Abu Ubaidah: Mun Harbo Sojojin Mamaya 4 Daga Nesa A Beit-Hanun
Published: 26th, April 2025 GMT
Mai Magana da yawun dakarun ‘Kassam” Abu Ubaidah ya sanar da cewa; sun harbo sojojin mamaya 4 ta hanyar wani kwanton bauna da su ka yi musu a Beit-Hanun.
Kakakin dakarun na ” Kassam” ya kuma ce; Har yanzu suna ci gaba da kwamawa da ‘yan mamaya da kuma yi musu kwanton bauna a wurare mabanbanta.”
Abu Ubadah ya kuma jaddada cewa; ‘yan gwgawarmaya su ne ke zabin lokacin da wurin da za su kai wa abokan gaba hari, kuma jaruntarsu tana bayyana daga garin Beit Hanun zuwa Rafah, da hakan yake a a matsayin abin alfahari ta fuskar soja.
A ranar Alhamis din da ta gabata, ‘yan gwgawarmayar sun harbo sojojin HKI 4 daga cikinsu har da masu manyan mukamai, tare da halaka su da kuma jikkata wasu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Ya bayyana halin da aka shiga mara daɗi, inda ya jajanta wa iyalan waɗanda suka mutu da waɗanda suka yi asarar dukiyoyi, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta tallafa musu wajen sake gina musu gidajen su da sauya muhallinsu.
Fintiri ya kuma soki waɗanda ke yaɗa rahotannin ƙaryar game da lamarin, ba tare da fahimtar ainihin abin da ke faruwa ba, inda ya ce hakan yana da nasaba da tuggun siyasa da son zuciya.
Ya bayyana cewa maƙasudin ambaliyar sun haɗa da ruwan sama mai yawa da toshewar hanyoyin ruwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp