Falasdinawa 39 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’o’I 24
Published: 27th, April 2025 GMT
A cikin sa’o’i 24 da su ka gabata an sami shahidai 39 sanadiyyar hare-haren wuce gona da iri da sojojin mamaya su ka kai a sassa mabanbanta na zirin Gaza.
A birnin Khan-Yunsu Falasdinawa 3 sun yi shahada, daga cikinsu da akwai karamin yaro, yayin da wasu da dama su ka jikkata.
Majiyar kiwon lafiya ta Falasdinawa ta ambaci cewa, wani masunci ya yi shahada saboda harin da ‘yan sahayoniya su ka kai masa a gabar ruwan garin Khan-Yunus.
A wani labarin daga yankin na Gaza, sojojin HKI suna ci gaba da rusa gidajen fararen hula a arewacin birnin Rafah dake kudancin zirin Gaza.
Tun da HKI ta sake komawa yaki gadan-gadan akan al’ummar Falasdinu a ranar 18 ga watan Maris, Falasdinawa 2,111 ne su ka yi shahada, yayin da wasu 5,483 su ka jikkata.
Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza da ta fitar da wannan kididdigar ta kuma bayyana cewa; tun daga 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu jumillar Falasdinawan da su ka yi shahada, sun kai 51,495 wadanda kuma su ka jikkata sun kai 117,524.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
Uwargidan Shugaban Nijeriya, Sanata Remi Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.
Sanata Tinubu wadda ta miƙa cakin kuɗin ga Gwamna Hyacinth Alia ta sanar da bayar da tallafin ne a jawabinta na jaje wanda ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke Makurdi.
Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a ChinaUwargidan shugaban ƙasar ta buƙaci a yi amfani da wannan tallafin a matsayin gudunmawar farfaɗo da yankin da waɗanda suka tsallake rijiya da baya a yayin harin musamman yaran da yanzu ke buƙatar komawa makarantu.
Ana iya tuna cewa, tun a daren ranar 13 ga watan Yuni zuwa wayewar gari 14 ga watan ne aka kashe fiye da mutum 100 a ƙauyen Yelwata, lamarin da ya janyo Allah wadai daga sassa daban-daban a faɗin ƙasar.
Jihar Benuwe dai na daga cikin jihohin da ke fuskantar matsalar tsaro a Nijeriya, musamman rikicin manoma da makiyaya da kuma na ƙabilanci, wanda ke sanadiyyar salwantar rayuka da dama.