An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba
Published: 27th, April 2025 GMT
Rundunar ’yan sanda a Jihar Taraba ta cafke mutane tara kan zargin satar mutane.
Haka kuma, rundunar ta gano bindigogi ƙirar AK-47 guda huɗu da kuma bindigogi ƙirar AK-49 guda uku da alburusai guda arba’in da biyar a hannun waɗanda aka cafke.
Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa Ƙungiyoyin da suka yi shuhura a Firimiyar IngilaKakakin rundunar ’yan sandan, ASP James Lashen ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a birnin Jalingo.
Ya bayyana sunayen ababen zargin da aka kama da suka haɗa da Shehu Ibrahim da Abdullahi Haruna da kuma Yusuf Bello.
Sauran kuma sun haɗa da Sulaiman Muhammed da Tijjani Bello da Muhammed Umar.
Kazalika, akwai kuma Adamu Ibrahim da Solomon Nathaniel da kuma Haruna Adamu.
ASP James, ya ce ’yan sanda sun sami nasarar kama waɗanda ake zargin ne bayan samu bayanan asiri dangane da ayyukansu.
Ya ce waɗanda aka kama sun shaida wa ’yan sanda cewa suna daga cikin guggun masu satar mutane a jihohin Gombe da Filato da Kaduna da Bauchi da kuma Jihar Taraba.
ASP James ya bayyana cewa ana ci gaba da faɗaɗa bincike kan ababen zargin kuma nan gaba kaɗan za a gurfanar da su a kotu.
Ya ce kwamishinan ’yan sanda, Emmanuel Bretet ya ɗauki alwashin murkushe masu aikata laifuka a Jihar Taraba domin ganin an kare rayuka da dukiyar al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Taraba Satar Mutane
এছাড়াও পড়ুন:
Miliyoyin Mutane Sun Gudanar Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”
Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.
A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.