Leadership News Hausa:
2025-04-30@19:57:40 GMT

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

Published: 28th, April 2025 GMT

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

Gwamnatin tarayya ta ɗauki nauyin dukkanin buƙatun ɗaliban na zana jarabawar, ciki har da abinci da wurin kwana, har na tsawon kwanaki uku. Kwamishinan ilimi na jihar Bauchi, Dakta Lawal Mohammed Rimin Zayam, ya yaba da wannan mataki na JAMB, yana mai kira ga iyaye da su tura ‘ya’yansu dake da lalura ta musamman makaranta domin samun ilimi.

Kwamishinan ya kuma yi kira ga al’umma da iyaye su fahimci muhimmancin ilimi, musamman ga yara masu naƙasa, yana mai cewa gwamnati za ta ci gaba da wayar da kan iyaye don ganin suna tura ‘ya’yansu makaranta.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jarrabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”

 

To, bayanai a sama sun nuna ra’ayi iri daya na gwamnatocin dimbin kasashe masu tasowa. Ban da haka, wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar yada labarai ta Sin CGTN, da jami’ar Renmin ta kasar Sin suka gudanar a kasashe 38, ya nuna cewa, matakan ramuwar gayya da kasar Sin ta dauka kan kasar Amurka suna samun goyon baya tsakanin al’ummun kasashe daban daban, inda a dimbin kasashe masu tasowa da suka hada da Najeriya, da Kenya, da Masar, da Ghana, da Afirka ta Kudu, da Turkiya, matakan kasar Sin suka samu goyon baya daga mutane fiye da kaso 70% da aka gudanar da bincike kansu. Kana a kasashen yamma da suka hada da Faransa, da Jamus, da Canada, da Birtaniya, da dai sauransu, jimillar ta kai tsakanin kaso 65.5% zuwa 70.5%.

 

Sai dai kasar Sin ba ta son yakin ciniki, ko da yake tana wakiltar ra’ayi mai adalci na akasarin kasashe. Kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, “Babu mai samun nasara a yakin harajin fito, da na ciniki.” Amma, bisa la’akari da cewa kasar Amurka ce ta ta da yakin ciniki, to, kasar Sin ba za ta taba mika wuyarta ba, kuma ba za ta yi hakuri da matakin cin zarafi ba. Sin ta nanata cewa, idan kasar Amurka na son daidaita al’amarin ta hanyar tattaunawa, to, ya kamata ta “daina barazana da matsin lamba, ta yi tattaunawa bisa tushen daidaito, da mutunta juna, da amfanawa juna.”

 

Hakika, ban da wadannan abubuwan da aka ambata, don kaddamar da tattaunawa, ana bukatar sanin ya kamata, wanda kasar Amurka ta rasa. Misali, yadda kasar Amurka ta janye jikinta daga dimbin kungiyoyin kasa da kasa, da yarjeniyoyin duniya, da daina samar da tallafi ga sauran kasashe, sun nuna yunkurinta na kaucewa daukar nauyi sakamakon raguwar karfinta a fannin tattalin arziki. Sai dai wannan yanayi mai kunci bai hana ta ci gaba da neman ba da umarni ga sauran kasashe, da cin zarafinsu ba. Ban da haka, mu kan ga yadda shugabannin kasar Amurka suke ba da umarni da gyara shi cikin sauri, da yin karairayi yadda suka ga dama, da wulakanta takwarorinsu na sauran kasashe, da kasa kare bayanan sirrin da suka shafi yaki, wadanda suka nuna gazawarsu wajen aiki. Ma iya cewa, yanzu haka, kasar Amurka tamkar damisar takarda ce, mai ban tsoro amma maras karfi.

 

Za mu jira lokacin da za a iya komawa teburin shawarwari don tattauna batun kawo karshen yakin ciniki, inda za a jira har zuwa lokacin da kasar Amurka za ta gamu da dimbin matsaloli, ta yadda za ta yi watsi da matakan zalunci, da sake samun sanin ya kamata. Amma yanzu muna iya tabbatar da matakin da ya kamata kasashe masu tasowa su dauka, wato karfafa hadin kansu, maimakon mika wuya ga kasar Amurka, wadda ta kasance tamkar wata “damisar takarda”, da ke neman cin zarafin sauran kasashe, da ta da rikici a duniya. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa