Aminiya:
2025-09-17@23:21:23 GMT

Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal

Published: 28th, April 2025 GMT

Miliyoyin mutane sun auka cikin yanayi na duhu sakamakon ɗaukewar wutar lantarki a ƙasar Sifaniya da wasu sassan Portugal.

Lamarin ya shafi harkokin sufuri da sadarwa, da ma harkokin kasuwanci da dama.

Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku

Sai dai asibitoci na gudanar da harkokinsu yadda aka saba saboda suna amfani da injinan janareto.

Shugabar gwamnati a yankin Madrid ta ce “abin da za mu yi shi ne mu nemi gwamnatin tarayya ta ayyana shiri na gaggawa don sojoji su kare doka da oda.”

Kamfanin lantarki na Sifaniya ya ce an gyara matsalar a yankunan arewaci da kudancin ƙasar.

Har yanzu dai ba a san abin da ya janyo matsalar ɗaukewar wutar ba, wadda ta shafi Portugal mai maƙwabtaka.

Bankin Sifaniya ya ce harkokin hada-hada ta intanet na ci gaba da aiki yadda ya kamata, sai dai an ambato wasu masu cirar kuɗi sun fuskanci ƙalubale a na’urar ATM.

A wani bidiyo da ya wallafa a shafin X, Mai Garin Madrid, Jose Luis Martinez-Almeida, ya buƙaci mazauna da su taƙaita zirga-zirgar saboda fargabar abin ka iya zuwa ya komo.

A Portugal kuwa, masu ruwa sun ce yana iya yankewa nan da kowane lokaci a yayin da jama’a ke tururuwar sayen ababen buƙata a manyan shaguna kamar tocilan, jannarera da batura.

Babban kamfanin lantarki na Portugal, EDP, ya shaida wa kwamstomi cewa babu takamaiman lokacin dawo da wutar da za a iya shafe sa’o’i kafin kammala gyara kamar yadda jaridar Publico ta ruwaito.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lantarki Sifaniya

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Saboda wannan baiwa daga Allah, iyalai da ‘yan uwan mai akuyar suka sanar da shirye-shiryen gudanar da bikin murnar haihuwar ‘ya’yan akuyar a ranar Lahadi mai zuwa a Garun Dakasoye, karamar hukumar Garun Malam ta Jihar Kano, inda za a yi musu suna da kuma karatun Alkur’ani mai girma.

 

A nasa bangaren, mahaifin budurwar, Malam Aliyu dake Garin Dakasoye, ya tabbatar da cewa za su gudanar da bikin domin nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa wannan ni’ima da ya ba su.

 

Ya kara da cewa: “Mun gode wa Allah bisa wannan arziki, kuma muna sa ran gudanar da bikin tare da sanya musu suna domin nuna godiya ga Allah mai daukaka.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki