HausaTv:
2025-05-18@17:07:01 GMT

Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar

Published: 28th, April 2025 GMT

Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa  da ita ba.

 A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an  gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.

Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”

Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.

Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.

A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato

Aƙalla mutane bakwai sun mutu yayin da wasu 11 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya faru a ƙauyen Essa da ke kan hanyar Agaie-Badeggi, ƙaramar hukumar Katcha, jihar Neja.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa motar ɗauke da hatsi ta gwamnatin tarayya ce, kuma fasinjojinta maza ne kimanin 36, daga Legas zuwa Kano.

Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato  An Tsinci Gawarwakin Yara Biyar Cikin Tsohuwar Mota A Nasarawa

Hatsarin ya faru ne da ƙarfe 3 na daren ranar Lahadi, lokacin da direban ya yi ƙoƙarin ƙetare wani ɓangare mara kyau na hanyar da ake ginawa.

Daraktan hukumar kula da sufuri na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana kan aikin ceto da binciken kan iftila’in.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
  • Iran Ta Jaddada Kawo Karshen Bakar Siyasar gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Kan Al’ummar Falasdinu
  • Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh                                                                                                              
  • Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • Saudiya Ta Samar Da Wata Manhaja Ta Kiwon Lafiyar Mahajjata A Cikin Harsun 8 A Duniya
  • Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci
  • Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Mutum 10 sun rasu sakamakon rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Rasha Da Ukraine sun tabbatar da aikewa da tawaga domin tattaunawa a Turkiyya