Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027
Published: 26th, April 2025 GMT
Ya kara da cewa kungiyar dattawan Arewa ba za ta lamunci cin zarafin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba.
Sai dai da take magana da LEADERSHIP, ACF ta bayyana cewa kungiyar ba za ta goyi bayan duk wani dan takarar shugaban kasa a bainar jama’a a zaben 2027 ba.
Da yake magana ta wayar tarho a ranar Lahadi, sakataren yada labarai na ACF na kasa, Farfesa T.
Mai magana da yawun ACF, duk da haka, kungiyar za ta bincika dukkan batutuwan tare da gabatar da su ga masu jefa kuri’a don su iya yin zabi mai kyau a 2027.
“Dakta Baba-Ahmed yana da ‘yancin bayyana ra’ayinsa. Bai dade da ya bar cikin gwamnati ba, kuma duk abin da ya ce hakkinsa ne. Kun san muna gab da zabukan 2027, kuma yawancin irin wadannan ra’ayoyin mutane da kungiyoyi za su bayyana a yayin da zabuka ke gabatowa. Muna sa ran ganin karin irin wannan sharhi. Ko yake, ACF ba kungiya ce ta siyasa ba. Ba ma nuna bangaranci.
“Yayin da zabe ke gabatowa, za mu iya nazarin batutuwa ne kawai mu gabatar da su ga masu jefa kuri’a don su yanke shawarar wanda za su zaba. Ba za mu bayyana goyon baya ga duk wani dan takarar jam’iyyar siyasa da zai tsaya takara a zaben shugaban kasa a 2027 ba. Za mu ci gaba da kasancewa a matsayin kungiyar kare muradun al’ummar Arewa,” in ji ACF.
A halin da ake ciki, wata kungiya mai suna ‘Arewa Think Tank’ (ATT), ta nuna goyon baya ga matsayin Gwamnan Jihar Nasarawa Abdullahi Sule cewa ya kamata Arewa ta yi aiki don sake zaben Bola Tinubu a 2027.
A kwanan nan ne Gwamna Sule ya bayyana cewa Arewa na bukatar hada kai don aiwatar da yunkurin Shugaba Tinubu ba.
A kan kashe-kashen da aka yi kwanan nan a jihohin Filato da Benuwai, Arewa Think Tank ta yi zargin cewa makiyan ‘yan siyasa suna yin duk mai yiwuwa, ciki har da shigar da kasashen waje, don kawo cikas ga gudanar da babban zabben 2027.
A cikin wata sanarwa da shugaban ATT, Muhammad Alhaji Yakubu ya fitar, ya ce kungiyar ta sha alwashin goyon bayan yin tazarcen Shugaba Tinubu, domin ya ci gaba da ayyukan da ya faro.
“Mun san cewa goyon bayan wa’adi na biyu na Shugaba Tinubu zai cika alkawarin da ya yi wa yankin Arewa tun gabanin babban zaben 2023.
“Mun amince kuma mun goyi bayan Gwamna Sule saboda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Arewa ta tsakiya, kuma mun san cewa ba a san Arewa da yin watsi da alkawuran da ta dauka ba.”
ATT ta bukaci shugabannin Arewa da su nesanta kansu daga wasu ‘yan siyasa da ke da niyyar rikitar da siyasar Nijeriya saboda sun kasa cimma burinsu.
Kungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta rufe kan iyakokin kasar nan tare da hana bakin haure shigowa Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya naɗa tsohon shugaban rundunar sojin ruwa kuma tsohon Kantoman jihar Ribas, Ibok-Ete Ekwe Ibas a matsayin Jakadan Najeriya.
Tinubu ya kuma naɗa Ita Enang, tsohon sanata da uwargidan tsohon gwamnan jihar Imo Chioma Ohakim da tsohon ministan cikin gida kuma tsohon shugaban rundunar sojin ƙasa Abdulrahman Dambazau, a matsayin jakadun.
’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwaSunayensu nasu na zuwa ne ’yan kwanaki bayan Tinubu ya aike wa Majalisar Dattijai jerin farko na waɗanda yake son nadawa a matsayin jakadun.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar sabbin naɗe-naɗen a gaban majalisar a yayin zamanta na ranar Alhamis.
A cikin wasikar, shugaban ƙasa ya roƙi ’yan majalisa da su yi gaggawar duba sunayen domin bai wa gwamnati damar cike muhimman guraben jakadun.
Akpabio ya mika jerin sunayen ga kwamitin majalisar dattawa kan harkokin ƙasashen waje, tare da umarnin cewa kwamitin ya kammala tantancewa ya kuma dawo da rahoto cikin mako guda.
Shugaban ƙasa a baya ya naɗa tsohon mai ba da shawara na fadar shugaban ƙasa Reno Omokri da tsohon ministan sufurin jiragen sama Femi Fani-Kayode da tsohon shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu a matsayin jakadu.