A watan Janairu, kwamitin ya raba naira tiriliyan 1.703 tare ga gwamnatoin tarayya da jihohi da kananan hukumomi. A wannan kudade, gwamnatin tarayya ta karbi naira biliyan 552.59, jihohi sun karbi naira biliyan 590.61, yayin da kuma kananan hukumomi sun karbi naira biliyan 434.57.

 

Rabon kudaden ya dogara ne kan kudaden shiga na naira biliyan 749.

73, harajin BAT naira biliyan 718.78, harajin canja wurin kudi ta hanyar lantarki na naira biliyan 20.55, da kuma karin naira biliyan 214.

 

Rabon watan Fabrairu ya kai naira biliyan 1.678, inda gwamnatin tarayya ta karbi naira biliyan 569.66, jihohi sun karbi naira biliyan 562.20, sannan kuma kananan hukumomi sun sami naira biliyan 410.56.

 

Kudaden shiga sun hada da naira biliyan 827.63 na kudaden shiga na doka da naira biliyan 609.43 daga VAT da naira biliyan 35.17 daga EMTL da naira biliyan 28.22 daga ma’adanai da karin naira biliyan 178.

 

A watan Maris, kwamitin ya raba naira tiriliyan 1.578. Gwamnatin tarayya ta karbi naira biliyan 528.70, jihohi sun karbi naira biliyan 530.45, sannan kuma kananan hukumomi sun karbi naira biliyan 387.

 

Kudaden shiga da aka rarraba sun hada da naira biliyan 931.33 a cikin kudaden shiga na doka da naira biliyan 593.75 daga harajin BAT da naira biliyan 24.97 daga EMTL, da naira biliyan 28.71 daga musayar kudade.

 

Kudaden shiga daga VAT a watan Janairun 2025 ya kai na naira biliyan 771.89, ya ragu zuwa naira biliyan 654.46 a watan Fabrairu da naira biliyan 637.62 a Maris. A halin yanzu, kudaden shiga na doka ya karu daga naira tiriliyan 1.848 a watan Janairu zuwa naira tiriliyan 1.653 a watan Fabrairu da naira tiriliyan 1.718 a watan Maris.

 

Duk da wadannan karin kudaden shiga, har yanzu kananan hukumomi ba su fara amsar kudadensu kai tsaye ba daga asusun tarayya, sabanin umarnin kotun koli da ta bayar a watan Yulin 2024.

 

Kotun koli ta ba da umarnin a biya kudaden kananan hukumomi daga asusun tarayya kai tsaye don tabbatar da ‘yancin cin gashin kansu na kudi da kuma kare su daga tsoma baki daga gwamnatocin jihohi.

 

Kungiyar kananan hukumomi ta Nijeriya (ALGON) ta zargi ofishin babban lauyan gwamnatin tarayya da kawo cikas ga aiwatar da ‘yancin cin gashin kai na kananan hukumomi, duk da cewa kotun koli ta yanke hukunci kan bayar da kudaden kai tsaye ga dukkan kananan hukumomi 774 da ke kasar nan.

 

ALGON ta kuma dauki matakin shari’a a kan babban lauyan gwamnatin tarayya da wasu cibiyoyin tarayya da dama a karar mai lamba ta FHC/ABJ/05/353/2025, suna nemanbai wa kananan hukumomi cikakken ‘yancin sarrafa kudadensu da kansu.

 

Karar ta kuma hada har ministan kudi, Wale Edun da ministan kasafin kudi da tsare-tsare na kasa, Abubakar Bagudu da akanta janar na tarayya da CBN da NNPCL da kuma bankunan kasuwanci a matsayin wadanda ake tuhuma.

 

ALGON ta ce ta dauki wannan matsayin a kotu ne da nufin ba kawai tilasta ‘yancin gashin kai a takarda ba har ma da tabbatar da aiwatar da shi.

 

Shari’ar wacce da farko aka shirya yi a gaban Mai Shari’a Inyang Ekwo, amma kotun ba ta samu zama ba. An dage shari’ar zuwa ranar 29 ga Mayu, 2025.

 

Da yake mayar da martani, Sakatare Janar na ALGON, Mohammed Abubakar, ya nuna takaicinsa kan ci gaba da jinkirin biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye duk da hukuncin kotun koli.

 

Abubakar ya ce lamarin ya zama mai rikitarwa kuma yawancin ‘yan Nijeriya sun yi takaicin faruwar hakan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: sun karbi naira biliyan naira tiriliyan 1 gwamnatin tarayya da naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Yau Jumma’a da safe, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan kasar Senegal Ousmane Sonko da shugaban kasar Ecuador Daniel Noboa a birnin Beijing, fadar milkin kasar Sin. Wadannan shugabannin biyu sun zo kasar Sin ne domin halartar taron dandalin tattaunawa kan tattalin arzikin duniya na lokacin zafi na Davos.

A yayin ganawarsa da Ousmane Sonko, Xi Jinping ya ce, kasar Sin tana son zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Senegal, tare da aiwatar da “Manyan matakai 10 bisa hadin gwiwar abokantaka” yadda ya kamata, da kuma kaddamar da karin ayyukan tallafawa al’umma, tare da sa kaimi ga kamfanonin kasar Sin su zuba jari a kasar Senegal domin raya sabbin makamashi, da gina ababen more rayuwa na zamani da dai sauransu, ta yadda Sin da Senegal za su kasance abokan juna dake hadin gwiwa da cimma moriyar juna.

A nasa bangare kuma, Ousmane Sonko ya ce, kasar Senegal da kasar Sin mambobin kasashe masu tasowa ne dake da buri iri daya, kuma kasar Segenal tana son yin mu’amala da kasar Sin kan harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya, tana kuma tsayawa tsayin daka wajen karfafa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare da kasar Sin, domin inganta yanayin adalci na duniya, tare da kiyaye moriyar kasashe masu tasowa.

Ban da haka kuma, bayan ganawar shugaba Xi Jinping da shugaban kasar Ecuador Daniel Noboa, an kulla shirin “Hadin gwiwa tsakanin gwamantin Jamhuriyyar Jama’ar kasar Sin da gwamantin Jamhuriyar kasar Ecuador, wajen inganta shawarar ‘Ziri daya da hanya daya’”. (Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
  • 2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya
  • NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 
  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
  • NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?
  • An tallafawa iyalan ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • An tallafawa iyalan jami’an ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno
  • Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
  • DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?
  • Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027