HausaTv:
2025-04-30@19:22:17 GMT

 Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza

Published: 30th, April 2025 GMT

A yau Laraba sa jijjifin Safiya an sami shahidai 3 a Gaza da hakan ya kara yawan shahidai zuwa 40 a cikin sa’o’i 24.

Bugu da kari, baya ga shahidan da suke faduwa a kowace rana, ana fama da matsananciyar yunwa a cikin yankin, bayan karewar kayan abincin HKI ta sake komawa yaki kwanaki 44 da su ka gabata.

A cikin sansanin ‘yan hijira na “Nusairat”  mutane 3 sun yi shahada da su ka hada da karamar yarinya sanadiyyar harin da sojojin na HKI su ka kai wa yankin.

A gabashin birnin Khan-Yunus ma dai wasu Falasdinawa sun yi shahada.

Daga ranar 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu adadin wadanda su ka yi shahada sun wuce 52,000,wadanda su ka jikkata kuma sun haura 100,000.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta bayyana cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila’ tana aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa ana gani kai tsaye a tauraron dan Adam

Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International a yau Talata ta yi Allah wadai da shirun da duniya ta yi game da yadda gwamnatin yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya take aiwatar da kisan kiyashi a zirin Gaza, kai tsaye duniya na gani ta hanyar tauraron dan Adama.

A yayin gabatar da rahoton shekara-shekara na kungiyar ta Amnesty kan kare hakkin bil’adama a duniya Agnes Callamard, sakatariyar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International, ta ce tun ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023, duniya ke kallon yadda ake aiwatar da kisan kare dangi kai tsaye a tauraron dan Adam a Zirin Gaza.

Ta kara da cewa, “Sun ga kasashe kamar babu abin da zasu iya saboda da rauni” tare da nuna cewa “gwamnatin mamayar Isra’ila na kashe dubban Falasdinawa maza da mata, ta hanyar kisan kiyashi kan dukkanin iyalai da suka hada da kananan yara, da lalata gidaje, rusa cibiyoyin tsare rayuka, rusa asibitoci da cibiyoyin ilimi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza