Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa ’yan sanda umarnin daina tsaron manyan mutane a faɗin Najeriya.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ne, ya bayyana hakan a ranar Lahadi.

’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi

Onanuga, ya ce daga yanzu ’yan sanda za su mayar da hankalinsu ne aikin kare al’umma da yaƙar ’yan ta’adda.

An ɗauki wannan mataki ne a wani taron tsaro da aka gudanar a Abuja, wanda manyan shugabannin tsaro suka halarta, ciki har da shugabannin ’yan sanda, sojin sama, sojin ƙasa da hukumar DSS.

Sabon tsarin ya nuna cewa duk wani babban mutum da yake buƙatar tsaro dole ne, ya nemi jami’an tsaro daga Hukumar NSCDC maimakon ’yan sanda.

Najeriya ba ta da isassun ’yan sanda a yankunan karkara, kuma hakan yana haifar da tsaiko wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Saboda haka Shugaba Tinubu, ya umarci a ƙara yawan ’yan sandan da ke bai wa jama’a tsaro.

Onanuga, ya kuma ce Shugaban Ƙasa ya amince da ɗaukar ƙarin sabbin ’yan sanda 30,000.

Gwamnatin Tarayya za ta haɗa kai da gwamnatocin jihohi domin inganta cibiyoyin horas da ’yan sanda a faɗin Najeriya.

Taron tsaron da aka gudanar a ranar Lahadi, ya samu halartar Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Sunday Kelvin Aneke, Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, da Darakta-Janar na DSS, Tosin Adeola Ajayi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?
  • ’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara
  • Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta
  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana
  • Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya
  • Gwamnatin Kebbi Ta Bayar da Umarnin Rufe Makarantu a Jihar