Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da kashe-kashen kisan kiyashi, kuma ana ci gaba da fama da yunwa a Gaza a daidai lokacin da kasashen duniya suka yi shiru

An shiga rana ta arba’in da fara sabon farmakin da haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa Zirin Gaza, a daidai lokacin da ake ci gaba da samun ta’adi da kisan kare dangi da ba a taba ganin irinsa ba, a daidai lokacin da Amurka ke goyon bayan ta’asar da kuma shiru na kasa da kasa wanda masu lura da al’amura suka bayyana a matsayin babban abin kunya.

A cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza, adadin wadanda suka yi shahada  sakamakon hare-haren ta’addancin ‘yan sahayoniyya ya kai 51,355 da kuma jikkatan wasu 117,248 tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023.

Adadin wadanda suka yi shahada da jikkata tun daga ranar 18 ga watan Maris na wannan shekara ta 2025, watau kwanaki arba’in, ya kai kimanin shahidai 2,000 da kuma jikkatan 5,207.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna

Aisha ta koma gidan mijinta, marigayi Muhammadu Buhari da ke Jihar Kaduna, bayan shafe kwanaki a Daura tana karɓar gaisuwa.

Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe, ce ta jagoranci tawagar gwamnatin jihar wajen tarbar Aisha a Filin Jirgin Sama na Kaduna a ranar Lahadi.

Tsohon shugaban jami’ar Kashere ya rasu a Abuja Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP

Daga cikin waɗanda suka tarbe ta akwai Shugabar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Munira Suleiman Tanimu, da wasu manyan jami’an gwamnati.

Tarbar da aka yi mata ta nuna yadda jihar ke ci gaba da girmama tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da iyalinsa bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban ƙasar nan.

Bayan tarbar ta, Dakta Hadiza ta raka Aisha Buhari da iyalanta zuwa gidan marigayin.

Wannan ya nunacewar iyalan marigayin za su ci gaba da rayuwa a jihar, tare da ƙarfafa zumunci tsakanin gwamnatin jihar.

Dubban mutane na ci gaba da miƙa ta’aziyyarsu kan rasuwar tsohon shugaban wanda ya mulki Najeriya sau biyu.

 

Ga hotunan a ƙasa:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
  • Dakarun Yemen Zasu Kara Daukan Matakai Kan Jiragen Ruwan Da Ke Hulda Da Isra’ila
  • HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna
  • Sojojin HKI Sun Kutsa cikin Jirgin Ruwan “Hanzala” Dake Son Karya Killace Yankin Gaza
  •  An Kashe Sojojin HKI 3 A Yankin Khan-Yunus Na Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kiran Cewa; Ina Masu Fafatukar Kare Hakkin Dan Adam Suke A Bala’in Gaza?
  • Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Furuci Da Halakar Sojan Guda Da Ya Jikkata A Zirin Gaza