A cewar kungiyar ta OPEC, wannan ya ya faru ne duk da raguwar yawan man da Nijeriya ta samar a watan da ya gabata, musamman idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.46 a kowace rana a watan Fabrairun da ya gabata.

 

Rahoton ya ci gaba da cewa, duk da raguwar, yawan Man da kasar nan ta samar shi ne mafi yawa a Afirka, inda ya zarce na kasashen Algeria da Dimoliradiyyar Kongo.

 

Kazalika, kungiyar ta bayyana cewa, ta hanyar ci gaba da karfin da ta samu a watan Fabrairu, kasar nan, dara kasar Algeria, inda ta samar da ganga 909,000 a kowace rana, da kuma jamuriyar Kongo da ta samar da ganga 263,000 a kowace rana.

 

Kungiyar ta kara da cewa, kasar nan, ta samar da ganga miliyan 1.51 a kowace rana a watan Maris da ya wuce, idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.54 a kowace rana a watan Fabrairun da ya gabata.

 

Bugu da kari, hukumar kula da harkokin Man Fetur na kan tudu ta kasa NUPRC, ta bayyana cewa, yawan Man da Nijeriya ta samar ya ragu zuwa ganga 1,400,783 a kowace rana a watan Maris da wuce.

 

Sai dai, a cewar hukumar, duk da raguwar yawan man da aka samar a watan Maris da ya gabata, matsakaicin yawan Danyen Man da aka samar a Nijeriya, ya kai kaso 93 cikin dari na adadin ganga miliyan 1.5 da kungiyar OPEC ta ware wa Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a kowace rana a watan ganga miliyan 1 yawan Man da da ya gabata

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Rabon Na’urorin Rarraba Lantarki 500

A wani yunkuri na bunkasa samar da wutar lantarki da kuma bunkasar tattalin arziki, gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da rabon kashi na farko na taransfoma 500 ga al’ummomin karkara a fadin kananan hukumomin jihar 44.

 

Gwamna Abba Yusuf ne ya kaddamar da shi a hukumance a Kano a wani shirin da nufin magance kalubalen rashin samar da wutar lantarki.

 

Gwamna Yusuf ya ce samar da taransfoma wani shiri ne na bunkasa masana’antu da zaburar da harkokin kasuwanci musamman a yankunan karkara.

 

“Wannan rabon shi ne kashi na farko na aikin samar da wutar lantarki a yankunan karkara, ba wai kawai wani aikin samar da wutar lantarki ba ne, wani muhimmin mataki ne na inganta samar da wutar lantarki ga jama’armu. Samar da wutar lantarki mai inganci na da matukar muhimmanci ga ci gaban masana’antu da bunkasar tattalin arziki.”

 

Gwamnan ya bukaci masu ruwa da tsakin al’umma da su mallaki na’urar taransifoma gaba daya, sannan ya umurci shugabannin kananan hukumomin da su kafa kwamitoci don kula da ayyukan da kuma tabbatar da tsaro.

 

Kwamishinan Ma’aikatar Raya Karkara da Cigaban Al’umma Abdulkadir Abdulsalam ya yabawa kokarin Gwamnan na inganta rayuwar al’umma da bunkasa tattalin arzikin karkara.

 

“Wannan rabon na nuna alamar ci gaba da yunƙurin da Gwamna ya yi na tunkarar ƙalubalen da al’ummomin karkara ke fuskanta. Na’urar taransifoma za ta inganta rayuwar jama’a sosai, da inganta tattalin arziƙi, da kuma jawo hankalin masu zuba jari.”

 

Bikin ya samu halartar mataimakin gwamnan jihar Kano, kakakin majalisar dokokin jihar Kano, mai martaba Sarkin Karaye, da manyan jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
  • An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya
  • Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito
  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Yobe
  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Gombe
  • NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
  • An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Rabon Na’urorin Rarraba Lantarki 500
  • Sheikh Kassim: Mayakan Hizbullah Mazajen Fagen Daga Ne
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala