Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Published: 26th, April 2025 GMT
“Rashin samar da daidaito a hada-ahadar kasuwanci, ya kasance abinda ya sanya Hukumar ta NPA ke cazar kudaden gudanar da aiki da yawa,” Inji Dantsoho.
Dantsoho wanda Janar Manaja na sashen hudda da jama’a da gudanar da tsare-tsare na Hukumar NPA Miista Seyi Iyawe Akinyemi ya wakilce shi a wajen taron, ya ce, NPA ta bai wa kamfanini biyar Lasisi a jihar Legas, bisa kokarin da take yi, na bunkasa fitar da kaya zuwa waje ta hanyar amfani da Tashoshin ta.
Sai dai, ya sanar da cewa, Hukumar na duba yuwuwar samar da rangwamen cazar kudaden, musamman domin ta kara inganta ayyukanta.
Ya yi nuni da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa waje ne da ke taimaka wa wajen kara habaka tattalin arzikin kasa, musamman saboda shigowar kasuwanci cikin kasar.
Dantsoho ya kara da cewa, yin ragin, zai bayar da dama wajen kara karfafa gasa a kasashen da ke Afiraka.
Shi ma a na sa sakon a wajen taron Babban Sakatare kuma Shugaban Majalisar Masu Fiton Kaya zuwa Ketare NSC, Dakta Akutah Pius Ukeyima, ya sanar da cewa, tabbatar da inganci a Tashar Jiragen Ruwa, abu da ya wuce, batun jigar kaya a Tashar, amma ana da bukatar komi ya tafi yadda ya kamata.
Ukeyima, ya bayyana haka ne, ta bakin Madam Margaret Ogbonna, Daraktar Sashen Kula da Ayyuka a NSC, ya kara da cewa, Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, na fuslantar cazar kudade da yawa a yankin Afirka, musamman duba da yadda cazar kudaden, suka kai daga kashi 30 zuwa 40, wanda ya dara na Afirka ta Yamma.
A cewarsa, a yanzu, Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar nan, rashin inganci, wanda hakan ke ci gaba da shafar gudanar da hada-gadar kasuwanci.
Ya ci gaba da cewa, a yayin da Nijeriya ke ta kokarin tara sama da kashi 85 a cikin dari na fannin hada-hahadar kasuwancinta, musamman ta hanyar yin amfani da Tashoshin Jiragen Ruwanta, sai dai, cazar kudade da yawa a Tashohin Jiragen Ruwan Kasar, akalla a cikin kwana 18 zuwa 20, na ci gaba da zama kalubale, musamman duba da yadda cazar kudaden, daga kwana 3 uwa 5 suka dara na duniya.
“Wannan matsalar na janyo jinkiri da kuma shafar shiga da fitar da kaya.” Inji Ukeyima.
Ya bayyana cewa, domin a lalubo da mafita kan wannan matsalar, NSC ta mayar da hankali wajen ganin an wanzar da matakan da suka dace, musamman na bunkasa kundin farashi a Tashar Jiragen Ruwan Kasar.
Shi kuwa a na sa jawabin na maraba, Shugaban LCCI, Mista Gabriel Idahosa, ya alakanta Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasar, a matsayin fannin da ke kara bunakasa gasar gudanar da hada-hadar kasuwanci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasa.
“Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar sun kasance wata mahada ce ta gudanar da hada-hadar kasuwanci ta kasa da kasa, musamman duba da yadda ake fhigar da kaya da kuma fitar da su waje,” Inji Idahosa.
“Tabbabar da ingancin gudanar da ayyuka a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, ta hanyar rage cazar kudade masu yawa, tabbatar da ana tura kaya kan lokaci, karfafa gasar hada-hadar kasuwanci, na kara taimakawa Tashoshin,” A cewar Idahosa.
Ya kara da cewa, amma rashin tabbatar da ingancin, kara yawan cazar kudade, na rage yawan adadin hada-hadar kasuwancin da ake bukatar gudanar wa, wanda kuma hakan, ke janyo tattalin azriki nakasau.
A cewarsa, Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar nan, sun jima suna fuskanatar matsaloli, wanda hakan ya janyo rashin samar da inganci da kuma bayar da gudunmawarsu, kan habaka tattalin arzikin kasar.
“Daya daga cikin manyan kalubalen da Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar ke fuskanta sun hada da samun cunkoso a Tashoshin da kuma samun jinkiri, musamman a Tashar Apapa da ta Tin Can Island da ke a jihar Legos, “ Inji Idahosa.
“Kayan aikin a Tashoshin, an jima ana yin amfani da su, wanda hakan ke haira da samun jinkirin gudanar da aiki, cazar kudade da yawa na tura kaya, wanda hakan ke sanya ba a samun damar gudanar da gasar hada-hadar kasuwanci, kamar yadda ta dace,” A cewar Idahosa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar A Tashoshin Jiragen Ruwa hada hadar kasuwanci cazar kudade da yawa a Tashoshin Jiragen cazar kudaden wanda hakan
এছাড়াও পড়ুন:
An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia, Mohammed Haliru Arabo, na tsawon wata uku, kan rikicin shugabanci.
Shugaban Majalisar, Danladi Jatau, ne ya sanar da hakan a ranar Talata a Lafia, bayan Shugaban Kwamitin Majalisar kan Harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu, Musa Ibrahim Abubakar, ya gabatar da korafi kan rikicin mulki da ke faruwa a karamar hukumar.
Jatau ya ce matakin ya zama dole domin ba da damar gudanar da bincike kan yadda ake tafiyar da mulkin karamar hukumar, wanda ya ce yana shafar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
Ya bayyana cewa dakatarwar ta yi daidai da sashe na 7 da na 128 na kundin tsarin mulkin 1999 da aka yi wa kwaskwarima, wanda ya ba majalisa ikon sanya ido kan harkokin mulki.
Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a SakkwatoA cewarsa: “Domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Lafia, dole ne mu gudanar da bincike kan abin da ke faruwa. Bisa ikon da kundin tsarin mulki ya ba mu, shugaban karamar hukumar Lafia ya dakata na tsawon wata uku. Za a ci gaba da gudanar da harkokin karamar hukumar har sai an kammala bincike.”
Kwamitin harkokin kananan hukumomi da masarautu ya samu umarni da ya gudanar da binciken cikin wannan lokaci. A yayin dakatarwar, mataimakin shugaban karamar hukumar, Uba Arikya, zai rike ragamar mulki.
Tun da farko, Musa Ibrahim Abubakar ya gabatar da kudiri a matsayin gaggawa, inda ya nuna damuwa kan yadda aka dakatar da shugaban karamar hukumar na tsawon wata shida ba tare da bin ka’ida ba. Ya ce hakan ya saba wa kundin tsarin mulki, kuma yana haifar da rashin tabbas a siyasar yankin.
Ya jaddada bukatar majalisar jihar ta shiga tsakani domin tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin kudi da mulkin karamar hukumar.
Kwamitin ya kuma bukaci majalisar ta yi nazari sosai kan lamarin domin kawo karshen rashin tabbas da rikicin da ya kunno kai a Lafia.