Gwamnatin jihar ta ce, matakin na daya daga cikin kokarin gwamnati mai ci na inganta ayyukanta domin samar da romon dimokuraɗiyya ga al’ummar jihar Sokoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kaduna Za Ta Mayarda Yara 200,000 Zuwa Makaranta 

 

A wani yunkuri na rage adadin yara da suka daina zuwa makaranta, Gwamnatin Jihar Kaduna ta kaddamar da shiri mayarda yara 200,000 zuwa makaranta a cikin shekaru hudu masu zuwa, karkashin shirin Reaching Out-of-School Children (ROOSC).

 

An bayyana wannan shiri ne a wani taron bita na kwanaki biyu da aka shirya tare da haɗin gwiwar Save the Children.

 

A cewar, wakilin Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Salisu Baba Lawal shirin zai shafi dukkan ƙananan hukumomi 23 a faɗin jihar.

 

“Wannan shiri na Gwamnatin Jihar Kaduna ne tare da haɗin gwiwar abokan ci gaba da masu aiwatar da ayyuka,” in ji shi.

 

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta samo lamunin tallafin kudi domin aiwatar da wannan shiri da nufin maganin matsalar yara da suka bar makaranta a faɗin jihar,” ya ƙara da cewa.

 

“Zuwo yanzu, an riga an horar da malamai 405, an gina sabbin makarantu 102, sannan ana ci gaba da gyara wasu makarantu 170.

 

Shirin yana ƙarfafa rajistar yara a makaranta da inganta koyarwa da samar da ingantaccen yanayi na koyo da koyarwa.”

 

Save the Children International da UNICEF su ne manyan abokan hulɗar wannan shiri, kuma yana samun goyon bayan kai tsaye daga Gwamna Uba Sani.

 

Save the Children ta raba kayan aiki da horar da malamai a karkashin shirin Reaching Out-of-School Children na Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Ma’aikatar Ilimi.

 

Shirin ROOSC yana mai da hankali kan ɗorewa, daidaito tsakanin jinsi, da kuma tallafawa marasa galihu, domin tabbatar da damar samun ingantacciyar ilimin firamare ga yara, matasa, da samari a fadin Jihar Kaduna.

 

Save the Children da UNICEF sun samu wakilci daga gwamnatin jihar ta hannun Ma’aikatar Ilimi don inganta tsarin koyarwa (Save the Children) da kuma ƙarfafa tsarin ilimi gaba ɗaya (UNICEF).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 
  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Mayarda Yara 200,000 Zuwa Makaranta 
  • Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB
  • Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21
  • Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
  • Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151
  • Mutanen da suka rasu a ambaliyyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi