Aminiya:
2025-07-30@21:52:49 GMT

An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba

Published: 27th, April 2025 GMT

Rundunar ’yan sanda a Jihar Taraba ta cafke mutane tara kan zargin satar mutane.

Haka kuma, rundunar ta gano bindigogi ƙirar AK-47 guda huɗu da kuma bindigogi ƙirar AK-49 guda uku da alburusai guda arba’in da biyar a hannun waɗanda aka cafke.

Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa Ƙungiyoyin da suka yi shuhura a Firimiyar Ingila

Kakakin rundunar ’yan sandan, ASP James Lashen ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a birnin Jalingo.

Ya bayyana sunayen ababen zargin da aka kama da suka haɗa da Shehu Ibrahim da Abdullahi Haruna da kuma Yusuf Bello.

Sauran kuma sun haɗa da Sulaiman Muhammed da Tijjani Bello da Muhammed Umar.

Kazalika, akwai kuma Adamu Ibrahim da Solomon Nathaniel da kuma Haruna Adamu.

ASP James, ya ce ’yan sanda sun sami nasarar kama waɗanda ake zargin ne bayan samu bayanan asiri dangane da ayyukansu.

Ya ce waɗanda aka kama sun shaida wa ’yan sanda cewa suna daga cikin guggun masu satar mutane a jihohin Gombe da Filato da Kaduna da Bauchi da kuma Jihar Taraba.

ASP James ya bayyana cewa ana ci gaba da faɗaɗa bincike kan ababen zargin kuma nan gaba kaɗan za a gurfanar da su a kotu.

Ya ce kwamishinan ’yan sanda, Emmanuel Bretet ya ɗauki alwashin murkushe masu aikata laifuka a Jihar Taraba domin ganin an kare rayuka da dukiyar al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Taraba Satar Mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo

Fiye da mutane 21 ne suka mutu a wani harin ta’addanci da aka kai kan wani coci a gabashin Kongo

Rahotonni sun tabbatar da cewa; Sama da mutane 21 ne aka kashe a wani hari da mayakan ‘yan tawayen kungiyar Allied Democratic Forces (ADF) suka kai kan wani cocin Katolika da ke gabashin Kongo, wanda ya hada da kona gidaje da shaguna a yankin.

A ranar Lahadin da ta gabata ne mayakan da suke da alaka da kungiyar Allied Democratic Forces (ADF) da ke samun goyon bayan kungiyar ‘yan ta’adda ta ISIS suka kaddamar da harin ta’addanci kan wata majami’ar Katolika a gabashin Kongo.

“Sama da mutane 21 ne aka kashe a ciki da wajen cocin,” Dieudonné Duranthabo, wani jami’in kungiyoyin farar hula a Komanda, ya shaidawa kamfanin dillacin labarai na Associated Press cewa: “Sun gano akalla gawarwakin mutane uku da suka kone, sannan an kona gidaje da dama.”

Harin ya faru ne da misalin karfe 1:00 na safiyar Lahadi a cikin wani  cocin Katolika da ke yankin Komanda a gabashin Kongo. An kuma kona gidaje da shaguna da dama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo