“Rashin samar da daidaito a hada-ahadar kasuwanci, ya kasance abinda ya sanya Hukumar ta NPA ke cazar kudaden gudanar da aiki da yawa,” Inji Dantsoho.

 

Dantsoho wanda Janar Manaja na sashen hudda da jama’a da gudanar da tsare-tsare na Hukumar NPA Miista Seyi Iyawe Akinyemi ya wakilce shi a wajen taron, ya ce, NPA ta bai wa kamfanini biyar Lasisi a jihar Legas, bisa kokarin da take yi, na bunkasa fitar da kaya zuwa waje ta hanyar amfani da Tashoshin ta.

 

Sai dai, ya sanar da cewa, Hukumar na duba yuwuwar samar da rangwamen cazar kudaden, musamman domin ta kara inganta ayyukanta.

 

Ya yi nuni da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa waje ne da ke taimaka wa wajen kara habaka tattalin arzikin kasa, musamman saboda shigowar kasuwanci cikin kasar.

 

Dantsoho ya kara da cewa, yin ragin, zai bayar da dama wajen kara karfafa gasa a kasashen da ke Afiraka.

 

Shi ma a na sa sakon a wajen taron Babban Sakatare kuma Shugaban Majalisar Masu Fiton Kaya zuwa Ketare NSC, Dakta Akutah Pius Ukeyima, ya sanar da cewa, tabbatar da inganci a Tashar Jiragen Ruwa, abu da ya wuce, batun jigar kaya a Tashar, amma ana da bukatar komi ya tafi yadda ya kamata.

 

Ukeyima, ya bayyana haka ne, ta bakin Madam Margaret Ogbonna, Daraktar Sashen Kula da Ayyuka a NSC, ya kara da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, na fuslantar cazar kudade da yawa a yankin Afirka, musamman duba da yadda cazar kudaden, suka kai daga kashi 30 zuwa 40, wanda ya dara na Afirka ta Yamma.

 

A cewarsa, a yanzu, Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar nan, rashin inganci, wanda hakan ke ci gaba da shafar gudanar da hada-gadar kasuwanci.

 

Ya ci gaba da cewa, a yayin da Nijeriya ke ta kokarin tara sama da kashi 85 a cikin dari na fannin hada-hahadar kasuwancinta, musamman ta hanyar yin amfani da Tashoshin Jiragen Ruwanta, sai dai, cazar kudade da yawa a Tashohin Jiragen Ruwan Kasar, akalla a cikin kwana 18 zuwa 20, na ci gaba da zama kalubale, musamman duba da yadda cazar kudaden, daga kwana 3 uwa 5 suka dara na duniya.

 

“Wannan matsalar na janyo jinkiri da kuma shafar shiga da fitar da kaya.” Inji Ukeyima.

 

Ya bayyana cewa, domin a lalubo da mafita kan wannan matsalar, NSC ta mayar da hankali wajen ganin an wanzar da matakan da suka dace, musamman na bunkasa kundin farashi a Tashar Jiragen Ruwan Kasar.

 

Shi kuwa a na sa jawabin na maraba, Shugaban LCCI, Mista Gabriel Idahosa, ya alakanta Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasar, a matsayin fannin da ke kara bunakasa gasar gudanar da hada-hadar kasuwanci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa.

 

“Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar sun kasance wata mahada ce ta gudanar da hada-hadar kasuwanci ta kasa da kasa, musamman duba da yadda ake fhigar da kaya da kuma fitar da su waje,” Inji Idahosa.

 

“Tabbabar da ingancin gudanar da ayyuka a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, ta hanyar rage cazar kudade masu yawa, tabbatar da ana tura kaya kan lokaci, karfafa gasar hada-hadar kasuwanci, na kara taimakawa Tashoshin,” A cewar Idahosa.

 

Ya kara da cewa, amma rashin tabbatar da ingancin, kara yawan cazar kudade, na rage yawan adadin hada-hadar kasuwancin da ake bukatar gudanar wa, wanda kuma hakan, ke janyo tattalin azriki nakasau.

 

A cewarsa, Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar nan, sun jima suna fuskanatar matsaloli, wanda hakan ya janyo rashin samar da inganci da kuma bayar da gudunmawarsu, kan habaka tattalin arzikin kasar.

 

“Daya daga cikin manyan kalubalen da Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar ke fuskanta sun hada da samun cunkoso a Tashoshin da kuma samun jinkiri, musamman a Tashar Apapa da ta Tin Can Island da ke a jihar Legos, “ Inji Idahosa.

 

“Kayan aikin a Tashoshin, an jima ana yin amfani da su, wanda hakan ke haira da samun jinkirin gudanar da aiki, cazar kudade da yawa na tura kaya, wanda hakan ke sanya ba a samun damar gudanar da gasar hada-hadar kasuwanci, kamar yadda ta dace,” A cewar Idahosa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar A Tashoshin Jiragen Ruwa hada hadar kasuwanci cazar kudade da yawa a Tashoshin Jiragen cazar kudaden wanda hakan

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin PDP na yanzu za su rusa mana jam’iyya — Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya , Nyesom Wike, ya yi gargadin cewa irin yadda gwamnonin jam’iyyar PDP ke tafiyar da al’amuranta a yanzu, zai iya sanadin rushewar jam’iyyar.

Wike, ya bayyana haka ne a lokacin da yake hira da ’yan jarida a Abuja ranar Juma’a, inda ya zargi gwamnonin PDP da gaza magance rikicin jam’iyyar yadda ya kamata.

An kama Sakataren APC na mazaba a Yobe kan zargin aikata kisan kai
Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027

Rahotanni sun nuna cewa akwai rashin jituwa tsakanin Wike da gwamnonin PDP.

Jam’iyyar na shirin gudanar da babban taronta na kasa a watan Nuwamba a birnin Ibadanna  Jihar Oyo, amma wasu rahotanni na cewar magoya bayan Wike na ƙoƙarin hana gudanar da taron.

A kwanakin baya, Sakataren Jam’iyyar na Kasa, Samuel Anyanwu, ya zargi Kwamitin Gudanarwa na Jam’iyyar naKasa (NWC) da yin amfani da sa hannunsa na bogi wajen aike wa INEc wasiƙa don sanar da shirin gudanar da taron.

Sai dai wasu shugabannin jam’iyyar sun ce Anyanwu yana aiki ne bisa umarnin Wike.

A yayin tattaunawar da ya yi da ’yan jarida, Wike ya ce: “Ban faɗa tun farko cewa tarkon da kuke saka wa kanku zai kama ku ba? Na faɗa tun da wuri, irin yadda waɗannan gwamnonin ke tafiyar da jam’iyyar, za su kashe ta ne.

“Kuna gudanar da taron jam’iyya, kuna kiran mutane manyan jam’iyya, amma kun bar ni saboda ba gwamna ba ne, ta yaya za ku ci gaba a haka?”

Wike ya kuma nesanta kansa daga masu goyon bayan tsohon Ministan Harkoki na Musamman, Tanimu Turaki, a matsayin sabon shugaban jam’iyyar.

“Ban san wani abu game da Tanimu Turaki kan zama shugaban jam’iyya ba. Wataƙila zai zama shugaban wani bangare daban ne, ba PDP dana sani ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa tun da farko ya yi hasashen wasu ’ya’yan jam’iyyar za su fice daga cikinta.

“Tun farko na faɗa cewa idan abubuwa suka ci gaba da tafiya a haka, PDP za ta rika yin asara. Ana tafiyar da abubuwa bisa kuskure, kuma yanzu kowa yana gani. Abin kunya ne,” in ji shi.

“Duk abin da na faɗa a da yanzu yana faruwa,” a cewar Wike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya
  • Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
  • An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing
  • Yau Ne Ake Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa  A Ivory Coast
  • Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD
  • Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa
  • Ƙungiya ta tallafa wa ɗaliban makarantar masu buƙata ta musamman a Gombe
  • Gwamnonin PDP na yanzu za su rusa mana jam’iyya — Wike
  • An kama Sakataren APC na mazaba a Yobe kan zargin aikata kisan kai
  • A Shirye Nake Na Kare Nasarar Da Na Samu A Zabe – Tchiroma Bakary