Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, ya bayyana cewa sauyin jam’iyyar da manyan ‘yan suke yi zuwa jam’iyyar APC ana kamba ma shi fiye da yadda ya kamata, yana cewa wannan sauyin ba zai shafi kokarinsa na neman mafita ga matsalolin Nijeriya ba. Ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a Kano yau Litinin.

El-Rufai ya bayyana cewa shi ne na farko da ya koma jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) daga APC a kokarinsa na warware matsalolin Nijeriya ta hanyar kawar da tsarin kawancen siyasa.

Ficewar El-Rufai Daga APC Babban Rashi Ne – Tsohon Hadimin Buhari El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC

“SDP ta hankali wajen nemo mafita ga matsalolin Nijeriya da kuma ba da dama ga wadanda a siyasance ta hanyar kawancen jam’iyyu” in ji El-Rufai.

Ya kara da cewa sauyin jam’iyyar ‘yan siyasa ba shi ne babban batu ba, a cewarsa, babban batu shi ne wanda zai iya warware matsalolin Nijeriya da kuma isar da wannan ga al’umma ta yadda za su fita zabe a ranar zabe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: matsalolin Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno

’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su, masu shekaru hudu da biyar, a Jihar Borno.

An ceto yaran ne a yayin wani samame da ’yan sanda suka kai a Ƙaramar Hukumar Jere, inda masu garkuwar suka je karbar kuɗin fansa.

Sanarwa da ASP Nahum Kenneth Daso, kakakin rundunar ya fitar ta ce, bayan sun sami rahoto a ranar 4 ga Disamba cewa yara uku sun bace, washegari masu garkuwar suka sako ɗaya daga cikin yaran da takardar neman naira miliyan 10 domin sakin sauran biyun.

A ranar ce jami’an rundunar suka kai samame a wurin da aka ware don karɓar kuɗin fansar.

Ganin hakan masu garkuwa da mutanen, suka farga da wannan tarko da aka musu nan da nan suka yi watsi da yaran suka gudu cikin duhu.

An ceto yaran ba tare da wani rauni ko biyan kuɗin fansa ba, kuma sun sake haɗuwa da iyalansu, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano waɗanda ake zargi.

Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Yobe, Naziru Abdulmajid, ya ba da umarnin zurfafa bincike kuma ya umurci jami’an rundunar da su qarfafa sintiri, su gudanar da ayyukan bincike mai tsauri, da kuma ci gaba da gudanar da ayyukansu don rage yawaitar aikata laifuka a baya-bayan nan.

Hukumar tsaron ta kuma yi kira ga mazauna yankin da su kasance cikin shiri da kuma bayar da rahoton ayyukan da ake zargi, tare da samar da lambobin tuntuɓar gaggawa don hanzarta kai xauki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • Nigeria: Har Yanzu Da Akwai Daliban Makaranta 250 Da Suke Hannun Masu Garkuwa Da Su
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia
  • Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata