HausaTv:
2025-12-13@16:49:19 GMT

Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar

Published: 28th, April 2025 GMT

Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa  da ita ba.

 A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an  gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.

Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”

Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.

Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.

A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda

Kotun Kolin Najeriya ta soke afuwar da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya yi wa Maryam Sanda, inda ta ce shugaban ya wuce makadi da rawa ta hanyar yin afuwa ga wacce har yanzu kararta ke gaban kotu.

A hukuncin da aka yanke ranar Juma’a, kotun ta yanke hukunci da rinjayen alƙalai huɗu cikin biyar, inda ta tabbatar da hukuncin kisa da Babban Kotun Abuja ta yanke, kuma Kotun Daukaka Kara ta tabbatar.

‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’ Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa

An yanke wa Sanda hukunci ne a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, a lokacin rikicin cikin gida a gidansu da ke Abuja.

Kotun ta yi watsi da ƙarar da ta shigar, tana mai cewa masu gabatar da ƙara sun tabbatar da laifin kisan kai ba tare da wata shakka ba.

A hukuncin jagoran alkalan, Mai Shari’a Moore Adumein ya ce Kotun Daukaka Kara ta yi daidai wajen tabbatar da hukuncin kotun farko.

Ya ce shiga tsakani na shugaban ƙasa bai dace ba a irin wannan yanayi.

Mai Shari’a Adumein ya ce: “Ba daidai ba ne ga bangaren zartarwa ya yi ƙoƙarin amfani da ikon afuwa kan laifin kisan kai, wanda har yanzu kararsa na gaban kotu.”

A watan Oktoba, an rage hukuncin Maryam zuwa shekaru 12 a kurkuku bayan Shugaba Tinubu ya amince da jerin sunayen wadanda ya yi wa afuwa.

Wannan mataki ya biyo bayan nazari da ya fara da sunaye 175, kafin daga baya a cire wasu saboda irin laifukan da suka aikata.

A lokacin, Mai Ba da Shawara na Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce rage hukuncin Sanda “ya dogara ne da tausayi saboda amfanin ’ya’yanta da kuma kyakkyawan halinta,” sannan ya ce ta nuna “nadama.”

Wannan mataki ya janyo suka a fadin Najeriya, ciki har da adawa daga dangin marigayi Bello.

Hukuncin na Kotun Kolin yanzu dai ya soke afuwar ta Shugaban Ƙasa.

Maryam Sanda ta shafe kusan shekaru shida a kurkuku, kuma hukuncin da aka rage zai bar ta da kusan shekaru shida nan gaba. Amma da hukuncin na ranar Juma’a, an dawo da hukuncin kisa da aka yanke mata tun farko.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a