Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, ya bayyana cewa sauyin jam’iyyar da manyan ‘yan suke yi zuwa jam’iyyar APC ana kamba ma shi fiye da yadda ya kamata, yana cewa wannan sauyin ba zai shafi kokarinsa na neman mafita ga matsalolin Nijeriya ba. Ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a Kano yau Litinin.

El-Rufai ya bayyana cewa shi ne na farko da ya koma jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) daga APC a kokarinsa na warware matsalolin Nijeriya ta hanyar kawar da tsarin kawancen siyasa.

Ficewar El-Rufai Daga APC Babban Rashi Ne – Tsohon Hadimin Buhari El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC

“SDP ta hankali wajen nemo mafita ga matsalolin Nijeriya da kuma ba da dama ga wadanda a siyasance ta hanyar kawancen jam’iyyu” in ji El-Rufai.

Ya kara da cewa sauyin jam’iyyar ‘yan siyasa ba shi ne babban batu ba, a cewarsa, babban batu shi ne wanda zai iya warware matsalolin Nijeriya da kuma isar da wannan ga al’umma ta yadda za su fita zabe a ranar zabe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: matsalolin Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki

Wasu magidanta a garin Malam-Sidi, da ke Ƙaramar Hukumar Kwami a Jihar Gombe, sun yaba da aikin haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Gombe da UNICEF sula yi wajen rage matsalar ƙarancin abinci a tsakanin ƙananan yara.

Shirin, wanda ake kira PARSNIP, yana bai wa yara masu shekaru 6 zuwa 23 wani nau’in abinci na musamman mai suna SQ-LNS.

Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno

Wannan abincin yana ɗauke da sinadarai 24 da ke taimakawa wajen kare yara daga rashin abinci mai gina jiki da kuma bunƙasa lafiyarsu wajen girma.

A ziyarar da manema labarai suka kai, iyaye mata sun bayyana yadda shirin ya taimaka musu.

Malama Hussaina Bappayo ta ce SQ-LNS “abinci ne mai tasiri” saboda yadda ya taimaka wa yaranta sun ƙara ƙarfi da girma sosai.

Hakazalika, Malama Asmau Tela, ta ce ’yarta, wadda ta sha fama da gudawa da wasu ƙananan cututtuka, yanzu ta samy lafiya tun da ta fara cin wannan abinci.

Saboda nasarar shirin, iyaye mata da yawa suna zuwa cibiyoyin lafiya don karɓar SQ-LNS ga yaransu.

Wasu sun ce hakan ya rage musu kuɗin magani saboda yara sun daina yawan yin rashin lafiya.

Sai dai sun roƙi gwamnati da UNICEF su ƙara yawan abincin, domin yanzu ana fama da ƙarancinsa saboda buƙatar ta ƙaru.

Wasu iyayen, sun ce abincin ya taimaka sosai wajen rage yawan yara masu fama d ƙarancin abinci mai gina jiki, amma sun yi gargaɗin cewa idan ba a samun abincin, yara da yawa za su shiga hatsari.

Philomena Irene daga UNICEF ta bayyana cewa daga 2023 zuwa 2025, yara 106,248 ne suka amfana da SQ-LNS a Jihar Gombe.

Ta kuma ce sama da mata 20,347 ne suka samu horo kan kula da lafiyar uwa da jarirai, ciki har da yadda ake amfani da MUAC wajen auna girman yara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia
  • Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata
  • Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai
  • MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000