Leadership News Hausa:
2025-08-15@13:08:38 GMT

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

Published: 26th, April 2025 GMT

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

Ya kara da cewa kungiyar dattawan Arewa ba za ta lamunci cin zarafin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba.

 

Sai dai da take magana da LEADERSHIP, ACF ta bayyana cewa kungiyar ba za ta goyi bayan duk wani dan takarar shugaban kasa a bainar jama’a a zaben 2027 ba.

 

Da yake magana ta wayar tarho a ranar Lahadi, sakataren yada labarai na ACF na kasa, Farfesa T.

A. Muhammad Baba, wanda aka nemi ya yi tsokaci kan kalaman Baba-Ahmed, ya ce a matsayinsa na dattijo, Baba-Ahmed yana da ‘yancin bayyana ra’ayinsa.

 

Mai magana da yawun ACF, duk da haka, kungiyar za ta bincika dukkan batutuwan tare da gabatar da su ga masu jefa kuri’a don su iya yin zabi mai kyau a 2027.

 

“Dakta Baba-Ahmed yana da ‘yancin bayyana ra’ayinsa. Bai dade da ya bar cikin gwamnati ba, kuma duk abin da ya ce hakkinsa ne. Kun san muna gab da zabukan 2027, kuma yawancin irin wadannan ra’ayoyin mutane da kungiyoyi za su bayyana a yayin da zabuka ke gabatowa. Muna sa ran ganin karin irin wannan sharhi. Ko yake, ACF ba kungiya ce ta siyasa ba. Ba ma nuna bangaranci.

 

“Yayin da zabe ke gabatowa, za mu iya nazarin batutuwa ne kawai mu gabatar da su ga masu jefa kuri’a don su yanke shawarar wanda za su zaba. Ba za mu bayyana goyon baya ga duk wani dan takarar jam’iyyar siyasa da zai tsaya takara a zaben shugaban kasa a 2027 ba. Za mu ci gaba da kasancewa a matsayin kungiyar kare muradun al’ummar Arewa,” in ji ACF.

 

A halin da ake ciki, wata kungiya mai suna ‘Arewa Think Tank’ (ATT), ta nuna goyon baya ga matsayin Gwamnan Jihar Nasarawa Abdullahi Sule cewa ya kamata Arewa ta yi aiki don sake zaben Bola Tinubu a 2027.

 

A kwanan nan ne Gwamna Sule ya bayyana cewa Arewa na bukatar hada kai don aiwatar da yunkurin Shugaba Tinubu ba.

 

A kan kashe-kashen da aka yi kwanan nan a jihohin Filato da Benuwai, Arewa Think Tank ta yi zargin cewa makiyan ‘yan siyasa suna yin duk mai yiwuwa, ciki har da shigar da kasashen waje, don kawo cikas ga gudanar da babban zabben 2027.

 

A cikin wata sanarwa da shugaban ATT, Muhammad Alhaji Yakubu ya fitar, ya ce kungiyar ta sha alwashin goyon bayan yin tazarcen Shugaba Tinubu, domin ya ci gaba da ayyukan da ya faro.

 

“Mun san cewa goyon bayan wa’adi na biyu na Shugaba Tinubu zai cika alkawarin da ya yi wa yankin Arewa tun gabanin babban zaben 2023.

 

“Mun amince kuma mun goyi bayan Gwamna Sule saboda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Arewa ta tsakiya, kuma mun san cewa ba a san Arewa da yin watsi da alkawuran da ta dauka ba.”

 

ATT ta bukaci shugabannin Arewa da su nesanta kansu daga wasu ‘yan siyasa da ke da niyyar rikitar da siyasar Nijeriya saboda sun kasa cimma burinsu.

 

Kungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta rufe kan iyakokin kasar nan tare da hana bakin haure shigowa Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kundin tsarin mulki na hukumar sadarwa ta Najeriya (NCC) da asusun samar da ayukka na kasa da kasa (USPF), dukkanin su a karkashin ma’aikatar sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arziki na zamani.

 

A cikin wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai baiwa shugaban kasa shawara kan yada labarai ya fitar, ya ce an nada Idris Olorunnimbe a matsayin shugaban hukumar NCC, yayin da Dr. Aminu Waida ya ci gaba da zama mataimakin shugaban zartarwa/Babban jami’in gudanarwa, mukamin da aka nada shi a watan Oktoban 2023 kuma majalisar dattawa ta tabbatar da shi a watan Nuwamba na wannan shekarar.

 

A baya Olorunnimbe ya yi aiki a hukumar kula da ayyukan yi na jihar Legas (LSETF), inda ya jagoranci kwamitin masu ruwa da tsaki da gudanar da mulki tare da jagorantar shirye-shiryen samar da ayyukan yi da samar da kasuwanci ga matasa.

 

Sauran mambobin hukumar NCC sun hada da Abraham Oshidami (Kwamishina, Ayukkan Fasaha), Rimini Makama (Kwamishiniyar Gudanarwa), Hajia Maryam Bayi (Kwamishinar kula da ma’aikata), Col. Abdulwahab Lawal (Rtd), Sanata Lekan Mustafa, Chris Okorie, Gimbiya Oforitsenere Emiko, da Sakataren Hukumar.

 

 

Ga USPF, Dokta Bosun Tijani, Ministan Sadarwa, Ƙirƙiri da Tattalin Arziki na Zamani, zai zama shugaba. Olorunnimbe kuma an nada mataimakin shugaba.

 

Sauran mambobin sun hada da Oshidami, Makama, Aliyu Edogi Aliyu (wakilin FMCIDE), Joseph B. Faluyi (Ma’aikatar Kudi ta Tarayya), Auwal Mohammed (Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsare ta Tarayya), Uzoma Dozie, Peter Bankole, Abayomi Anthony Okanlawon, Gafar Oluwasegun Quadri, da Sakataren USPF.

 

PR/Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
  • Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
  • Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu
  • Shugaban Tinubu Ya Rantsar Da Farfesa Dakas James Shugaban Hukumar Gyaran Dokoki Ta Kasa
  • Kano Na Karbar Bakuncin Babban Taron Kungiyar NUJ Na Kasa
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
  • Lafiyar Tinubu kalau – Soludo