Leadership News Hausa:
2025-06-14@22:57:54 GMT

Sarkin Daura Zai Karrama Ja’o’ji Da Wasu Samarin Arewa

Published: 27th, April 2025 GMT

Sarkin Daura Zai Karrama Ja’o’ji Da Wasu Samarin Arewa

Sun ƙara da cewa, “Samun shugabannin matasa masu jajircewa a wannan yankin babbar albarka ce ga al’ummarmu.

“Hakan na nuna mana cewa akwai kyakkyawar makoma ta ci gaba a Arewa gaba ɗaya.”

Sannan sun bayyana cewa sun aike wa ƙungiyoyinsu a dukkanin jihohi 19 na Arewa goron gayyata domin naɗin sabbin muƙamai a Masarautar Daura.

“Za a gudanar da babban taron karramawa wanda ba a taɓa ganin irinsa ba a nan kusa, domin naɗin sabbin muƙamai da Masarautar Daura za ta yi.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gammayar Ƙungiyoyi Sarkin Daura

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa

Yayin da damina ke ƙara ƙaratowa, Gwamnatin Jihar Kano, ta fara wani aikin tsaftace manyan magudanan ruwa domin daƙile aukuwar ambaliyar ruwa.

An fara aikin ne a yankin shataletalen Baban Gwari, ɗaya daga cikin wuraren da ambaliya ke yawan aukuwa a Birnin Kano.

Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya

Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ce ke jagorantar aikin tsaftace magudanan ruwan.

Wannan mataki na daga cikin shirin gwamnatin jihar na kare rayuka, dukiyoyi, da kuma inganta ababen more rayuwa.

A lokacin ƙaddamar da aikin, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Hashim Muhammad Dahiru, ya bayyana cewa an zaɓi Baban Gwari saboda muhimmancinsa da kuma yadda wajen yake a lokacin damina.

Ya ce wajen ya daɗe da zama wajen zubar da shara barkatai da kuma toshe hanyoyin ruwa.

Ya ƙara da cewa wannan wajen ba wai kawai muhimmiyar mahaɗa ba ce, amma kuma yana ɗaya daga cikin manyan hanyoyin ruwa da ke da alaƙa da ruwan Jakara da Kwarin Gogau.

Kwamishinan ya bayyana cewa mazauna yankin da masu wucewa sun sha fuskantar ambaliya da ta shafi rayuwarsu, lafiyarsu da kuma zirga-zirgarsu.

Ya ce wannan aikin ba na al’ada ba ce, illa alama ce da ke nuna cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin kare muhalli da kuma samar da birni mai jure sauyin yanayi da ambaliya.

Ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jagoranci da goyon bayan da ya bai wa ma’aikatar wajen aiwatar da wannan aiki.

Ya ce gwamnatin ta amince da sanya tsaftace magudanan ruwa a matsayin aikin da za a riƙa gudanarwa a kowace shekara domin tabbatar da tsaftar hanyoyin ruwa a faɗin jihar.

Haka kuma, gwamnatin ta bayar da kwangilar gyaran shataletalen Baban Gwari domin inganta zirga-zirga da rage yawan ambaliya, ta hanyar gina sabbin hanyoyin ruwa.

Kwamishinan ya bayyana cewa waɗannan matakai suna nuna irin hangen nesa da damuwar gwamnan jihar kan lafiyar jama’a da kuma kare su daga illolin da ke zuwa da ambaliya da sauyin yanayi.

Ya buƙaci jama’a da su daina zubar da shara barkatai, musamman a cikin magudanan ruwa, ya kuma buƙaci su riƙa ɗaukar nauyin tsaftace muhallinsu.

Ya ce gwamnatin za ta yi nata aikin, amma ana buƙatar haɗin gwiwar kowa da kowa domin a cimma nasara.

Ya kuma buƙaci ma’aikata da abokan aikin muhalli da su gudanar da aikinsu da kulawa da gaskiya, yana mai cewa aikin ba wai tsaftace magudanan ruwa ba ne kawai, amma aikin ne na kare rayuka, daƙile haɗura da kuma gina sabuwar Kano mai tsafta da lafiya.

A ’yan shekarun nan, yankin Baban Gwari ya yi ƙaurin suna wajen yawan aukuwar ambaliya, har ma da rasa rayuka da dukiyoyi.

Wannan ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa domin magance matsalar kafin saukar daminar bana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas
  • Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike