Shugaban Amurka ya bayyana cewa: Fira ministan Isra’ila Netanyahu ba zai ja shi zuwa shiga cikin yaki da Iran ba, kuma a shirye yake ya gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci da shugaban kasar Iran

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya jaddada cewa: Ba za a sanya shi shiga yaki da Iran ba saboda manufofin fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu.

Trump ya kara da cewa a wata hira da ya yi da mujallar Time, a shirye yake ya gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci ko kuma shugaban kasar Iran.

Duk da imanin da ya yi cewa: Amurka da Iran za su iya cimma yarjejeniya, amma Trump ya sake nanata barazanarsa na cewa idan ba a cimma matsaya ba, to zai bi sahun ‘yan yahayoniyya wajen kai wa Iran hari, domin ganin cewa, Iran ba ta mallaki makamin nukiliya ba.

Trump ya kuma musanta yunkurin cewa zai hana Isra’ila kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Qassem: Kawar Da Hizbullah Ne Babban Burin Isra’ila A Lebanon

Babban Sakataren Hezbollah Sheikh Naim Qassem ya bayyana cewa “Amurka, ta hanyar wakilanta na Isra’ila, tana neman kawar da karfin gwagwarmayar Lebanon da kuma ba sojojin kasar makamai don fuskantar Hezbollah,” yana mai jaddada cewa manufar wannan matakin shine “kawar da karfin soja da duk wani karfi  fadin Lebanon domin Isra’ila ta ci gaba da cin karenta babu babbaa duk inda ta ga dama a cikin kasar.”

Sheikh Naim Qassem ya kara da cewa “An kafa Hezbollah ne bisa ka’idojin jihadi,  kare mutunci mutunci, da alfaharin Lebanon, da goyon bayan Falasdinu,” yana mai cewa “daga 2000 zuwa 2023, mun kasance cikin yanayi na tsoro.”

Ya bayyana cewa yakin baya-bayan yana a matsayin shinge ga mamayar Isra’ila, wanda ya tsayar da hankoron mamayar Isra’ila kan Lebanon a wasu iyakoki a kudancin Lebanon,” yana mai nuna cewa “Yarjejeniyar Nuwamba tana da muhimmanci domin ya haɗa da tura sojojin Lebanon a kudancin Kogin Litani.”

Ya ƙara da cewa, “Mu masu nasara ne saboda sojojin Lebanon suna nan a kudancin Kogin Litani, domin su ‘ya’yanmu ne. Kuma mu masu nasara ne a cikin wannan yarjejeniyar saboda ƙasar ta yi alƙawarin cika alkawalin da ta dauka.”

Sheikh Qassem ya zargi Amurka da “kasa aiwatar da alkawullanta ta hanyar tursasa Isra’ila yin aiki da yarjejeniyar, domin Lebanon za ta dawo da ‘yancinta da mutuncinta ne kawai idan Isra’ila ta janye.” Ya jaddada cewa “Amurka da Isra’ila suna tsoma baki a cikin makomar Lebanon, suna tantance ayyukan sojojinta, tattalin arzikinta, siyasa, da matsayinta na yankin.”

Ya bayyana cewa “matsin lamba da ake yi wa gwamnati domin ta yi sassauci ba tare da wani lamuni ba, zai kara karfafa gwiwar Isra’ila ne wajen yin gaban kanta a kasar Lebanon.”

Sheikh Qassem ya ci gaba da cewa, “Isra’ila tana son ta mallaki Lebanon ta mayar da ita wurin da za ta kara faɗaɗa matsugunan yahudawa ‘yan share wuri zauna, a matsayin wani ɓangare na Shirin kafa Isra’ila Babba.” Ya nuna cewa “kowace rana suna fito da sabbin hujjoji, tun daga batun  kwance damarar makamai zuwa gindaya wa gwamnatin Lebanon sharudda masu tsauri kan Hizbullah, wanda hakan ke nuni da cwa Hizbullah da karfinta su ne Babbar matsala a gare su.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Masar Da Sudan Sun Jaddada Wajabcin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yankin November 12, 2025 Venezuela: Maduro Ya Sanya Hannu Kan Dokar Tsaron Kasa Mai Cikakkiyar Kariya November 12, 2025 UNICEF: Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza November 12, 2025 Ministocin harkokin wajen kasashen yamma sun yi Allah wadai da ta’asar RSF a El Fasher Darfur November 11, 2025 Abdel-Aty: Diflomasiyya Ce Kawai Hanyar Da Maido Da Zaman Lafiya A Libya November 11, 2025 Larijani : ‘babu wani sabon sako’ da muka aika wa Amurka November 11, 2025 Gaza : Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau 282 tun bayan aiwatar da ita November 11, 2025 Iraki : Ana zaben ‘yan majalisa don tsara makomar siyasar kasar November 11, 2025 Sudan ta soki shirun kasashen duniya game ta’asar dake faruwa a kasar November 11, 2025 Hamas ta soki kudurin Isra’ila na yin dokar hukuncin kisa kan laifin ta’addanci November 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin Juma’a Ya Bukaci Ganin An Kai Karar Donald Trump A Kotunan Duniya
  • Iran ta yi tir da G7 kan goyon bayan takunkuman Amurka
  • Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
  • Ramaphosa Ya Caccaki Trump Kan Kauracewa Taron G20 A Johannesburg
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki
  • Amurka Na Shirye-Shiryen Aikewa Da Sojoji Guda 1000 A Iyakar Isra’ila Da Yankin Gaza
  • Shugaban Iran Ya Aike Da Wasika Ta Musamman Zuwa Ga Yarima Mai Jiran Gado Na Saudiya
  • Sheikh Qassem: Kawar Da Hizbullah Ne Babban Burin Isra’ila A Lebanon
  • Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba