An saki Falasɗinawa 200 da ke ɗaure a Isra’ila
Published: 26th, January 2025 GMT
Isra’ila ta sako Falasɗinawa 200 daga cikin waɗanda take riƙe da su a kurkuku kamar yadda yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninta da ƙungiyar Hamas ta tanada.
Wannan dai na zuwa ne bayan da Hamas ta saki rukuni na biyu na ’yan Isra’ilar da ta yi garkuwa da su — wasu sojojin Isra’ila mata da Hamas take riƙe da su tsawon watanni.
A wata sanarwa da hukumomin gidan yari na Isra’ila suka fitar sun ce: “Bayan kammala dukkanin abubuwan da suka wajaba a gidajen yarin da kuma amincewar hukumomi an saki dukkanin ’yan ta’addan daga gidajen yari na Ofer da Ktziot,” kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na AFP da na Reuters suka ce.
Sai dai sabanin Falasɗinawan da aka saki a makon da ya gabata waɗanda yawanci hukuncinsu na zaman gidan yari kaɗan ne, a wannan karon, 121 daga cikin fursunonin suna kan hukuncin rai da rai ne — wasu bisa laifin kisan kai fiye da sau daya da ya hada da kisan farar hula ’yan Isra’ila.
Shekarun Falasɗinawa fursunonin sun bambanta sosai, inda mafi ƙanƙanta da aka saki shi ne mai shekara 16, yayin da mai shekara 69 ya kasance mafi girma a cikinsu.
Ɗaya daga cikin fursunonin ya shafe shekara 39 a gidan kurkukun Isra’ila, bayan da aka kama shi da farko a 1986.
Waɗanda aka yanke wa hukuncin manyan laifuka mafiya tsanani ba sa cikin waɗanda aka saki yau.
Kusan 70 daga cikinsu za a fitar da su daga Isra’ila ne inda za a bi da su ta Masar zuwa ƙasashe makwabta da suka haɗa da Qatar da Turkiyya, kafin a kai su Falasɗinu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari
Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta yanke wa wani shugaban ISWAP Hussaini Ismaila, hukuncin ɗaurin shekaru 20 a gidan yari bayan samun sa da aikata laifukan ta’addanci.
Alƙalin kotun, Mai Shari’a Emeka Nwite, ya yanke hukuncin ne bayan Ismaila, wanda ake kira Mai Tangaran, ya amsa tuhume-tuhume guda huɗu da Hukumar DSS ta gabatar a kansa.
Gwamna Abba ya gabatar da N1.36trn a matsayin kasafin 2026 Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda matsalar tsaro a NajeriyaDSS ta ce Ismaila ne, ya jagoranci kai wasu hare-haren ta’addanci a Kano a shekarar 2012.
Hare-haren sun haɗa da harin Hedikwatar ’Yan Sanda ta Bompai, Barikin ’Yan Sandan Mopol a titin Kabuga, ofishin ’yan sanda na Farm Centre, ofishin ’yan sanda na Unguwa Uku, da wasu wurare.
Mutane da dama sun jikkata a yayin kai waɗannan hare-hare.
An kama Ismaila ne a ranar 31 ga watan Agustan 2017, a ƙauyen Tsamiyya Babba da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa, a Jihar Kano.
Daga nan aka gurfanar da shi a gaban kotu bisa dokar hana aikata ta’addanci ta 2013.
Shari’ar ta ɗauki lokaci saboda ɗaukaka ƙara da kuma tabbatar da bayanan da ya bayar da farko ba tursasa shi aka yi ba.
A ƙarshe, lauyoyin gwamnati sun kira shaidu biyar, ciki har da jami’an DSS da mutanen da harin ya shafa.
Da farko Ismaila, ya ƙi amincewa da laifin da ake tuhumarsa amma bayan gabatar da shaida na biyar, ya sauya maganarsa ya amsa laifin.
Lauyansa daga Hukumar LAC, P. B. Onijah, ya roƙi kotu ta yi masa sassauci, inda bayyana cewa Ismaila ya nuna nadama kuma bai son ɓata wa kotu lokaci.
A hukuncin da ya yanke, Mai Shari’a Nwite ya yanke masa shekar 15 kan tuhumar farko da kuma shekaru 20 kan sauran kowace tuhuma uku.
Dukkanin hukuncin za su tafi a lokaci guda, kuma za su fara aiki tun daga ranar da aka kama shi a shekarar 2017.
Alƙalin ya umarci Hukumar Gyaran Hali ta tsare shi a gidan yari da Babban Kwamandan Hukumar ya zaɓa.
Bayan ya kammala zaman gidan yari, dole a yi masa horon gyaran hali da kawar da ra’ayin ƙiyayya kafin a sake mayar da shi cikin al’umma.