A watan Janairu, kwamitin ya raba naira tiriliyan 1.703 tare ga gwamnatoin tarayya da jihohi da kananan hukumomi. A wannan kudade, gwamnatin tarayya ta karbi naira biliyan 552.59, jihohi sun karbi naira biliyan 590.61, yayin da kuma kananan hukumomi sun karbi naira biliyan 434.57.

 

Rabon kudaden ya dogara ne kan kudaden shiga na naira biliyan 749.

73, harajin BAT naira biliyan 718.78, harajin canja wurin kudi ta hanyar lantarki na naira biliyan 20.55, da kuma karin naira biliyan 214.

 

Rabon watan Fabrairu ya kai naira biliyan 1.678, inda gwamnatin tarayya ta karbi naira biliyan 569.66, jihohi sun karbi naira biliyan 562.20, sannan kuma kananan hukumomi sun sami naira biliyan 410.56.

 

Kudaden shiga sun hada da naira biliyan 827.63 na kudaden shiga na doka da naira biliyan 609.43 daga VAT da naira biliyan 35.17 daga EMTL da naira biliyan 28.22 daga ma’adanai da karin naira biliyan 178.

 

A watan Maris, kwamitin ya raba naira tiriliyan 1.578. Gwamnatin tarayya ta karbi naira biliyan 528.70, jihohi sun karbi naira biliyan 530.45, sannan kuma kananan hukumomi sun karbi naira biliyan 387.

 

Kudaden shiga da aka rarraba sun hada da naira biliyan 931.33 a cikin kudaden shiga na doka da naira biliyan 593.75 daga harajin BAT da naira biliyan 24.97 daga EMTL, da naira biliyan 28.71 daga musayar kudade.

 

Kudaden shiga daga VAT a watan Janairun 2025 ya kai na naira biliyan 771.89, ya ragu zuwa naira biliyan 654.46 a watan Fabrairu da naira biliyan 637.62 a Maris. A halin yanzu, kudaden shiga na doka ya karu daga naira tiriliyan 1.848 a watan Janairu zuwa naira tiriliyan 1.653 a watan Fabrairu da naira tiriliyan 1.718 a watan Maris.

 

Duk da wadannan karin kudaden shiga, har yanzu kananan hukumomi ba su fara amsar kudadensu kai tsaye ba daga asusun tarayya, sabanin umarnin kotun koli da ta bayar a watan Yulin 2024.

 

Kotun koli ta ba da umarnin a biya kudaden kananan hukumomi daga asusun tarayya kai tsaye don tabbatar da ‘yancin cin gashin kansu na kudi da kuma kare su daga tsoma baki daga gwamnatocin jihohi.

 

Kungiyar kananan hukumomi ta Nijeriya (ALGON) ta zargi ofishin babban lauyan gwamnatin tarayya da kawo cikas ga aiwatar da ‘yancin cin gashin kai na kananan hukumomi, duk da cewa kotun koli ta yanke hukunci kan bayar da kudaden kai tsaye ga dukkan kananan hukumomi 774 da ke kasar nan.

 

ALGON ta kuma dauki matakin shari’a a kan babban lauyan gwamnatin tarayya da wasu cibiyoyin tarayya da dama a karar mai lamba ta FHC/ABJ/05/353/2025, suna nemanbai wa kananan hukumomi cikakken ‘yancin sarrafa kudadensu da kansu.

 

Karar ta kuma hada har ministan kudi, Wale Edun da ministan kasafin kudi da tsare-tsare na kasa, Abubakar Bagudu da akanta janar na tarayya da CBN da NNPCL da kuma bankunan kasuwanci a matsayin wadanda ake tuhuma.

 

ALGON ta ce ta dauki wannan matsayin a kotu ne da nufin ba kawai tilasta ‘yancin gashin kai a takarda ba har ma da tabbatar da aiwatar da shi.

 

Shari’ar wacce da farko aka shirya yi a gaban Mai Shari’a Inyang Ekwo, amma kotun ba ta samu zama ba. An dage shari’ar zuwa ranar 29 ga Mayu, 2025.

 

Da yake mayar da martani, Sakatare Janar na ALGON, Mohammed Abubakar, ya nuna takaicinsa kan ci gaba da jinkirin biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye duk da hukuncin kotun koli.

 

Abubakar ya ce lamarin ya zama mai rikitarwa kuma yawancin ‘yan Nijeriya sun yi takaicin faruwar hakan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: sun karbi naira biliyan naira tiriliyan 1 gwamnatin tarayya da naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal

An dawo da wutar lantarki a safiyar Talatar nan a Sifaniya da Portugal bayan katsewar da aka samu ta sa’o’i wadda ita ce mafi muni da aka gani a Turai.

A jiya Litinin ce dai miliyoyin mutane suka auka cikin duhu bayan ɗaukewar wutar lantarkin a ƙasashen biyu wadda ke ci gaba da ɗiga ayar tambaya kan abin da ya haifar da ita.

Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok

Kafofin watsa labarai sun ruwaito cewa ɗaukewar wutar lantarkin ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama da na ƙasa da katse hanyoyin sadarwa ta wayar hannu da kuma rufe na’urorin cire kuɗi na ATM a duk faɗin ƙasashen biyu.

Wata sanarwa da hukumar samar da wutar lantarki a Spain ta Red Electrica ta fitar, ta ce da misalin ƙarfe 7 na safiya agogon ƙasar, an samu nasarar dawo da sama da kashi 99 na wutar lantarki a ƙasar.

Haka nan ita ma takwararta ta Portugal ta ce tun cikin daren jiya Litinin, aka dawo da wutar lantarkin da dukkanin tashoshin wutar ƙasar guda 89.

Bayan ɗauke wutar da aka samu a Spain, jami’an ba da agajin gaggawa sun sanar da nasarar kuɓutar da mutane dubu 35 da suka maƙale a jiragen ƙasa na ƙarƙashin ƙasa.

Har yanzu dai hukumomi ba su bayyana dalilin da ya sa aka samu ɗaukewar wutar lantarkin ba, wanda shi ne karo na biyu da irin wannan mummunar katsewar wutar lantarki ta faru a Turai cikin watanni

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata