Aminiya:
2025-11-02@06:07:40 GMT

Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal

Published: 28th, April 2025 GMT

Miliyoyin mutane sun auka cikin yanayi na duhu sakamakon ɗaukewar wutar lantarki a ƙasar Sifaniya da wasu sassan Portugal.

Lamarin ya shafi harkokin sufuri da sadarwa, da ma harkokin kasuwanci da dama.

Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku

Sai dai asibitoci na gudanar da harkokinsu yadda aka saba saboda suna amfani da injinan janareto.

Shugabar gwamnati a yankin Madrid ta ce “abin da za mu yi shi ne mu nemi gwamnatin tarayya ta ayyana shiri na gaggawa don sojoji su kare doka da oda.”

Kamfanin lantarki na Sifaniya ya ce an gyara matsalar a yankunan arewaci da kudancin ƙasar.

Har yanzu dai ba a san abin da ya janyo matsalar ɗaukewar wutar ba, wadda ta shafi Portugal mai maƙwabtaka.

Bankin Sifaniya ya ce harkokin hada-hada ta intanet na ci gaba da aiki yadda ya kamata, sai dai an ambato wasu masu cirar kuɗi sun fuskanci ƙalubale a na’urar ATM.

A wani bidiyo da ya wallafa a shafin X, Mai Garin Madrid, Jose Luis Martinez-Almeida, ya buƙaci mazauna da su taƙaita zirga-zirgar saboda fargabar abin ka iya zuwa ya komo.

A Portugal kuwa, masu ruwa sun ce yana iya yankewa nan da kowane lokaci a yayin da jama’a ke tururuwar sayen ababen buƙata a manyan shaguna kamar tocilan, jannarera da batura.

Babban kamfanin lantarki na Portugal, EDP, ya shaida wa kwamstomi cewa babu takamaiman lokacin dawo da wutar da za a iya shafe sa’o’i kafin kammala gyara kamar yadda jaridar Publico ta ruwaito.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lantarki Sifaniya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

An zabi Doro ne bayan naɗin Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin sabon Shugaban Jam’iyyar APC ta ƙasa. Kakakin fadar shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana Doro a matsayin ƙwararren masani da ke da fiye da shekaru 20 na ƙwarewa a fannoni da dama ciki har da aikin asibiti, gudanar da harkokin magunguna, da jagoranci a Nijeriya da Birtaniya.

An haifi Doro a ranar 23 ga Janairu, 1969, a Kwall, ƙaramar hukumar Bassa ta jihar Plateau. Yana da digiri a fannin magunguna da shari’a, MBA a dabarun kasuwanci na IT, da kuma digiri na biyu a fannin aikin lafiya mai zurfi (Advanced Clinical Practice).

Da amincewar da aka yi masa a yau, ana sa ran Bernard Doro zai rantse a matsayin ɗan majalisar zartarwa (FEC) a zaman majalisar ministoci na gaba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar October 30, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15 October 30, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
  • Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai