An kashe sojoji 12 a yankin Tillaberi na yammacin ƙasar mai iyaka da Mali da Burkina Faso, yankin da ke zama tungar masu iƙirarin jihadi da ’yan ina da kisa masu nasaba da ’yan ƙungiyoyin al Qaeda da IS.
Ma’aikatar tsaron Nijar ta sanar da cewa an yi wa dakarunta na bataliyar ko-ta-kwana mai suna Almahao kwanton ɓauna ne a wani kauye da ke kusa da Sakoira na yammacin Tillaberi, inda sojan suka jima suna ɓarin wuta da ’yan ta’adda kafin a kawo musu ɗauki.
Gwamnatin ta bayyana cewa tuni ta cafke mutane biyu da ake zargi da kai harin a barikin sojojin da ke da nisan mil shida daga ƙauyen Sakoira a jihar ta Tillaberi.
A baya gwamnatin ƙasar ta sanar da kashe ’yan ta’adda tara, ta kuma ƙwace makamai daga hannu masu iƙirarin jihadi da suka kai wani harin da ta daƙile a yankin.
A yankin Tahoua mai iyaka da Nijeriya, rundunar tsaron Nijar ɗin ta sanar da ɗauki ba dadi da Lakurawa masu yawan yin kutse kuma suna kai hari ga bututun man fetur ɗinta da ke zuwa gaɓar teku a Benin.
Nijar Mali da kuma Burkina faso sun shafe sama da shekaru 10 ƙarƙashin barazanar ƴan ta‘adda masu iƙirarin jihadi da ke afkawa jami’an tsaro da kuma fararen hula lokaci zuwa lokaci.
To sai dai kuma ƙididdiga ta nuna ƙaruwar kai hare-hare tun bayan da sojojin ƙasashen uku suka yanke shawarar kifar da gwamnatin fararen hula.
Rikicin yankin Sahel da ya samo asali daga ƙasar Mali a 2012, wanda kuma ya faɗaɗa har zuwa ƙasashen Burkina Faso da Nijar da kuma Benin da ya halaka dubban mutane kama daga sojoji har zuwa farar hula.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Jamhuriyar Nijar.
Mataimakin shugaban kasar na farko Mohammad-Reza Aref ya ce Iran na ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar da sauran kasashen nahiyar Afirka bisa tsarin juyin juya halin Musulunci.
Aref ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da ministan man fetur na kasar Nijar Sahabi Oumarou wanda ke Tehran, inda yake jagorantar wata tawaga, domin halartar taron hadin gwiwar tattalin arzikin Iran da Afirka karo na uku.
Ya ce da gaske ne gwamnatin Iran mai ci a yanzu tana son raya dangantakar da ke tsakaninta da kasashen Afirka ciki har da Nijar dangane da batutuwan da suka dace.
Ya kara da cewa, “Kasancewar manyan jami’an Nijar a taron da kuma kwamitin hadin gwiwa wani mataki ne mai ban sha’awa na inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.”
Mataimakin shugaban kasar ya jaddada cewa, bunkasa alaka da Nijar abu ne mai matukar muhimmanci, “idan aka yi la’akari da matsayinta kan ci gaban yanki da na kasa da kasa da kuma ra’ayi daya kan batutuwan Falasdinu da Lebanon.”
A yayin da yake tsokaci ga kiran da ministan na Nijar ya yi na inganta alaka a fannin noma, man fetur, da makamashi mai dorewa, Aref ya bayyana wadannan fannoni guda uku a matsayin muhimman batutuwan da suka shafi dangantakar Iran da Nijar, wadanda ya ce kwamitin hadin gwiwa zai duba su.
Yayin da yake tsokaci kan dangantakar tattalin arziki, ya ce, ya kamata kamfanoni masu zaman kansu na kasashen biyu su zuba jari don ciyar da matakin hadin gwiwa zuwa matsayi mafi girma.