Ministan ya ce sabon gidan yanar na intanet zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da suka daɗe suna dagula harkokin sayayya a gwamnati, kamar yadda ake fama da rashin ingantattun tsare-tsare, ƙarancin ƙwararru da rashin tsarin horaswa na dindindin.

 

Ya ce: “Ƙaddamar da wannan sabon shafin ba kawai cigaba ba ne a fannin fasaha; wata babbar hanya ce ta sauya fasalin aiki gaba ɗaya wadda ke magance manyan ƙalubale a tsarin sayen kaya na gwamnati, irin su cikas da ke yawan faruwa, rashin ingantattun hanyoyin sayayya, ƙarancin ma’aikatan da suka dace, da kuma rashin ingantaccen tsarin gina ƙwarewa.

 

“Waɗannan matsaloli sun daɗe suna hana a yi amfani da dukiyoyin gwamnati yadda ya kamata tare da kawo cikas ga cigaban tattalin arziki gaba ɗaya a ƙasar nan.”

 

Ya ce wannan sabon tsari zai bai wa jami’an sayayya damar samun horo, takardun shaida, da kuma damar yin aiki da ƙwarewa, daidai da matakin duniya.

 

Idris ya ce: “Za a tabbatar da cewa mu jami’an gwamnati muna sayen kaya ba kawai bisa doka ba, har ma ƙwararru ne kuma masu iya gogayya a matakin duniya.”

 

Idris ya yaba wa Darakta-Janar na BPP, Dakta Adebowale Adedokun, bisa jajircewa da hangen nesan sa wajen inganta tsarin sayayya a Nijeriya.

 

Ya ce wannan gidan yana hujja ce ta jajircewar sa wajen ganin an sabunta tsarin sayayya a ƙasar nan.

 

Ministan ya kuma buƙaci ‘yan ƙasa da su fahimci cewa sabon gidan yanar ba kawai don gwamnati ba ne, har ma wata hanya ce da za su iya amfani da ita wajen neman ingantattun ayyuka da gaskiya.

 

“Don haka ina kira ga dukkan hukumomi da jami’an gwamnati da su rungumi wannan shiri gaba ɗaya, kuma ina kira ga kafafen yaɗa labarai, musamman, da su taimaka wajen yaɗa amfanin sa da kuma sa ido kan yadda ake aiwatar da shi,” inji shi.

 

Cikin waɗanda suka halarci taron akwai Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, Misis Didi Esther Walson-Jack; Ministan Kuɗi kuma Ministan Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Mista Wale Edun; Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa; Ministar Harkokin Mata, Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim; Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa (rtd); da Darakta-Janar na FRCN da NTA, Dakta Mohammed Bulama da Kwamared Abdulhamid Dembos.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Gwamnan Jihar Neja, Umar Mohammed Bago, ya janyo ce-ce-ku-ce a fadin Najeriya bayan da ya sake jaddada cewa duk wani malamin addini da ke shirin yin wa’azi dole ne ya gabatar da rubutaccen wa’azinsa domin tantancewa kafin ya gabatar da shi ga jama’a.

A cewar gwamnatin jihar, wannan mataki na da nufin daƙile kalaman ƙiyayya, tsattsauran ra’ayi da barazanar tsaro da ke tasowa daga wa’azin da ba a tantance ba.

Da yake jawabi a shirin Politics on Sunday na gidan talabijin na TVC, Gwamna Bago ya musanta zargin cewa dokar ta hana wa’azi gaba ɗaya, yana mai cewa matakin na da nufin tabbatar da zaman lafiya da hana tayar da fitina.

Gwamnan ya ce:

“Ban hana wa’azi ba. Duk wanda zai yi wa’azi a ranar Juma’a, ya kawo rubutaccen wa’azinsa domin tantancewa. Wannan ba sabon abu ba ne. A Saudiyya ma haka ake yi. Ba za a bar malami ya yi wa’azi da ke cin mutuncin jama’a ko gwamnati ba, yana mai cewa ba da damar yin wa’azi ba yana nufin a yi amfani da damar wajen tayar da hankali.”

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnati na aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro kamar DSS, ’yan Sanda, Sibil Difens da sojoji domin sa ido kan wa’azin da ka iya tayar da hankali.

Matakin ya fara jawo ce-ce-ku-ce ne bayan da Darakta Janar na Hukumar Kula da Harkokin Addini ta Jihar Neja, Umar Farooq, ya sanar da cewa duk wani malami dole ne ya nemi lasisin wa’azi cikin watanni biyu ko ya fuskanci hukunci.

“Abin da ake bukata shi ne su zo ofishinmu, su cike fom, sannan su fuskanci kwamitin tantancewa kafin su fara wa’azi,” in ji Farooq.

Wannan sanarwa ta haifar da martani iri-iri daga shugabannin addini da ƙungiyoyin fararen hula, inda da dama ke nuna fargabar cewa dokar za ta iya zama hanyar danne ’yancin faɗin albarkacin baki.

Babban Limamin Jami’ar Fasaha ta Minna, Sheikh Bashir Yankuzo, ya bayyana ra’ayi mai sassauci, yana mai cewa duk da cewa gwamnati na da haƙƙin daƙile kalaman ƙiyayya, ba za ta hana wa’azi na gaskiya ba.

Sheikh Yankuzo ya ce:

“Wa’azi umarni ne daga Allah, kuma gwamnati ba ta biya kowa albashi don yin wa’azi. Amma idan akwai masu tayar da hankali ko amfani da kalaman batanci, to gwamnati na da ikon dakile hakan don tabbatar da zaman lafiya.”

Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Jihar Neja ta bakin Sakataren ta, Raphael Opawoye, ta ce ba a sanar da su hukuncin ba.

“CAN ba ta da masaniya kan dokar. Za mu fitar da sanarwa idan an sanar da mu a hukumance,” in ji Opawoye.

Sai dai wani malamin addinin Musulunci, Ustaz Uthman Siraja, ya soki dokar kwata-kwata, yana mai cewa ta take ‘yancin addini da ibada.

Ya bayyana cewa:

“Hana wa’azi cin zarafin ’yancin addini ne. Mafi alheri shi ne gwamnati ta gayyato malamin da ya tayar da hankali ta hukunta shi, ba wai a tantance wa’azi gaba ɗaya ba.”

Gwamna Bago ya kare dokar da cewa matakin tsaro ne na rigakafi, musamman ganin tarihin jihar na fuskantar hare-haren ’yan bindiga, rikicin addini da tsattsauran ra’ayi.

Yayin da wa’adin cike fom da samun lasisi ke ƙara matsowa, idanu sun karkata zuwa Jihar Neja don ganin ko dokar za ta kawo zaman lafiya ko kuma ta ƙara dagula al’amura tsakanin gwamnati da al’ummar addini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha