HausaTv:
2025-06-15@00:30:09 GMT

Falasdinawa 39 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’o’I 24

Published: 27th, April 2025 GMT

A cikin sa’o’i 24 da su ka gabata an sami shahidai 39 sanadiyyar hare-haren wuce gona da iri da sojojin mamaya su ka kai a sassa mabanbanta na zirin Gaza.

A birnin Khan-Yunsu Falasdinawa 3 sun yi shahada, daga cikinsu da akwai karamin yaro, yayin da wasu da dama su ka jikkata.

Majiyar kiwon lafiya ta Falasdinawa ta ambaci cewa, wani masunci ya yi shahada  saboda harin da ‘yan sahayoniya su ka kai masa a gabar ruwan garin Khan-Yunus.

A wani labarin daga yankin na Gaza, sojojin HKI suna ci gaba da rusa gidajen fararen hula a arewacin birnin Rafah dake kudancin zirin Gaza.

Tun da HKI ta sake komawa yaki gadan-gadan akan al’ummar Falasdinu a ranar 18 ga watan Maris, Falasdinawa 2,111 ne su ka yi shahada, yayin da wasu 5,483 su ka jikkata.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza da ta fitar da wannan kididdigar ta kuma bayyana cewa; tun daga 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu jumillar Falasdinawan da su ka yi shahada, sun kai 51,495 wadanda kuma su ka jikkata sun kai 117,524.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya

A yau ne Najeriya ke bikin ranar Dimokuraɗiyya, wanda masana siyasa a ciki da wajen ƙasar ke jinjina kan yadda aka kwashe shekara 26 kan tafarkin mulkin farar hula.

Najeriya, ta kasance ƙasa mafi yawan al’umma a Nahiyar Afirka inda ake bikin murnar ranar dimokuraɗiyyar domin tunawa da zaɓen 12 ga watan Yuni wanda ake ganin shi ne zaɓe mafi inganci da aka taɓa gudanarwa a Najeriya.

NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya? An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato

Hakan dai na zuwa ne duk kuwa da cewa an soke zaɓen, lamarin da ya haifar da taƙaddama da ruɗani game da zaɓen.

Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ne ya sauya bikin ranar dimokuradiyyar daga 29 ga watan Mayu zuwa 12 ga watan Yuni domin karrama wanda ake da yaƙinin shi ne ya lashe zaɓen shugaban ƙasar na 1993, wato Moshood Abiola.

Hakan dai na nufin Najeriya ta kwashe shekara 26 tana kan tafarkin mulkin farar hula dimukuraɗiyya ba tare da katsalandan na sojoji ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki