Leadership News Hausa:
2025-06-30@22:10:21 GMT

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

Published: 26th, April 2025 GMT

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

Ya kara da cewa kungiyar dattawan Arewa ba za ta lamunci cin zarafin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba.

 

Sai dai da take magana da LEADERSHIP, ACF ta bayyana cewa kungiyar ba za ta goyi bayan duk wani dan takarar shugaban kasa a bainar jama’a a zaben 2027 ba.

 

Da yake magana ta wayar tarho a ranar Lahadi, sakataren yada labarai na ACF na kasa, Farfesa T.

A. Muhammad Baba, wanda aka nemi ya yi tsokaci kan kalaman Baba-Ahmed, ya ce a matsayinsa na dattijo, Baba-Ahmed yana da ‘yancin bayyana ra’ayinsa.

 

Mai magana da yawun ACF, duk da haka, kungiyar za ta bincika dukkan batutuwan tare da gabatar da su ga masu jefa kuri’a don su iya yin zabi mai kyau a 2027.

 

“Dakta Baba-Ahmed yana da ‘yancin bayyana ra’ayinsa. Bai dade da ya bar cikin gwamnati ba, kuma duk abin da ya ce hakkinsa ne. Kun san muna gab da zabukan 2027, kuma yawancin irin wadannan ra’ayoyin mutane da kungiyoyi za su bayyana a yayin da zabuka ke gabatowa. Muna sa ran ganin karin irin wannan sharhi. Ko yake, ACF ba kungiya ce ta siyasa ba. Ba ma nuna bangaranci.

 

“Yayin da zabe ke gabatowa, za mu iya nazarin batutuwa ne kawai mu gabatar da su ga masu jefa kuri’a don su yanke shawarar wanda za su zaba. Ba za mu bayyana goyon baya ga duk wani dan takarar jam’iyyar siyasa da zai tsaya takara a zaben shugaban kasa a 2027 ba. Za mu ci gaba da kasancewa a matsayin kungiyar kare muradun al’ummar Arewa,” in ji ACF.

 

A halin da ake ciki, wata kungiya mai suna ‘Arewa Think Tank’ (ATT), ta nuna goyon baya ga matsayin Gwamnan Jihar Nasarawa Abdullahi Sule cewa ya kamata Arewa ta yi aiki don sake zaben Bola Tinubu a 2027.

 

A kwanan nan ne Gwamna Sule ya bayyana cewa Arewa na bukatar hada kai don aiwatar da yunkurin Shugaba Tinubu ba.

 

A kan kashe-kashen da aka yi kwanan nan a jihohin Filato da Benuwai, Arewa Think Tank ta yi zargin cewa makiyan ‘yan siyasa suna yin duk mai yiwuwa, ciki har da shigar da kasashen waje, don kawo cikas ga gudanar da babban zabben 2027.

 

A cikin wata sanarwa da shugaban ATT, Muhammad Alhaji Yakubu ya fitar, ya ce kungiyar ta sha alwashin goyon bayan yin tazarcen Shugaba Tinubu, domin ya ci gaba da ayyukan da ya faro.

 

“Mun san cewa goyon bayan wa’adi na biyu na Shugaba Tinubu zai cika alkawarin da ya yi wa yankin Arewa tun gabanin babban zaben 2023.

 

“Mun amince kuma mun goyi bayan Gwamna Sule saboda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Arewa ta tsakiya, kuma mun san cewa ba a san Arewa da yin watsi da alkawuran da ta dauka ba.”

 

ATT ta bukaci shugabannin Arewa da su nesanta kansu daga wasu ‘yan siyasa da ke da niyyar rikitar da siyasar Nijeriya saboda sun kasa cimma burinsu.

 

Kungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta rufe kan iyakokin kasar nan tare da hana bakin haure shigowa Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar

Bayan hare-haren da kungiyoyin yan ta’adda masu iko da kasar Siriya suka kai kan wani Cuci a kasar Siriya jami’an gwamnatin kasar Siriya sun nuna damuwarsu da yiyuwar wadannan kungiyoyi su kawo hare-hare a cikin kasar ta Lebanon musamman a cikin wadan nan kwanaki na makokin Imam Hussain (a).

Wani Jami’in gwamnati a kasar ta Lebanon ya fadawa Jaridar da The National ta kasar Amurka kan cewa a makon da ya gabata an kama wani shugaban yan kungiyar yan ta’adda ta ISIS a cikin kasar, tare da zarginsa da shiri hare-hare masu yawa a kasar Lebanon.

Kafin haka dai a cikin watan da ya gabata wani dan ta’ada ya tarwatsa kansa a cikin wani coci a birnin Damascus babban birnin kasar Siriya inda ya kashe mutane 25.

Kungiyar yan ta’adda ta Daesh dai sun fara aiki karkashin kasa tun bayan da dakarun kungiyar Hizbulla.. da kuma sojojin kasar Lebanon sun fatattakesu a shekara 2017. Sannan a wasu lokutan sun kai hare-hare kan kungiyar Hizbullah a kasar.

Sannan bayan kungiyar HTS ta kwace mulki a hannun shugaba Asad a shekarar da ta gabata, har yanzun akwai yiyuwar barazanar hare-haren ISIS tana nan a kan kasar ta Lebanon.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
  • Kebbi: PDP za ta yi haɗaka don ƙalubalantar APC a zaɓen 2027
  • Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
  • Sheikh Na’im Kasim: Muna Da Karfin Ci Gaba Da Bugawa Da Abokan Gaba
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  • Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
  • Za a birne Aminu Ɗantata a Madina – Iyalansa