Aminiya:
2025-11-03@06:23:02 GMT

Na shiga fim ne don isar da saƙon Musulunci — Malam Inuwa Ilyasu

Published: 26th, April 2025 GMT

A wannan makon Aminiya ta samu tattaunawa da shahararren jarumi a masana’antar fina-finan Hausa ta Kannyood, Malam Inuwa Ilyasu, wanda ya shafe sama da shekara 40 yana harkar wasan kwaikwayo. Ga yadda tattaunawar ta kasance:

Gabatar da kanka?

To da farko dai sunana Inuwa Ilyasu.

Yaushe ka fara harkar fim?

Gaskiya dai kusan da ni aka fara yin fim kuma lokacin da muka fara yi, mun fara da yin tunanin ya za mu yi saboda kafin nan ai akwai wasan daɓe da muka fara yi.

A wancan lokaci muna faɗakarwa ta wasan kwaikwayo kusan tun wajejen 1970. Daga nan muka fara tunanin ta yaya za mu yi ƙoƙarin mu ma mu fara yin irin namu.

Yawancin fina-finanka kana fitowa ne a matsayin malami, kana faɗakarwa ko bayar da shawara a addinance. Wannan matsayin kai kake zaɓa ko kuwa masu shirya fim ne suke ba ka?

A’a ba ni na zaɓar wa kaina ba.

Idan na fahimce ka, an duba cancanta da kuma wanda aka gani zai iya bayar da abin da ake so ake ɗora ka a kai?

Yauwa, ana yin sa’a ce dai za ni ce ta tarar da mu je, domin ni daman dalilina na yin wasan kwaikwayo shi ne, saboda in samu in cusa aƙida ta addinin Musulunci da tarbiyartarwarsa da kuma cusa al’adarmu da ɗabi’unmu ga matasa masu tasowa. Misali, ai ka ga irin yadda wasu masu fim ɗin Indiya suke cin karensu babu babbaka.

Daga lokacin da ka fara wasan daɓe zuwa yadda ka juya zua yin fim, shin kana ga saƙonnin da kake son isar wa jama’a suna tasiri wajen faɗakarwa ?

Alhamdulillahi, ana samun nasara Insha Allahu, saboda mutane da yawa in na haɗu da su ko kuma ma wasu su ne za su neme ni, su yi yabo saboda Allah Ya sa sun ci karo da wata faɗakarwa da na yi a wani shirin da ta yi tasiri matuƙar gaske ga rayuwarsu.

Ka shafe sama da shekara 40 a sana’ar harkar fim, ko kai ma ka fara tunanin kafa wani kamfani da idan ka yi fim za ka riƙa ɗorawa a manhajar Youtube kamar yadda wasunku ke yi halin yanzu?

To ni irin wannan ba ya cikin tunanina. Kamar yadda na gaya maka a baya, mun fara yi ne da manufa, kuma muna yi ne domin faɗakarwa ga jama’a a ƙarƙashin ƙungiya da na faɗa mai suna “Dabo”. Haka kuma mun samu nasara, domin wasu daga cikin waɗanda suke a Kannywood ɗin cewa suke yi daga kallon fim ɗin da muke yi, suka koya. Wasu kuma daga irin faɗakarwar da ake yi a fim ta ba su sha’awa har su ma suka shigo matsayin masu yin fim. Wani kuma zai ce shi fim ya kalla, ya sa masa soyayyar abin a zuciyarsa, Alhamdulillahi an samu ci gaba sosai da nasara.

Kamar ta wace gaɓa nasarorin da aka samu?

Gaɓoɓin da dama, saboda za ka samu wasannin da muka yi, wasu suka kalla za su ɗauki darasin rayuwa, sannan muna harkar arziki da jama’a, ana ta nuna mana soyayya ba wata matsala. Sannan idan ma suna muke so mu samu, mun samu. Kai wasu ma na raɓe da mu, sun samu sannan akwai da dama da suke son su samu dama kamar yadda muka samu, amma ba su samu ba.

Wato dai fim ɗin duk da ka fito rawar da kake takawa da aka ba ka ana amfana da ita a kan duk abin da ka faɗakar ko ka a addinance ko a al’adance?

Eh, an samu ci-gaba sosai kuma Alhamdulillahi.

Ya kake kallon ƙalubalen da ake samu a tsakanin masu harkar fim?

Ban fahimce ka ba.

Irin ’yan matsaloli da ka taso tsakanin mawaƙa ko masu yin fim na baya-bayan nan da ake zargin su da wuce gona da iri?

Irin waɗannan abubuwan gaskiya muna ta yaƙin su a matsayinmu na dattawa. Amma ka san ɗan-adam sai da hikima.

Wace shawara kake da ita ga Masana’antar Kannywood da kuma masu nufin nan gaba su shigo ta, lura da cewa yanzu ka zama uba a cikinta tun daga kan hukuma da kuma jarumai?

Eh to akwai buƙatar sake duba inda hukuma za ta shigo ta gyara a cikin harkar, domin muna magana ne a kan addini da tarbiyya, musamman ta Musulmi. Ya kamata a ce gwamnati da ta kafa wannan hukuma ta tallafi to kuma ta duba hanyar da za ta tallafa wa wannan harkar saboda harkar fim tana bayar da dama ga matasa ta samun sana’a. Haka kuma tana hana zaman kashe wando. Sannan kuma ana amfani da fim wajen kawar da wasu miyagun abubuwa da suke faruwa a cikin al’umma, ta yadda ba sai an fito, ana kokawa ko kama mutane ba don yin gyaran. Saboda mu ƙalubale gare mu, mu tabbatar masu kallo za su gamsu da abin da muke yi kuma su faɗaka.

Ban sani ba ko akwai wani saƙo da kake son ka isar?

Saƙona shi ne, kowa lallai yana da buƙatar ya sanya hannu wajen tallafa wa wannan harka ta fim, saboda ta shafe shi a abin da ya shafi addininsa da al’adarsa. Don haka ya kamata kowa ya duba ta ina zai taimaka yadda za ta inganta, ta dace da waɗannan muhimman abubuwa.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kannywood kwaikwayo

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

A 2022, kasashe shida ne suka daina yanke hukuncin kisa, ko dai gaba daya ko kuma wani bangare.

Hudu daga cikinsu; Kazakhstan, Papua New Guinea, Saliyo, Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, sun jingine shi kwatakwata.

Ekuatorial Guinea da Zambia sun ce za a rika amfani da shi ne kawai kan laifuka mafiya kololuwar muni.

A watan Afrilun 2023, majalisar dokokin Malaysia ta kada kuri’ar daina amfani da shi a matsayin tilas kan laifuka 11, ciki har da kisa da kuma ta’addanci.

Majalisar dokokin Ghana ma ta kada kuri’ar soke hukuncin kisa a watan Yulin 2023.

 

Wadanne kasashe ne suka fi yanke hukuncin kisa?

Kasashe 20 ne suka zartar da hukunbcin kisa a 2022, idan aka kwatanta da 18 da suka yi hakan a 2021.

Kungiyar kare hakki ta Amnesty International ta ce jimillar mutum 1,518 aka zartar wa hukuncin kisa a duniya, inda aka samu karin kashi 32 cikin 100. Sai dai ta ce hakikanin adadin ya zarta haka sosai saboda yadda kasashe ke boye batun.

Bayan China, Amnesty ta ce kasashen da suka fi kashe mutane a 2024 su ne Iran (972), da Saudiyya (345), da kuma Iraki (63). Su ne suka zartar da kashi 91 cikin 100 na duka kasashen duniya.

Ana yi wa China kallon kasar da ta zarta kowacce aiwatar da hukuncin kisa a duniya, amma ba a sanin hakikanin adadin mutanen, saboda gwamnati ba ta bayyana su.

Kasashen Koriya ta Arewa da Bietnam ma na amfani da hukuncin kisa sosai amma ba su bayyanawa a hukumance.

Amnesty ta ce ta samu rahoton zartar da hukuncin kisa a bainar jama’a akalla sau uku a 2022 a Iran.

Ta ce Iran din ta kashe akalla mutum biyar saboda laifukan da suka aikata a lokacin da suke kasa da shekara 18 da haihuwa.

Saudiyya ta kashe mutane mafiya yawa a duniya a 2022 cikin shekara 30.

Kasashe biyar; Bahrain, Comoros, Laos, Nijar, Koriya ta Kudu – su ne suka yanke wa mutane hukuncin kisa a 2022 bayan sun shafe tsawon lokaci ba su yi amfani da shi ba.

Duk da cewa adadin na raguwa a Amurka, amma ya karu a 2021, amma duk da haka ya yi kasa sosai idan aka kwatanta da shekarar 1999.

 

Mutum nawa aka kashe saboda safarar miyagun kwayoyi?

Amnesty International ta ce sama da kashi 40 cikin 100 na mutanen da aka zartar wa hukuncin kisa a 2024 saboda laifukan ta’ammali da miyagun kwayoyi ne.

A 2022, an kashe mutum 325 saboda laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi. Kasashen da suka aikata hakan su ne:Iran 255 Saudiyya – 57 – Singapore – 11

A 2023, Singapore ta zartar da hukuncin kisa kan mace ta farko cikin shekara 20. A 2018 aka kama Saridewi Djaman da laifin safarar hodar ibilis.

 

Ta yaya kasashe ke zartar da hukuncin kisa?

Saudiyya ce kadai ta zayyana fille kai a matsayin hanyar aiwatar da hukuncin kisa a 2022.

Sauran hanyoyin sun hada da rataya, da allura mai guba, da kuma harbi da bindiga.

A watan Janairun 2024 jihar Alabama ta Amurka ta zartar wa wani mai laifin kisa Kenneth Smith hukuncin kisa ta hanyar amfani da iskar nitrogen gas.

Ya zama mutum na farko a duniya da aka zartar wa hukuncin ta irin wannan hanyar, a cewar cibiyar Death Penalty Information Center da ke Amurka.

Lauyoyin Mista Smiths sun ce salon da ba a taba gwadawa ba kafinsa “rashin imani ne”.

Alabama da wasu jihohin Amurka biyu ne suka amince da amfani da iskar gas din saboda kwayoyin da ake amfani da su wajen yi wa mutum allura mai guba ba sa samuwa cikin sauki.

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025 Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma