“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.

 

“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”

 

Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da rasuwar wasu mutum biyar sakamakon haɗura uku da suka auku a jihar.

Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya ce hatsrin farko ya faru ne da safiyar ranar Alhamis a unguwar Badawa Layin Day by Day ca Ƙaramar Hukumar Nassarawa.

Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin Jirgin sojin sama ya yi hatsari a Neja

Lamarin ya faru ne a wani gida mai faɗin kafa 25 da 20 wanda ya kama da wuta.

Ma’aikatan kashe gobara sun ceto wata yarinya mai shekara 10 daga a cikin gidan, amma daga baya ta rasu a asibiti.

An bai wa iyayenta gawarta.

Hatsari na biyu ya faru ne a Ƙauyen Badume Kanawa da ke Karamar Hukumar Bichi.

Wani mutum mai shekara 65, Sa’idu Gada, yana aiki a cikin rijiya lokacin da igiyar da ta ke riƙe da shi ta tsinke, ya faɗa ciki.

Ɗansa mai shekara 20, Sani Isyaku, ya shiga rijiya domin ceto shi, shi ma ya maƙale.

Wani mutum na uku, Yakubu Abdullahi mai shekara 60, ya shiga domin taimakonsu, shi ma daga bisani ya faɗa cikin rijiyar.

Ma’aikatan hukumar sun fito da su daga rijiyar, amma sun riga sun rasu.

An miƙa wa ’yan sandan Badume gawarwakinsu.

A wani lamari na daban kuma, wani yaro mai shekara 10, Hassan Iliyasu Haruna, ya zame tare da faɗa wa rijiya a Ƙaramar Hukumar Danbatta.

Ma’aikatan hukumar kashe gobara sun ceto shi, amma daga baya ya rasu.

An miƙa wa mahaifinsa gawar yaron.

Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Kano, Sani Anas, ya ja hankalin jama’a da su daina shiga rijiya domin ceto mutane, domin a cewarsa hakan na da hatsari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano