Shugaban Amurka ya bayyana cewa: Fira ministan Isra’ila Netanyahu ba zai ja shi zuwa shiga cikin yaki da Iran ba, kuma a shirye yake ya gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci da shugaban kasar Iran

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya jaddada cewa: Ba za a sanya shi shiga yaki da Iran ba saboda manufofin fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu.

Trump ya kara da cewa a wata hira da ya yi da mujallar Time, a shirye yake ya gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci ko kuma shugaban kasar Iran.

Duk da imanin da ya yi cewa: Amurka da Iran za su iya cimma yarjejeniya, amma Trump ya sake nanata barazanarsa na cewa idan ba a cimma matsaya ba, to zai bi sahun ‘yan yahayoniyya wajen kai wa Iran hari, domin ganin cewa, Iran ba ta mallaki makamin nukiliya ba.

Trump ya kuma musanta yunkurin cewa zai hana Isra’ila kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta yanke wa wani shugaban ISWAP Hussaini Ismaila, hukuncin ɗaurin shekaru 20 a gidan yari bayan samun sa da aikata laifukan ta’addanci.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a Emeka Nwite, ya yanke hukuncin ne bayan Ismaila, wanda ake kira Mai Tangaran, ya amsa tuhume-tuhume guda huɗu da Hukumar DSS ta gabatar a kansa.

Gwamna Abba ya gabatar da N1.36trn a matsayin kasafin 2026 Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda matsalar tsaro a Najeriya

DSS ta ce Ismaila ne, ya jagoranci kai wasu hare-haren ta’addanci a Kano a shekarar 2012.

Hare-haren sun haɗa da harin Hedikwatar ’Yan Sanda ta Bompai, Barikin ’Yan Sandan Mopol a titin Kabuga, ofishin ’yan sanda na Farm Centre, ofishin ’yan sanda na Unguwa Uku, da wasu wurare.

Mutane da dama sun jikkata a yayin kai waɗannan hare-hare.

An kama Ismaila ne a ranar 31 ga watan Agustan 2017, a ƙauyen Tsamiyya Babba da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa, a Jihar Kano.

Daga nan aka gurfanar da shi a gaban kotu bisa dokar hana aikata ta’addanci ta 2013.

Shari’ar ta ɗauki lokaci saboda ɗaukaka ƙara da kuma tabbatar da bayanan da ya bayar da farko ba tursasa shi aka yi ba.

A ƙarshe, lauyoyin gwamnati sun kira shaidu biyar, ciki har da jami’an DSS da mutanen da harin ya shafa.

Da farko Ismaila, ya ƙi amincewa da laifin da ake tuhumarsa amma bayan gabatar da shaida na biyar, ya sauya maganarsa ya amsa laifin.

Lauyansa daga Hukumar LAC, P. B. Onijah, ya roƙi kotu ta yi masa sassauci, inda bayyana cewa Ismaila ya nuna nadama kuma bai son ɓata wa kotu lokaci.

A hukuncin da ya yanke, Mai Shari’a Nwite ya yanke masa shekar 15 kan tuhumar farko da kuma shekaru 20 kan sauran kowace tuhuma uku.

Dukkanin hukuncin za su tafi a lokaci guda, kuma za su fara aiki tun daga ranar da aka kama shi a shekarar 2017.

Alƙalin ya umarci Hukumar Gyaran Hali ta tsare shi a gidan yari da Babban Kwamandan Hukumar ya zaɓa.

Bayan ya kammala zaman gidan yari, dole a yi masa horon gyaran hali da kawar da ra’ayin ƙiyayya kafin a sake mayar da shi cikin al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Yarjejeniyar  Da Aka Cimma Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA A Kasar Masar Ta Rushe
  • Amurka ta Shawarci Ukraine ta amince da yankunan da Rasha ta mamaye mata
  • Sudan ta yaba da kokarin Amurka da Saudiyya na kawo karshen rikicin kasar
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: A Yanzu Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Daraktar Hukumar IAEA Ya Ce: Suna Tuntubar Juna Da Iran Kuma Masu Bincikensu Sun Kamo Kasar
  • An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari
  • Kasar Maziko Tayi Watsi Da Shirin Trump Na Kai Harin Soji Kan Iyakar Kasar.
  • Iran : Dole ne kudirin Amurka ya kare hakkin Falasdinawa da samuwar kasar Falasdinu
  • Saudiyya za ta kara hannun jarinta a Amurka zuwa dala tiriliyan daya
  • Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis