Aminiya:
2025-08-01@20:23:14 GMT

Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano

Published: 28th, April 2025 GMT

Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya naɗa babban ɗan uwansa, Alhaji Sanusi Ado Bayero, a matsayin Galadiman Kano, bayan rasuwar Abbas Sanusi.

A gefe guda kuma, Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, wanda ke ta ƙaddamar kan sarautar Kano da Aminu Ado Bayero a gaba kotu, ya naɗa Mannir Sanusi a matsayin Galadiman Kano.

Wannan lamari na nuni da cewa rikicin Sarautar Kano ya ɗauki sabon salo, inda kowanne daga cikin ɓangarori biyun ya naɗa nasa Galadiman Kano, inda masu riƙe da sarautun biyu za su gudanar da ayyukansu daban-daban.

A cikin wasiƙar da ke ɗauke da wannan sanarwar, wadda Alhaji Awaisu Abbas Sanusi, babban jami’in gudanarwa na Majalisar Masarautar Kano ya sanya hannu, naɗin Sanusi Ado Bayero ya biyo bayan taron majalisar da Sarki Aminu ya jagoranta a ranar Laraba, 16 ga Afrilu, 2025.

Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”

A baya an naɗa Sanusi a matsayin Chiroman Kano, dan Majalisar Masarautar Kano, kuma Hakimin Gwale a zamanin mahaifinsa Sarki Ado Bayero.

Bayan rasuwar mahaifin nasa a shekarar 2014, a matsayinsa na babban ɗa kuma magaji, an ɗauka cewa Sanusi Ado ne  wanda ya cancanci ya gaje shi, War wasu rahotanni na farko sun sanar da shi a matsayin Sarki.

Sai dai, a ranar 8 ga Yuni, 2014, aka naɗa ɗan ɗan uwansa, Sanusi Lamido Sanusi, a matsayin Sarkin Kano. A sakamakon haka, Sanusi Ado ya ƙi yin mubaya’a a gare shi kuma, don nuna rashin amincewa, kuma ya yanke shawarar barin Kano.

Bayan raba Masarautar Kano, da cire Sarki Sanusi II, da kuma naɗin ƙanensa, Aminu Ado Bayero, a matsayin Sarki na 15 a watan Yulin 2020, an mayar da Sanusi Ado Bayero kan matsyinsa a Majalisar Masarautar Kano kuma aka ba shi sarautar Wamban Kano.

Tarihin Sanusi Ado Bayero

Sanusi kammala digirinsana farko a fannin shari’a a shekarar 1983 kuma an rantsar da shi a matsayin lafiya a shekarar 1984.

Tsohon ma’aikacin Gwamnatin Jihar Kano ne inda ya yi aiki daga 1985 zuwa 2015, har ya kai matsayi mafi girma na Babban Sakataren.

Daga baya aka naɗa shi a matsayin Manajan Daraktan Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Najeriya, muƙamin da ya riƙe har zuwa lokacin da aka cire shi a watan Agustan 2015.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sanusi Ado Bayero Sanusi Bayero Sarkin Kano Sanusi Ado Bayero Masarautar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

Gwamna Zulum ya nuna jin dadinsa ga kwamishinonin biyu, tare da yi musu fatan alheri a cikin ayyukansu na gaba.

 

Sai dai ya sanar da nadin Engr. Mohammed Habib da Ibrahim Hala Hassan domin maye gurbin kwamishinonin biyu da aka sauke.

 

A halin da ake ciki, Gwamna Zulum ya kuma amince da nadin Farfesa Yusuf Gana Balami a matsayin Shugaban Hukumar Ilimin Sakandare ta Jihar Borno.

 

Balami, Farfesa a fannin ilimi, ya fito ne daga Hawul da ke kudancin jihar.

 

Zulum ya taya Balami murna tare da bukatar sa da ya yi amfani da shekarunsa na gogewa a fannin ilimi, a matsayin shugaba a bangaren gudanarwa da karantarwa wajen sake fasalin ilimin sakandare a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44