Aminiya:
2025-06-29@06:21:36 GMT

Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya

Published: 30th, April 2025 GMT

Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya ta naɗa Sheikh Bashir Aliyu Umar a matsayin shugabanta bayan rasuwar Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.

Wata sanarwa da majalisar ta fitar a yau Laraba ta ce an amince da shuagabancin Dokta Bashir ne kai-tsaye saboda kasancewarsa mataimakin shugaba.

A ranar Litinin ne Sheikh Hadiyyatullah ya rasu yana da shekara 81 a Jihar Osun.

“Nan gaba za a sanar da mataimakin shugaban,” in ji sanarwar da Nafiu Baba Ahmed ya sanya wa hannu a matsayin sakataren majalisar.

Sheikh Bashir sanannen malami ne kuma shi ne babban limamin masallacin Juma’a na Al-Furqan da ke Alu Avenue a Unguwar Nasarawa ta Jihar Kano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Majalisar Shari ar Musulunci

এছাড়াও পড়ুন:

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Wasan farko da Leicester za ta buga a gasar Championship zai kasance a gida, inda za ta kara da Sheffield Wednesday ranar Laraba, 10 ga watan Agusta mai zuwa.

A baya, Van Nistelrooy ya taɓa riƙe matsayin kocin riƙon ƙwarya na Manchester United, bayan da suka sallami Eric Ten Hag kafin su ɗauki Ruben Amorim daga Sporting CP ta ƙasar Portugal.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan 
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Jaddada Cewa: Iran Tana Da Hakkin Tace Sinadarin Uranium A Kasarta
  • Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
  •  Arakci:  Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
  • Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
  • Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
  • 2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya
  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
  • Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya