Ministan harkokin wajen Iran ya nufi birnin Muscat na kasar Oman a yau domin gudanar da zaman tattaunawa ba na kai tsaye ba da Amurka

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya sanar da cewa: A yau ne ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya nufi birnin Muscat na kasar Oman a karkashin jagorancin tawagar diflomasiyya da fasaha don shiga zagaye na uku na shawarwarin da ba na kai tsaye ba da Amurka ta hanyar shiga tsakanin mahukuntan Oman.

Baqa’i ya bayyana cewa: Bangarorin biyu sun amince da gudanar da tarukan fasaha tare da halartar manyan jami’an shawarwari, yana mai bayanin cewa “bisa tsarin da Oman ta shirya da kuma hadin gwiwa tsakanin Iran da Amurka, za a gudanar da tarukan fasaha da shawarwari kai tsaye tsakanin ministan harkokin wajen Iran da wakilin shugaban Amurka na musamman a ranar Asabar.”

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Ci gaban da ake samu a shawarwarin yana bukatar daya bangare ya nuna kyakykyawar fahimta, da gaske, da kuma hakikanin gaskiya, yana mai jaddada cewa: Tawagar Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi aiki ne bisa gogewar da ta gabata da kuma dabi’ar daya bangaren, kuma ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen cimma halaltacciyar hakki da muradun al’ummar Iran.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen Iran

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar

Shugaban kasar Ukrain Volodymyr Zelensky ya fito fili ya bayyana cewa bai amince da sabon shirin shugaban kasar Amurka Donal Trump na kawo karshen yaki a kasarsa. Ya kuma bayyana cewa kasar Ukraine tana cikin mafi munin hali a tarihin kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa shugaban kasar Amurka yana takurawa kasarsa ta amince da al-amura guda 28 da ya gabatar wanda a fadinsa zai kawo karshen yakin shekari kimani 3 wanda kasarsa take fafatawa da kasar Rasha.

Labarin ya kara da cewa daga cikin al-amuran da shugaban ya gabatar a wannan shirin kawo karshen yaki a Ukraine sun hada da amincewa da zaben raba gardaman da aka gudanar a shekara 2014 wanda ya hade tsibirin Cremea da kasar Rasha, amincewa da mamayar da kasar Rasha tayiwa yankin Donesk da Luganks wadanda suka zabi kasancewa bangaren kasar Rasha har’ila yau da  kawo karshen burinta na zama mamba a cikin kungiyar tsaro ta NATO.

Trump ya bukaci Ukraine ta kawo karshen samuwar sojojin kasar a dai-dai wuraren da take fafatawa da kasar Rasha a halin yanzu.

Kakakin fadar kremlin Dmitry Peskov ya yi kira ga shugaba Zelesky  ya amince da tattaunawa da kuma fahintar juna a kan wannan yakin, ko kuma ya fuskanci hatsarin kara rasa wasu yankuna na kasarsa.

Shugaban dai yana cikin tsaka mai wuya, saboda rashin amincewa da shawarwarin da shugaba Trump ya gabatar zai sa kasar Ukrai ta rasa babban aboki kamar Amurka. Sannan a dayan bangaren kuma amincewa da wadan nan shawarwari kaskanci ne da rashin mutunci ga kasarsa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yan Wasan Kasar Iran Sun tashi Da Lambobin Yabo 81 A Wasannin Zumunci Tsakanin Kasashen Musulmi November 22, 2025 Shugaban Rasha yace Ba zai Janye Ayyukan Soji  Da Yake Yi A Kasar Ukrain Ba November 21, 2025 Kwamitin Sulhu Na MDD Ya yi Tsokaci Kan Rashin Tsaro A Najeriya November 21, 2025 Araqchi: Iran Ta Shirya Tsaf Fiye Da Kowanne Lokacin  Musamman Bayan Yakin Kwanaki 12 November 21, 2025 China ta ce Ya Kamata A Aiwatar Da Sakamakon Taron Kolin Tianjin Don Inganta Kungiyar SCO November 21, 2025 Iran Ta yi Gargadi Game Da Sakamakon Da  Zai Iya Faruwa A Yankin Bayan Shigar Isra’ila Kasar Siriya November 21, 2025 Araqchi: Yarjejeniyar  Da Aka Cimma Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA A Kasar Masar Ta Rushe November 21, 2025 Kakakin Rundunar ‘IRGC’: Yakin Kwanaki 12 Ya Nuna Karfin Kariyar Makaman Masu Linzamin Iran November 21, 2025 Iran Da Wasu Kasashe Bakwai Sun Mayar Da Martani Kan Hudurin IAEA Kan Kasar Iran November 21, 2025 Kungiyar Hamas Ta Yi Kiran Da A Sanya Isra’ila Cikin Jerin Masu Aikata Abin Kunya Saboda Kashe Yara November 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijar:  Dubban Mutane Sun Tarbi Janar Thiani Bayan Komarwa Birnin Yamai
  • Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar
  • Yan Wasan Kasar Iran Sun tashi Da Lambobin Yabo 81 A Wasannin Zumunci Tsakanin Kasashen Musulmi
  • Tinubu Ya Jaddada Goyon Bayan Gwamnatin Tarayya Ga Muhimman Tsare-Tsaren Kaduna.
  • Araqchi: Yarjejeniyar  Da Aka Cimma Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA A Kasar Masar Ta Rushe
  • Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka
  • Kotu ta sanya ranar fara shari’ar shugabannin ƙungiyar Ansaru
  • AU ta yi Allah-wadai da tsoma bakin kasashen waje a harkokin tsaron Afirka
  • Ribadu ya jagoranci tawaga zuwa Amurka don ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: A Yanzu Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka