Za a raba tallafin karatu ga Dalibai 100 a Mazabar Chikun da Kajuru
Published: 26th, January 2025 GMT
Dan takarar zaben maye gurbin Dan Majalisar Tarayya da ke wakiltar Mazabar Chikum da Kajuru a jam’iyar APC Arc Sani A Abbas Sardaunan Chikum ya nada kwamitin mutane 7 domin raba tallafin karatu ga daliban yankin sa su 100 da suke karatun kimiyya da fasaha a manyan marantun Gwamnati.
Wannan wata manuniya ce game da kudurin Arc Sani Abbas na karfafa matasa ta bangaren ilimin don gobe su tayi kyau.
Babban aikin wannan kwamitin shi ne tantance daliban da suka cancanci amfana da wannan tallafin musamman wadanda babu ke barazanar hana su karatu. Wanda yin haka zai taimaka wajen tallafa musu su nemi ilimi don cike gibin da ake samu ta wannan bangaren.
Wannan tallafin kadan ne daga cikin irin manofofin da yake da su ba ga al’ummar sa ba, yana nuna cewa yana son ganin an sami al’umma mai ilimi.
‘Yan kwamitin sun hada da Hon. Dauda Abdulkadir Kujama a matsayin shugaba Sai wakilan kwamitin da suka hada da Hon Ibrahim Garba Danmajen Chikun da Hon. Ibrahim Umar.
Sauran su ne Mrs. Rebecca Akapson da Hon. Daniel Sisin Kobo
Saifu Adamu Bawa Kajuru sai Hon. Ganaka James Kogi da aka ba sakataren kwamitin.
Wanda ke bukatar samun wannan tallafi sai ya sauke wannan takarda ya cika ya kawo.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Riza’i: Babu Hannun Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
Kakakin kwamitin tsaron kasa a majalisar shawarar musulunci ta Iran ya bayyana cewa; ” Ya zuwa yanzu ba za mu iya yin hukunci akan dalilan da su ka haddasa fashewar abubuwa a tashar ruwa ta Shahid Raja’i ba, amma za mu iya cewa babu hannu waje a ciki.
Kakakin kwamitin tsaron kasar ta Iran Ibrahim Rizai wanda ya halarci taron da aka yi a Majalisa akan fashewar da aka samu a tashar ruwan ta shahid Raja’i, ya kuma kara da cewa; Fahimtata da abinda na ji daga abokan aikina dangane da abinda ya faru a tashar ruwa ta Shahid Raja’i, da kuma rahotannin da su ka iso mana, shi ne cewa abinda ya farun ba shi da alaka da waje.”
A ranar Asabar da ta gabata ne dai wasu abubuwa su ka fashe a tashar ruwa ta Shahid Raja’i dake Bandar Abbas a kudancin Iran, wanda ya haddasa asarar rayuka da kuma jikkatar daruruwan mutane.
An bude kwamitin bincike domin gano hakikanin abinda ya faru a tashar da kuma haddas fashewar abubuwan masu karfi.