Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
Published: 28th, April 2025 GMT
Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Uganda ta sanar da cewa, an kawo karshen Ebola da ta bulla a kasar bayan da aka dauki kwanaki 42 ba tare da an sami mutum daya wanda ya sake kamuwa da ita ba.
A wani bayani da ya fito daga hukumar kiwon lafiya ta duniya ( WHO), ta bayyana cewa, a lokacin bullar cutar an gabatar da mutane 14 masu dauke da ita, an tabbatar da 12 daga cikinsu, sai wasu biyu da ba a same ta a tare da su ba.
Haka nan kuma hukumar lafiyar ta ce, an sami mutuwar mutane 4 daga cikin wadanda su ka kamu da cutar ta Ebola, wasu mutane 10 kuma sun warke.”
Watanni 9 da su ka gabata ne dai aka tabbatar da bullar cutar a birnin Kamfala bayan da wani mutum da yake dauke da ita ya rasu.
Dajukan da kasar ta Uganda take da su, suna a matsayin matattarar cutar ta Ebola ce, wacce a karon farko ta bulla a cikin kasar a 2000.
A yankin yammacin Afirka cutar Ebola ta kashe fiye da mutane 11,000 a tsakanin 2013 zuwa 2016.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile juyin mulki a Benin
Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin.
Fadar gwammnatin faransa ta Élysée ta ce bisa bukatar hukumomin Benin ta bayar da “goyon baya ta fuskar bayar da bayanai da dabaru” ga sojojin Benin a matsayin martani ga yunkurin juyin mulki da aka dakile a karshen makon da ya gabata.
Sanarwar ta ce Emmanuel Macron ya yi hadin gwiwa” da “musayar bayanai da kasashen yankin,” in ji daya daga cikin masu ba shi shawara ga manema labarai, a cewar AFP.
Shugaban Faransa ya yi magana a ranar Lahadi da takwaransa na Benin, Patrice Talon, wanda sojoji suka nemi su hambarar, da kuma shugaban Najeriya da kuma kasar Saliyo.
Kasar Saliyo ce ke rike da shugabancin kungiyar ECOWAS, wacce ta dauki matakin soja don taimakawa Cotonou wajen dakile yunkurin juyin mulki.
Dama a jiya Shugaban Bola Tinubu ya tabbatar da cewa sojojin kasarsa sun taimaka wajen dakile juyin mulki a benin.
Wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai magana da yawun shugaban ya fitar ta ambato Shugaba Tinubu yana cewa “sojojin sun mayar da martani wajen ceto dimokuraɗiyya ta 35.”
Sanarwar ta ce shugaba Tinubu ya dauki mataki bayan samun buƙatar neman ɗauki daga Benin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda December 9, 2025 Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci