Leadership News Hausa:
2025-07-31@12:28:07 GMT

Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?

Published: 29th, April 2025 GMT

Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?

Wannan ya sa wasan yau zai zama mai ɗaukar hankali, domin kowanne daga cikinsu na burin ɗaukar kofin a karo na farko, domin a dakatar da yawan dariyar da ‘yan adawa ke musu.

A zagayen rukuni da suka haɗu a farkon wannan kakar, Arsenal ta lallasa PSG da ci 2-0.

Kocin Arsenal yanzu, Mikel Arteta, ya taɓa buga wasa a duka ƙungiyoyin.

Yana fatan ya zama kocin farko da zai jagoranci Arsenal ta lashe kofin Zakarun Turai.

Wannan ya sa magoya bayan Arsenal ke fatan ganin ƙungiyarsu ta yi abin mamaki a wasan da za a fara da misalin ƙarfe 8 na dare agogon Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arsenal Gasar Zakarun Turai

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba

 

Ministan Ƙasa na Ci Gaban Yankuna, Uba Maigari Ahmadu, ya yaba wa ci gaba da tattaunawa tsakanin jami’an gwamnati da shugabannin arewa yana mai cewa wannan “tattaunawa ce mai tarihi kuma cike da ƙarfi,” yana nuna cewa hangen nesa na Shugaba Bola Tinubu ga Arewa ya fara samo asali kuma yana haifar da sakamako.

 

Yayin jawabi a taron gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello a rana ta biyu na zaman tattaunawa tsakanin gwamnati da alumma, ministan ya jaddada cewa wannan zama shi ne karo na farko a tarihin mulkin Najeriya inda ministoci, daraktocin hukumomi, shugabannin kwamitoci, da sauran manyan jami’an gwamnati daga Arewa suka “mika kansu don a yi musu tambayoyi” daga mutanen da suke yi wa hidima.

 

Ya ce gwamnati na da rubutattun nasarori da ake iya gani, yana bayyana wannan mataki a matsayin sabon hanya don samun amincewar jama’a, “wadanda su ne a ƙarshe suka fi rinjaye wajen zabe.”

 

Tattaunawar ta shafi fannoni da dama – tsaro na abinci, noma, ilimi, lafiya da ci gaban ababen more rayuwa – inda mahalarta suka amince cewa wadannan matsaloli suna da alaƙa sosai kuma suna bukatar kulawa cikin gaggawa.

 

Ministan ya bayyana wannan zama a matsayin “tattaunawar fannoni daban-daban don makomar Arewa,” yana mai cewa burin shi ne samar da tsare-tsare masu amfani ga birane da karkara.

 

Lokacin da aka tambaye shi yadda “hanyar gaba” za ta kasance, Ahmadu ya ce manufar gwamnati ba kawai yin magana ba ce, amma ta saurara, ta yi rubutu, kuma ta yi aiki.

 

Ya kara da cewa gwamnati na mai da hankali sosai kan batun sarƙoƙin samar da abinci, farfaɗo da noma da kare ‘yancin al’ummomin makiyaya.

 

A matsayin abin da ya kira “juyin hali,” Ahmadu ya tabbatar cewa gwamnati ta amince da karin kasafin kuɗi don shirye-shiryen ci gaban Arewa – abin da ya nuna gwamnati ba kawai alkawari take yi ba, har ma tana saka kuɗi a bayansa.

 

Sai dai ministan bai boye kalubalen da ke akwai ba, ciki har da matsin tattalin arziki, rikicin al’adu da harsuna, da ƙarin matsa lamba kan ƙasar noma saboda sauyin yanayi da yawaitar jama’a.

 

Ahmadu ya jaddada cewa wannan lokaci “sabuwar farawa” ce ga Arewa, wadda ke buƙatar haɗin kai tsakanin shugabanni, al’umma da hukumomin gwamnati.

 

Taron zai ci gaba na wasu kwanaki, inda za a gabatar da ƙarin rahotanni daga ma’aikatun gwamnati da hukumomi kamar North-East Development Commission don bayyana ci gaban ayyuka.

 

“Wannan abu ne game da gaskiya, amana, da sabuwar farawa ga Arewa,” in ji Ahmadu, yana tabbatar da cewa tattaunawar da ake yi yanzu za ta tsara makomar yankin.

 

COV: Khadija Kubau

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano