Leadership News Hausa:
2025-09-18@08:25:41 GMT

Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya

Published: 26th, April 2025 GMT

Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya

Gwamnan ya bayyana cewa ba za a yi amfani da kudin al’umma ba ga mutanen da ba za su iya kula da mahajjata yadda ya kamata ba.

 

Gwamna Radda ya kara da cewa ya yi taro da shugabannin kananan hukumomi guda 34 domin tabbatar da cewa malaman da suka cancanta ne kadai aka zaba a matsayin masu koyarwa a ayyukan aikin hajjin bana.

 

Ya kuma yi alkawarin kafa kwamitin yada labarai domin yada ayyukan aikin hajjin tare da ba da kulawa ta musaman kan shawarwarin da aka bayar kan rahoton da kwamitin aiki hajjin ya gabatar.

 

Da yake gabatar da rahoton, tsohon mataimakin gwamnan Jihar Katsina kuma Amirul Hajj, Alhaji Tukur, ya bayyana wasu muhimman batutuwa da ke bukatar kulawa.

 

Ya kuma bayyana bukatar tallafa wa hukumar kula jin dadin alhazai wurin tantance malamai. Yana mai cewa mafi yawancin shugabannin kananan hukumomi sun sanya malaman da ba su da kwarewar yadda za su koyar da mahajjatan.

 

Amirul Hajja ya nuna damuwarsa bisa yadda ake samu wadanda ba ‘yan Nijeriya ba a cikin mahajjatan jihar tare da ba da shawarar inganta hanyoyin da ake bi wurin tantance mahajjatan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi

Mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mani Malam Mumini ya jajanta wa al’ummar karamar hukumar Gumi kan mumunan al’amuran da suka salwantar da rayukan mazauna kauyen Fas su 19 a makonnin da suka gabata.

 

Malam Mumini ya bayyana haka ne a lokacin da ya jagoranci wasu jami’an gwamnati da suka kai ziyarar jaje ga al’umma, inda ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da Majalisar Masarautar, da daukacin al’ummar Gumi.

 

Ya bayyana bala’in a matsayin mai raɗaɗi, yana mai jaddada cewa, gwamnatin jihar ta himmatu wajen magance matsalolin.

 

Mataimakin Gwamnan ya tuna cewa lamarin na farko ya faru ne a lokacin da mazauna kauyen cikin firgici kan harin da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka kai, suka shiga cikin wani jirgin ruwa wanda a karshe ya kife sakamakon kifewar da ya yi, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dama.

 

Ya kuma bayyana cewa, a yayin da bala’i na biyu ya faru kwanaki bayan wata motar bus ta Homa dauke da ‘yan  daurin aure ta kutsa cikin kogin Gwalli a kan hanyar da ta wuce kan gada mai dauke da yashi, inda mutane 19 suka mutu.

 

Ya yi nuni da cewa, duk da cewa dan majalisar da ke wakiltar yankin ya gabatar da kudiri a kan munin yanayin gadar, amma har yanzu ana duba lamarin a lokacin da bala’in ya afku.

 

Mani Malam Mumini ya ce tuni gwamnatin jihar ta aike da tawagar injiniyoyi domin tantance gadar da kuma hanyoyin da suka hada da juna.

 

Wani shugaban al’umma a Gwalli ya yi kira da a kawo dauki cikin gaggawa tare da jaddada muhimman dabarun hana gadar ta ruguje nan gaba.

 

Shima da yake nasa jawabin mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Zamfara, Adamu Aliyu Gumi, ya bayyana wannan lamari a matsayin babban rashi ga al’umma, ya kuma yi kira da a gaggauta daukar mataki na gaggawa domin kaucewa afkuwar bala’o’i.

 

A yayin ziyarar, Mataimakin Gwamnan ya kuma kai gaisuwar ban girma ga Mai Martaba Sarkin Gumi, Mai Shari’a Lawal Hassan mai murabus, tare da jajanta masa bisa wannan al’amarin da aka samu.

 

A nasa jawabi, mai martaba Sarkin Gumi, Mai Shari’a Lawal Hassan ya bukaci gwamnatin jihar da ta hada kai da hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA domin samar wa majalisar jiragen ruwa na zamani domin rage yawaitar hadurran jiragen ruwa.

 

Mai shari’a Hassan ya koka da cewa, kwalekwalen katako na gargajiya da ake amfani da su a halin yanzu ba su da tsaro kuma suna tabarbarewa cikin sauri, suna jefa rayuka cikin hadari.

 

Sarkin ya kuma yabawa gwamnatin jihar bisa kudurin da ta dauka na magance matsalar rashin tsaro da kuma kalubalen da ke addabar jihar.

 

Tun da farko, shugaban karamar hukumar Gumi, Aminu Nuhu Falale, ya kuma bukaci a kara kaimi wajen samar da tsaro musamman a yankin Birnin Magaji, saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga.

 

Ya bayyana cewa, hatsarin kwale-kwale na karshe ya samo asali ne sakamakon firgici yayin da mutanen kauyen suka yi yunkurin tserewa daga hannun ‘yan bindiga, lamarin da ya kai ga kifewar kwale-kwalen.

 

COV/AMINU DALHATU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Zamfara Ta Nemi Karin Tallafi Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar