Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Published: 29th, April 2025 GMT
kauyuka a China, ana nufin yankunan da suka bunkasa, wadanda suka kasance, sun yi kamance-ceniya da sun anguwanin GRA a Nijeriya da kuma a nahiyar Afirka.
A yankin na Hero Bay, an tanadar da tituna inganciyyar wutar lantarki, tsaftatattacen ruwan sha da kuma kafar Inernet
Akwai manyan bene masu tsawo a yankin, wadanda tsawonsu ya dara na bene mai hawa biyar, inda kuma aka tanadar wa da yankin, ababen more rayuwa.
kananan hukumomi ne, suka gina wadannan matsugunnan, musamman donin a dakile barazanar kwararowa alumma daga kauye, zuwa cikin birane.
A gwajin da aka yi na yankunan da su habaka sosai a China, ana buga misali da Hero Bay kan yadda gwamnati ke bai wa alumma kwarin guiwa na su ci gaba da zama a yankunan da suke, musamman ta hayar samar masu tallafin kudi da gidaje.
Wannan dabarun, baya ga kara bunkasa fannin aikin noma a kauyukan, sun kuma kara habaka fannin fasaha kimiyya a kauyukan da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar.
Wani mai gudanar da aikin bincike a cibiyar yin bincike a fannin fasaha ta kasar Wang Yongzhong, ya alakanta kauyukan a matsayin guraren da suka yi fice a duniya, da makuntan kasar, suka samar masu da ababen more rayuwa.
Samar da hanyoyi na daga cikin ayyukan da gwamnatin China, ke bai wa mahimmanci, musamman domin a samar da damar gudanar da zirga-zirgar gudanar da ayyukan yau da kullum, a cikin sauki.
Samar da yankin na Hero Bay, na daga cikin babban misalin mayar da kan gwamnatin kasar, na dakile kwararowar mazauna a karkara, musamman a tsakanin matasa zuwa cikin birane.
Wasu biranen sun kasance cike suke da manyan rukunonin gidage, amma wannan sabanin haka ne, a Hero Bay, duba da yadda aka samar da gidaje, ga ‘yan kauyen da ke da ra’ayin zama a cikinsu, wanda kuma za su iya habaka kasuwancinsu da gudanar da aikin noma, tare da kuma samar da makarantu, Asibiti da jami’an tsaro da sauransu.
Daura da Hero Bay, akwai masana’antar kera motoci, wadda kuma ke samar da ayyukan yi ga mazauna yankin, ta hanyar goyon bayan ayyuakn shirye-shirye na kananan hukumomi.
A cewar Mataimakin Daraktan shirin bayar da horo China, Mista Wu Hao, gwamnatin kasar ta samar da wadannan ababen more rayuwar ne, domin a dakile kwararar mazauna kauyukan zuwa cikin biranen kasar.
daya daga cikin mazauna yankin Madam Yang Baozhen, ta tabbatar da wannan maganar ta Mista Wu Hao, inda ta ce, ana karfafawa, musamman matasa guiwa domin su shiga a dama da su, a fannin hada-hadar kasuwancin yankin, wanda hakan ka samar da kauyukan kudaden shiga.
Kazalika, mazauna kauyukan da ba su da bukatar shiga fannin noma ko yin aiki a masana’anta, su kan bude gidajen sayar da abinci ko kuma yin wasu kanannan sana’oi.
A kauykan, ana kuma bayar da ilimin zamani kyauta, tun daga matakin Firamare zuwa na Sakandare.
Bisa tsarin mallakar filaye a kauyukan ba za ka sayi fili ko kuma ka sayar da shi ba, amma za ka iya bayar da jinginarsa, har zuwa tsawon shekaru 50 zuwa 70, wanda daga baya, za ka sabunta jinginar.
A cewar wani mai zagaya wa masu yawon bude ido, “A kasar duk wani fili da ke kasar, mallakar gwamnatin kasar ne, wadda kuma kowanne fili, an tsara abinda za a yi a kansa,”
A yayin da ake ci gaba da tattauna wa kan batun bunkasa nahiyar Afrika ciki har da Nijeriya, akwai bukatar a rungumi irin wannan tsarin na China, duba da cewa, abu ne, da kwalliya za ta biya kudin Sabulu.
Kazalika, ta hanyarin yin hadaka da tsarin samar da hanyoyi na BRI na China hakan zai samar da wata ingantacciyar hadaka ga kasashe masu tasowa da kuma ga cibiyar bunkasa kasuwanci ta kasa da kasa ta AIBO da ke a karkashin ikon ma’aikatar bunkasa kasuwanci ta China, musamman wajen bayar da horo kan dabarun zamani na bunkasa kasuwanci.
Hakazalika, ta hanyar rungumar wannan tsarin China, Afirka za ta iya magance yawan kwararowar mazauna karkara, zuwa cikin birane, wanda hakan zai kuma taimaka wa kasashen da ke a Afrika, wajen kara bunkasa tattalin arzikinsu da samar wa da ‘yan Afrika, alkibla mai dorewa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
Hukumomin ’yan sandan Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu hukumomin tsaro sun samu gagarumar nasara a ƙoƙarin da suke na daƙile munanan laifuka a ƙasar.
Na baya-bayan nan dai shi ne ceto mutanen da aka sace, da kashe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma ƙwato manyan bindigogi da alburusai a jihohin Delta da Katsina.
Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a AustraliaA wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce a jihar Katsina an samu gagarumar nasara a ranar 8 ga watan Yunin 2025, inda haɗin gwiwar JTF da suka haɗa da jami’an ’yan sanda da sauran jami’an tsaro suka daƙile wani yunƙurin yin garkuwa da mutane a hanyar ƙauyen Danmusa zuwa Mara Dangeza a ƙaramar hukumar Danmusa.
Adejobi ya ce hakan na iya yiwuwa ne ta hanyar shigar da wasu gungun ’yan bindiga da suka yi yunƙurin guduwa da waɗanda aka yi garkuwa da su a wani artabu da ya kai ga ceto mutum 11.
Nasarar da aka samu yankin Kudu maso KuduA halin da ake ciki kuma, a yankin Kudu maso Kudu, Jihar Delta, hukumar ’yan sanda ta kama wani Abubakar Hassan, wanda babban wanda ake zargi da aikata laifin satar mutane ne a tsakanin jihohin Delta da Ribas da Imo, da Enugu.
Jami’an da ke da alaƙa da samun nasarar sun yi hakan ne yayin da suke aiki da sahihan bayanai.
A yayin da ake yi masa tambayoyi, Hassan ya bayyana cewa shi ne ya jagoranci gudanar da hari a yankin Ughelli-Ozoro na jihar mai arzikin man fetur.
Ya kuma jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa maɓoyarsa a wani daji da ke Ozoro. A can jami’an sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da tarin alburusai huɗu da harsashi guda talatin da biyu.