Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin Farfesa Amina Salihi Bayero, a matsayin sabuwar Shugabar Jami’ar Northwest.

Naɗin nata zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Disamban 2025, har zuwa tsawon shekaru biyar.

EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar, ta ce gwamnan ya amince da naɗin ne bayan  tantancewa da kwamitin gudanarwar jami’ar ya yi mata.

A matsayinsa na jagoran jami’ar, Gwamna Abba, ya yaba wa shugaban kwamitin da mambobinsa kan jajircewarsu wajen bin ƙa’idojin tantancewar.

Haka kuma ya nemi a yi mata addu’ar samun nasara wajen gudanar da jagorancin Jami’ar.

Farfesa Amina Salihi Bayero ƙwararriya ce a fannin Chemistry, musamman Analytical Chemistry, kuma ita ce mace ta farko da ta samu digiri na uku a fannin daga Jami’ar Bayero Kano.

Ta taɓa riƙe muƙamai da dama a harkar ilimi da gudanarwa, ciki har da shugabar sashen Chemistry, da kuma Mataimakiyar Shugabar Jami’a (DVC) a Jami’ar Yusuf Maitama Sule.

Ana girmama ta saboda jajircewarta wajen horar da matasan masana kimiyya.

Ana sa ran naɗin nata zai ƙara ɗaukaka martabar jami’ar, ya inganta tsarin ilimi, tare da bai wa mata ƙofar samun manyan muƙamai a Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Kungiyar AU Ta yi Tir Da Harin Da RSF  Takai A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80