“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.

 

“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”

 

Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya tare da shugabannin Rundunonin Sojin Najeriya, za su ci gaba da kare duk wani jami’i da ke gudanar da aikinsa bisa doka.

Badaru, ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a taron da aka shirya domin bikin tunawa da Sojojin Najeriya na shekarar 2026 a Abuja.

’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa

Wannan na zuwa ne bayan ce-ce-ku-cen da ya faru ranar Talata tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da wani jami’in rundunar sojan ruwa, Laftanar A. M. Yerima.

An yi taƙaddama ne kan wani fili da ke Abuja da ake zargin mallakar wani tsohon Shugaban Rundunar Sojin Ruwa, Vice Admiral Awwal Gambo (mai ritaya) ne.

“A Ma’aikatar Tsaro, da kuma rundunonin sojoji, za mu ci gaba da kare jami’anmu masu aiki bisa doka,” in ji Badaru.

“Muna binciken al’amarin da ya faru, kuma muna tabbatar da cewa duk wani jami’i da yake aikinsa yadda doka ta tanada za a kare shi. Ba za mu bari wani abu ya same shi ba matuƙar yana yin aikinsa da kyau.”

Ministan, ya kuma sanar da sabon shirin gwamnati na haɗa tsofaffin sojoji cikin aikin tsaron al’umma da ci gaban yankuna ta hanyar shirin “Reclaiming the Ungoverned Space for Economic Benefits Programme (RUSEB-P)”.

Ya ce manufar shirin ita ce amfani da ƙwarewar tsofaffin jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a yankunan da ake samun rikice-rikice.

Badaru, ya bayyana cewa shirin RUSEB-P zai taimaka wajen rage aukuwar ta’addanci da kuma bunƙasa harkokin noma, hakar ma’adinai, da sauran ayyukan tattalin arziƙi.

Ya ƙara da cewa an kafa kwamiti da ke aiki kan yadda za a aiwatar da shirin.

Haka kuma, ya bayyana cewa gwamnati na shirin sake duba ‘Nigerian Legion Act’ domin kafa Ƙungiyar Tsofaffin Sojojin Najeriya (Veterans Federation of Nigeria – VFN), wacce za ta ƙarfafa tsarin kariya da tallafa wa walwalar tsofaffin jami’an tsaro.

Ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauye da za su inganta tsaron ƙasa, inganta walwalar sojoji, da kuma girmama sadaukarwar tsofaffin jami’an tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
  • Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi
  • Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • AIG Zubairu Ya Umurci ‘Yan Sanda a Kwara Su Ninka Kokarinsu Don Karfafa Tsaro
  • DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma