Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai, ya bayyana cewa sauyin jam’iyyar da manyan ‘yan suke yi zuwa jam’iyyar APC ana kamba ma shi fiye da yadda ya kamata, yana cewa wannan sauyin ba zai shafi kokarinsa na neman mafita ga matsalolin Nijeriya ba. Ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da manema labarai a Kano yau Litinin.

El-Rufai ya bayyana cewa shi ne na farko da ya koma jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) daga APC a kokarinsa na warware matsalolin Nijeriya ta hanyar kawar da tsarin kawancen siyasa.

Ficewar El-Rufai Daga APC Babban Rashi Ne – Tsohon Hadimin Buhari El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC

“SDP ta hankali wajen nemo mafita ga matsalolin Nijeriya da kuma ba da dama ga wadanda a siyasance ta hanyar kawancen jam’iyyu” in ji El-Rufai.

Ya kara da cewa sauyin jam’iyyar ‘yan siyasa ba shi ne babban batu ba, a cewarsa, babban batu shi ne wanda zai iya warware matsalolin Nijeriya da kuma isar da wannan ga al’umma ta yadda za su fita zabe a ranar zabe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: matsalolin Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

APC ta rage wa Mata kuɗin tsayawa takara a Borno

Jam’iyyar APC reshen Jihar Borno ta rage wa mata kashi 50 cikin 100 na farashin fom ɗin tsayawa takara, makonni gabanin zaɓen kananan hukumomi da za a gudanar a ranar 13 ga Disamba, 2025.

Da yake sanar da hakan a Maiduguri, shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Bello Ayuba, ya ce an ɗauki matakin ne domin magance matsalar ƙarancin kuɗi da ke hana mata shiga siyasa da tsayawa takara.

Yadda Morocco ta kafa tarihin ɗaga Kofin Duniya na FIFA U20 Dembele ya dawo PSG bayan jinyar makonni

“Wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarin da muke yi na samar da daidaito ga mata a fagen siyasa.

“Muna son ganin mata da yawa suna jagoranci a matakin ƙasa, suna ba da gudummawa da ƙarfinsu wajen gudanar da mulki,” in ji Ayuba.

A cewarsa, “an ƙayyade farashin fom ɗin neman kujerar shugaban ƙaramar hukuma ga maza kan naira miliyan 2, yayin da fom ɗin kansila zai ci ₦500,000, amma mata za su biya rabin wannan adadi — ₦1 miliyan da ₦250,000.”

Ya ƙara da cewa an kafa kwamitocin tantancewa da sasantawa domin tabbatar da cewa zaɓen fidda gwani zai gudana cikin gaskiya da lumana a dukkan ƙananan hukumomi 27 da gundumomi 112 na jihar.

“Za a gudanar da zaɓen fidda gwani a lokaci guda a ƙarshen wannan watan domin guje wa maguɗin zaɓe,” in ji shi.

Ayuba ya jaddada aniyar jam’iyyar ta tabbatar da sahihin zaɓe, inda ya ce Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Borno (BOSIEC) za ta gudanar da babban zaɓen a ranar 13 ga Disamba, 2025.

“Mun himmatu wajen tabbatar da ɗorewar dimokuraɗiyya ta hanyar adalci, daidaiton jinsi, da kuma gudanar da zaɓe cikin lumana,” in ji shi.

“Mata na da matuƙar muhimmanci ga shugabanci, kuma wakilcinsu yana ƙarfafa tsarin mulki.”

Masu sa ido da ƙungiyoyin kare haƙƙin mata sun yaba da matakin jam’iyyar APC, inda suka bayyana shi a matsayin muhimmiyar hanya ta ƙara daidaiton jinsi a siyasar Jihar Borno.

Sun ce rage kuɗin fom ɗin tsayawa takara ga mata ba kawai zai ƙarfafa gwiwar mata masu neman tsayawa takara ba, har ma zai zaburar da ƙananan ‘yan mata su ga shugabanci a matsayin abin da za su iya cimma.

Wannan mataki dai ya yi daidai da kiraye-kirayen ƙasa da ƙasa na ƙara shigar da mata cikin harkokin mulki, tare da ƙarfafa imanin cewa dimokuraɗiyya na bunƙasa ne idan maza da mata suka haɗa kai wajen tsara makomar al’ummarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
  • Uba Sani ya yi wa ma’aikatan manyan makarantu ƙarin kashi 70 a albashi
  • Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsa
  • Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
  • An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba
  • Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Hanya Akan Kudi Sama Da Naira Biliyan 4
  • APC ta rage wa Mata kuɗin tsayawa takara a Borno
  • Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara
  • Gwamnati ta ɗauki matakin rage shan gishiri a Nijeriya