai suna Almahao kwanton ɓauna ne a wani kauye da ke kusa da Sakoira na yammacin Tillaberi, inda sojan suka jima suna ɓarin wuta da ’yan ta’adda kafin a kawo musu ɗauki.

An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa

Gwamnatin ta bayyana cewa tuni ta cafke mutane biyu da ake zargi da kai harin a barikin sojojin da ke da nisan mil shida daga ƙauyen Sakoira a jihar ta Tillaberi.

A baya gwamnatin ƙasar ta sanar da kashe ’yan ta’adda tara, ta kuma ƙwace makamai daga hannu masu iƙirarin jihadi da suka kai wani harin da ta daƙile a yankin.

A yankin Tahoua mai iyaka da Nijeriya, rundunar tsaron Nijar ɗin ta sanar da ɗauki ba dadi da Lakurawa masu yawan yin kutse kuma suna kai hari ga bututun man fetur ɗinta da ke zuwa gaɓar teku a Benin.

Nijar Mali da kuma Burkina faso sun shafe sama da shekaru 10 ƙarƙashin barazanar ƴan ta‘adda masu iƙirarin jihadi da ke afkawa jami’an tsaro da kuma fararen hula lokaci zuwa lokaci.

To sai dai kuma ƙididdiga ta nuna ƙaruwar kai hare-hare tun bayan da sojojin ƙasashen uku suka yanke shawarar kifar da gwamnatin fararen hula.

Rikicin yankin Sahel da ya samo asali daga ƙasar Mali a 2012, wanda kuma ya faɗaɗa har zuwa ƙasashen Burkina Faso da Nijar da kuma Benin da ya halaka dubban mutane kama daga sojoji har zuwa farar hula.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: bariki Nijar

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya yi karin haske game da taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarta a Kazakhstan, yana mai cewa, Sin na da yakininta hanyar taro, ita da sauran kasashen yankin tsakiyar Asiya biyar, za su zurfafa dunkulewa, da amincewa da juna, da gina matsaya guda ta fuskar hadin gwiwa, da zurfafa daidaiton dabarun ci gaba, da daga matsayin hadin gwiwarsu a fannoni daban daban, da kara kuzarin gina al’umma mai makomar bai daya ta Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya.

 

Bisa gayyatar da shugaban jamhuriyar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya yi masa, shugaba Xi Jinping zai halarci taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, tsakanin ranekun 16 zuwa 18 ga watan nan na Yuni. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara