HausaTv:
2025-12-14@05:41:47 GMT

Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar

Published: 28th, April 2025 GMT

Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa  da ita ba.

 A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an  gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.

Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”

Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.

Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.

A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara

Daga Usman Muhammad Zaria

Shugaban kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bukaci ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar  tabbatar da ganin cewa kananan hukumonin jihar 27 sun wallafa cikakken kundin kasafin kudadensu cikin zangon farko na sabuwar shekara.

Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa, ya bayyana haka ne lokacin tantance kiyasin kasafin kudin sabuwar shekara na ma’aikatar kananan hukumomi.

Ya kuma yi kira ga ma’aikatar da ta duba batun rashin biyan albashi ga wasu daga cikin nadaddun kansiloli, kasancewar yanzu haka akwai nadaddun kansiloli 21 da ba sa samun albashin su.

Ya kara da cewar, kwamitin ya samu koke kan tsallake albashin wasu ma’aikatan kananan hukumomi sakamakon aikin tantance ma’aikata na IPPS  ta yadda wasu ma’aikatan sun yi ritaya ba tare sun karbi albashin da aka tsallake su ba.

A nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar kananan hikumomin Jihar, Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa, ya bada tabbacin yin duk abinda ya kamata domin magance wadannan batutuwa.

Ya ce ma’aikatar ta yi kiyasin kashe naira miliyan dubu 13 domin gudanar da manyan ayyuka da harkokin yau da kullum a shekarar 2026.

Hannun Giwa, ya kuma bayyana cewar daga cikin manyan ayyuka akwai gyaran ofisoshin shiyya na jami’an duba kananan hukumomi guda 7.

Yana mai cewar za’a kuma kammala aikin ginin sabbin ofisoshi dake kananan hukumomin Babura da Kafin Hausa.

Kazalika, Kwamishinan ya ce za’a sayi motocin aiki da babura ga jami’an duba kananan hukimomi da mataimakansu, tare da kudaden gudanarwa domin ziyarar aiki a lungu da sakon kananan hukumomin jihar 27.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC