Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Published: 26th, April 2025 GMT
A cewar kungiyar ta OPEC, wannan ya ya faru ne duk da raguwar yawan man da Nijeriya ta samar a watan da ya gabata, musamman idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.46 a kowace rana a watan Fabrairun da ya gabata.
Rahoton ya ci gaba da cewa, duk da raguwar, yawan Man da kasar nan ta samar shi ne mafi yawa a Afirka, inda ya zarce na kasashen Algeria da Dimoliradiyyar Kongo.
Kazalika, kungiyar ta bayyana cewa, ta hanyar ci gaba da karfin da ta samu a watan Fabrairu, kasar nan, dara kasar Algeria, inda ta samar da ganga 909,000 a kowace rana, da kuma jamuriyar Kongo da ta samar da ganga 263,000 a kowace rana.
Kungiyar ta kara da cewa, kasar nan, ta samar da ganga miliyan 1.51 a kowace rana a watan Maris da ya wuce, idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.54 a kowace rana a watan Fabrairun da ya gabata.
Bugu da kari, hukumar kula da harkokin Man Fetur na kan tudu ta kasa NUPRC, ta bayyana cewa, yawan Man da Nijeriya ta samar ya ragu zuwa ganga 1,400,783 a kowace rana a watan Maris da wuce.
Sai dai, a cewar hukumar, duk da raguwar yawan man da aka samar a watan Maris da ya gabata, matsakaicin yawan Danyen Man da aka samar a Nijeriya, ya kai kaso 93 cikin dari na adadin ganga miliyan 1.5 da kungiyar OPEC ta ware wa Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: a kowace rana a watan ganga miliyan 1 yawan Man da da ya gabata
এছাড়াও পড়ুন:
An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Gombe
Gwamna Mai Mala Buni, ya ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutane 48,000 domin jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ƙara ƙarfafa matakan kiwon lafiya a matakin farko a fadin Jihar Yobe.
Buni ya bayyana shirin fara samar da daidaito a bangaren kiwon lafiya wanda zai samar da inshorar lafiya ga mata masu rauni da yara ‘yan kasa da shekaru biyar sama da 38,000 a fadin jihar.
Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a ZariyaGwamnan ya bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba yayin da ya kaddamar da wasu sabbin tsare-tsare da nufin fadada harkokin kiwon lafiya, musamman ga marasa galihu.
Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin jawabinsa a wajen babban taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Damaturu, wanda ya samu halartar sarakunan gargajiya da malaman addini, abokan hulda, ma’aikatan lafiya da manyan jami’an hukumar gudanarwa a bangaren samar da kiwon lafiya a matakin farko da kuma kungiyoyin farar hula.
Gwamna Buni ya bayyana manufarsa ta samar da lafiya mai rahusa a matsayin ginshikin ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin al’umma.
Ya amince da goyon bayan gwamnatin tarayya da abokan hulda da suka hada da Gidauniyar Bill and Melinda Gates, Aliko Dangote Foundation, UNICEF, da WHO da dai sauransu.
Gwamnan ya jaddada kudirin jihar na samar da kiwon lafiya, inda ya ba da misali da kafa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 142, samar da kayan aiki da magunguna, da daukar kwararrun ma’aikatan kiwon lafiya sama da 2,000 a fadin Jihar.
Ya bayyana irin nasarorin da jihar ta samu ciki har da fitowar ta a matsayin zakara ta shekarar 2024 a bangaren samar da kiwon lafiya a matakin farko a fadin kasar nan ta Champion leadership for Primary Health Care PHC 2024.
Ya kuma yi tsokaci kan kafa Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Jihar Yobe (YSCHMA) da Hukumar Kula da Magunguna ta Jihar Yobe (YODMA) don magance kuɗaɗen kula da lafiya da samar da magunguna.
Kazalika, ya bukaci sarakunan gargajiya da su ba da goyon baya tare da bayar da gudunmawa wajen karfafa ayyukan kiwon lafiya a matakin farko a yankunansu.
Gwamnan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su lura da batutuwan da aka tattauna a taron tare da magance kura-kuran da ake da su a yankunansu da kuma wuraren gudanar da ayyukansu domin kara inganta harkar kiwon lafiya a matakin farko a Jihar.