Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Published: 26th, April 2025 GMT
A cewar kungiyar ta OPEC, wannan ya ya faru ne duk da raguwar yawan man da Nijeriya ta samar a watan da ya gabata, musamman idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.46 a kowace rana a watan Fabrairun da ya gabata.
Rahoton ya ci gaba da cewa, duk da raguwar, yawan Man da kasar nan ta samar shi ne mafi yawa a Afirka, inda ya zarce na kasashen Algeria da Dimoliradiyyar Kongo.
Kazalika, kungiyar ta bayyana cewa, ta hanyar ci gaba da karfin da ta samu a watan Fabrairu, kasar nan, dara kasar Algeria, inda ta samar da ganga 909,000 a kowace rana, da kuma jamuriyar Kongo da ta samar da ganga 263,000 a kowace rana.
Kungiyar ta kara da cewa, kasar nan, ta samar da ganga miliyan 1.51 a kowace rana a watan Maris da ya wuce, idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.54 a kowace rana a watan Fabrairun da ya gabata.
Bugu da kari, hukumar kula da harkokin Man Fetur na kan tudu ta kasa NUPRC, ta bayyana cewa, yawan Man da Nijeriya ta samar ya ragu zuwa ganga 1,400,783 a kowace rana a watan Maris da wuce.
Sai dai, a cewar hukumar, duk da raguwar yawan man da aka samar a watan Maris da ya gabata, matsakaicin yawan Danyen Man da aka samar a Nijeriya, ya kai kaso 93 cikin dari na adadin ganga miliyan 1.5 da kungiyar OPEC ta ware wa Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: a kowace rana a watan ganga miliyan 1 yawan Man da da ya gabata
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
Manajar ofishin na NIWA, da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.
Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.
“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.
“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.
Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA, Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa da ke a sassan kasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA