“Rashin samar da daidaito a hada-ahadar kasuwanci, ya kasance abinda ya sanya Hukumar ta NPA ke cazar kudaden gudanar da aiki da yawa,” Inji Dantsoho.

 

Dantsoho wanda Janar Manaja na sashen hudda da jama’a da gudanar da tsare-tsare na Hukumar NPA Miista Seyi Iyawe Akinyemi ya wakilce shi a wajen taron, ya ce, NPA ta bai wa kamfanini biyar Lasisi a jihar Legas, bisa kokarin da take yi, na bunkasa fitar da kaya zuwa waje ta hanyar amfani da Tashoshin ta.

 

Sai dai, ya sanar da cewa, Hukumar na duba yuwuwar samar da rangwamen cazar kudaden, musamman domin ta kara inganta ayyukanta.

 

Ya yi nuni da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa waje ne da ke taimaka wa wajen kara habaka tattalin arzikin kasa, musamman saboda shigowar kasuwanci cikin kasar.

 

Dantsoho ya kara da cewa, yin ragin, zai bayar da dama wajen kara karfafa gasa a kasashen da ke Afiraka.

 

Shi ma a na sa sakon a wajen taron Babban Sakatare kuma Shugaban Majalisar Masu Fiton Kaya zuwa Ketare NSC, Dakta Akutah Pius Ukeyima, ya sanar da cewa, tabbatar da inganci a Tashar Jiragen Ruwa, abu da ya wuce, batun jigar kaya a Tashar, amma ana da bukatar komi ya tafi yadda ya kamata.

 

Ukeyima, ya bayyana haka ne, ta bakin Madam Margaret Ogbonna, Daraktar Sashen Kula da Ayyuka a NSC, ya kara da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, na fuslantar cazar kudade da yawa a yankin Afirka, musamman duba da yadda cazar kudaden, suka kai daga kashi 30 zuwa 40, wanda ya dara na Afirka ta Yamma.

 

A cewarsa, a yanzu, Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar nan, rashin inganci, wanda hakan ke ci gaba da shafar gudanar da hada-gadar kasuwanci.

 

Ya ci gaba da cewa, a yayin da Nijeriya ke ta kokarin tara sama da kashi 85 a cikin dari na fannin hada-hahadar kasuwancinta, musamman ta hanyar yin amfani da Tashoshin Jiragen Ruwanta, sai dai, cazar kudade da yawa a Tashohin Jiragen Ruwan Kasar, akalla a cikin kwana 18 zuwa 20, na ci gaba da zama kalubale, musamman duba da yadda cazar kudaden, daga kwana 3 uwa 5 suka dara na duniya.

 

“Wannan matsalar na janyo jinkiri da kuma shafar shiga da fitar da kaya.” Inji Ukeyima.

 

Ya bayyana cewa, domin a lalubo da mafita kan wannan matsalar, NSC ta mayar da hankali wajen ganin an wanzar da matakan da suka dace, musamman na bunkasa kundin farashi a Tashar Jiragen Ruwan Kasar.

 

Shi kuwa a na sa jawabin na maraba, Shugaban LCCI, Mista Gabriel Idahosa, ya alakanta Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasar, a matsayin fannin da ke kara bunakasa gasar gudanar da hada-hadar kasuwanci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa.

 

“Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar sun kasance wata mahada ce ta gudanar da hada-hadar kasuwanci ta kasa da kasa, musamman duba da yadda ake fhigar da kaya da kuma fitar da su waje,” Inji Idahosa.

 

“Tabbabar da ingancin gudanar da ayyuka a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, ta hanyar rage cazar kudade masu yawa, tabbatar da ana tura kaya kan lokaci, karfafa gasar hada-hadar kasuwanci, na kara taimakawa Tashoshin,” A cewar Idahosa.

 

Ya kara da cewa, amma rashin tabbatar da ingancin, kara yawan cazar kudade, na rage yawan adadin hada-hadar kasuwancin da ake bukatar gudanar wa, wanda kuma hakan, ke janyo tattalin azriki nakasau.

 

A cewarsa, Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar nan, sun jima suna fuskanatar matsaloli, wanda hakan ya janyo rashin samar da inganci da kuma bayar da gudunmawarsu, kan habaka tattalin arzikin kasar.

 

“Daya daga cikin manyan kalubalen da Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar ke fuskanta sun hada da samun cunkoso a Tashoshin da kuma samun jinkiri, musamman a Tashar Apapa da ta Tin Can Island da ke a jihar Legos, “ Inji Idahosa.

 

“Kayan aikin a Tashoshin, an jima ana yin amfani da su, wanda hakan ke haira da samun jinkirin gudanar da aiki, cazar kudade da yawa na tura kaya, wanda hakan ke sanya ba a samun damar gudanar da gasar hada-hadar kasuwanci, kamar yadda ta dace,” A cewar Idahosa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar A Tashoshin Jiragen Ruwa hada hadar kasuwanci cazar kudade da yawa a Tashoshin Jiragen cazar kudaden wanda hakan

এছাড়াও পড়ুন:

Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI

Shugabgan kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan wanda ya gana da fira ministan kasar Iraqi Muahmad Shi’a Sudani a taron Doha na kasashen musulmi ya bayyana cewa; Wajibi ne kasashen musulmi su hada kai idan har suna son kawo karshen laifukan da HKI take tafkawa.

Bugu da kari, shugaban kasar ta Iran ya kuma tattaunwa wasu hanyoyin da ya kamata a yi aiki da su, matukar ana son kawo karshen ta’addancin ‘yan sahayoniya.

Shugaba Fizishkiyan ya kuma ce, laifukan da HKI take tafkawa akan fararen hula a Gaza, da kashe yara da mata ta hanyar yunwa, wani lamari ne da hankali bai iya daukarsa, kuma idan musulmi su ka hada hannu da karfe wuri daya za su kawo karshensa.

A nashi gefen Fira ministan kasar Iraki ya bayyana abinda HKI take yi da cewa, isgili ne da dokokin kasa da kasa,don haka nauyi ne da ya doru a wuyan kasashen musulmi da su yi aiki domin ganin dukar matakan da suka dace.

Haka nan kuma ya ce, taron na birnin Doha dama ce ta daukar irin wadannan matakan.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa