“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.

 

“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”

 

Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP

Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, ya fice daga jam’iyyar PDP.

Mai magana da yawun gwamnan, Daniel Alabrah, ne ya sanar da hakan a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook na ainihi, kodayake bai bayyana dalilin ficewar gwamnan daga jam’iyyar ba.

Har ila yau, bai bayyana ko Gwamna Diri zai koma APC mai mulki ko kuma hadakar ’yan adawa ta ADC ba.

Aminiya ta gano cewa Gwamna Diri yana halartar wani taro da mambobin majalisar zartarwa ta jiha, inda ya bayyana musu wannan bayani.

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Bayelsa, Rt. Hon. Abraham Ingobere, yana cikin mahalarta taron.

A cikin sa’o’i kaɗan da suka gabata, Gwamna Diri tare da tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, sun halarci bikin ƙaddamar da otal ɗin Best Western Plus da ke Yenagoa.

Haka kuma, dukkan mambobin PDP da ke cikin Majalisar Dokokin Jihar da kuma Kwamishinoni a Majalisar Zartarwa ta Jiha sun fice daga jam’iyyar.

Gwamna Diri ya taɓa zama Kwamishina a gwamnatin PDP a lokacin da Goodluck Jonathan ke matsayin Gwamnan Jihar Bayelsa. Haka kuma, ya kasance Babban Sakataren Gwamna Seriake Dickson, wanda shi ne wanda ya gabace shi.

An zaɓi Diri a matsayin ɗan Majalisar Wakilai a shekarar 2015 a ƙarƙashin PDP, sannan a 2019 aka zaɓe shi a matsayin Sanata mai wakiltar Bayelsa ta Tsakiya.

A shekarar 2020 aka zaɓe shi a matsayin Gwamnan Jihar Bayelsa, kuma aka sake zaɓar shi a 2023, duka a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa za ta tantance Amupitan a ranar Alhamis
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Dakta Umar Kabir Yusuf-Bakatsinen da ya kirkiro manhajar Masjid Suite da ke sada zumuncin hada masallaci da masallata
  • Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja