Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, ya bayyana cewa sauyin jam’iyyar da manyan ‘yan suke yi zuwa jam’iyyar APC ana kamba ma shi fiye da yadda ya kamata, yana cewa wannan sauyin ba zai shafi kokarinsa na neman mafita ga matsalolin Nijeriya ba. Ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a Kano yau Litinin.

El-Rufai ya bayyana cewa shi ne na farko da ya koma jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) daga APC a kokarinsa na warware matsalolin Nijeriya ta hanyar kawar da tsarin kawancen siyasa.

Ficewar El-Rufai Daga APC Babban Rashi Ne – Tsohon Hadimin Buhari El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC

“SDP ta hankali wajen nemo mafita ga matsalolin Nijeriya da kuma ba da dama ga wadanda a siyasance ta hanyar kawancen jam’iyyu” in ji El-Rufai.

Ya kara da cewa sauyin jam’iyyar ‘yan siyasa ba shi ne babban batu ba, a cewarsa, babban batu shi ne wanda zai iya warware matsalolin Nijeriya da kuma isar da wannan ga al’umma ta yadda za su fita zabe a ranar zabe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: matsalolin Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Umaurci Matawalle Ya Koma Kebbi a Cigaba da Kokarin Kubutar da Daliban da Aka Sace

Daga Bello Wakili

Shugaba Bola Tinubu ya umurci Ministan  Tsaro, Alhaji Bello Matawalle, da ya koma Jihar Kebbi biyo bayan sace dalibai  ’yan mata 24  a jihar.

An umurci Matawalle, wanda tsohon gwamnan Jihar Zamfara ne, da ya zauna a jihar domin sa ido kan ƙoƙarin  da ake yi na kubutar da ɗaliban da aka sace.

’Yan bindiga sun sace ɗalibai mata 24 na Makarantar Sakandare ta ’Yan Mata da ke garin Maga, Jihar Kebbi, da misalin  ƙarfe 4 na asubar ranar Litinin.

Matawalle, wanda ake sa ran zai isa Birnin Kebbi a ranar Juma’a, ya samu ƙwarewa wajen fuskantar matsalar ’yan fashi da garkuwa da mutane a lokacin da yake gwamnan Jihar Zamfara daga shekarar 2019 zuwa 2023.

Idan za a iya tunawa ranar 26 ga watan Fabrairun 2021, ’yan bindiga sun sace ɗalibai mata 279 da ke tsakanin shekaru 10 zuwa 17 a Makarantar Sakandare ta Kimiyya ta ’Yan Mata da ke Jangebe, a Jihar Zamfara. ’Yan bindigar sun saki dukkan waɗanda suka yi garkuwa da su a ranar 2 ga Maris 2021.

Shugaba Tinubu ya ɗage tafiyarsa da aka shirya zuwa Johannesburg, Afrika ta Kudu, da kuma Luanda, na kasar Angola, domin ya jira bahasin halin da ake ciki game da ’yan matan makarantar da aka sace a Kebbi da kuma harin da aka kai wa masu ibada na Cocin Christ Apostolic da ke Eruku, Jihar Kwara.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Tabbatar da Yunkurin Kafa Cibiyar Tarayya Ta Uku a Jigawa
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • Tinubu Ya Umaurci Matawalle Ya Koma Kebbi a Cigaba da Kokarin Kubutar da Daliban da Aka Sace
  • Babu wani addini da matsalar tsaron Nijeriya ta ƙyale — Fafaroma
  • Sai da Kwankwaso APC za ta iya samun nasara a 2027 — NNPP
  • Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai
  • IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka
  •  Iran Tana Cikin kasashe 10 Na Farko Da Su Ka Fi Yawan Wuraren Tarihi
  • Ribadu Ya Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Amurka Kan Zargin Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla