An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba
Published: 27th, April 2025 GMT
Rundunar ’yan sanda a Jihar Taraba ta cafke mutane tara kan zargin satar mutane.
Haka kuma, rundunar ta gano bindigogi ƙirar AK-47 guda huɗu da kuma bindigogi ƙirar AK-49 guda uku da alburusai guda arba’in da biyar a hannun waɗanda aka cafke.
Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa Ƙungiyoyin da suka yi shuhura a Firimiyar IngilaKakakin rundunar ’yan sandan, ASP James Lashen ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a birnin Jalingo.
Ya bayyana sunayen ababen zargin da aka kama da suka haɗa da Shehu Ibrahim da Abdullahi Haruna da kuma Yusuf Bello.
Sauran kuma sun haɗa da Sulaiman Muhammed da Tijjani Bello da Muhammed Umar.
Kazalika, akwai kuma Adamu Ibrahim da Solomon Nathaniel da kuma Haruna Adamu.
ASP James, ya ce ’yan sanda sun sami nasarar kama waɗanda ake zargin ne bayan samu bayanan asiri dangane da ayyukansu.
Ya ce waɗanda aka kama sun shaida wa ’yan sanda cewa suna daga cikin guggun masu satar mutane a jihohin Gombe da Filato da Kaduna da Bauchi da kuma Jihar Taraba.
ASP James ya bayyana cewa ana ci gaba da faɗaɗa bincike kan ababen zargin kuma nan gaba kaɗan za a gurfanar da su a kotu.
Ya ce kwamishinan ’yan sanda, Emmanuel Bretet ya ɗauki alwashin murkushe masu aikata laifuka a Jihar Taraba domin ganin an kare rayuka da dukiyar al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Taraba Satar Mutane
এছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
Daga Usman Mohammed Zaria
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Injiniya (Dr.) Muhammad Uba, ya yaba wa Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, bisa amincewa da sabbin ayyukan gina hanyoyi a fadin jihar, ciki har da na Birnin Kudu.
Ya ce wannan mataki na cikin ajandar gwamnati 12, musamman wajen inganta ci gaban ababen more rayuwa.
A cewarsa, Birnin Kudu za ta amfana da gina hanyoyi masu tsawon kilomita 113, wanda ya hada da hanyoyin kauyuka da wadanda ke hada al’umma da sauran sassan jihar.
Dr. Uba ya bayyana aikin a matsayin babban ci gaba wajen saukaka zirga-zirga, inganta harkokin tattalin arziki da samun sauki ga muhimman ayyuka ga jama’a.
Ya bayyana tabbacin cewa za a dade ana cin moriyar aikin hanyoyin, tare da hanzar ayyukan ci gaba da bunkasar karamar hukumar.
Shugaban ya yi addu’ar dorewar zaman lafiya da cigaba a Birnin Kudu tare da yin alkawarin ci gaba da hada kai da gwamnatin jiha domin tabbatar da cewa jama’a suna amfana da fa’idodin dimokuraɗiyya.