Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
Published: 29th, April 2025 GMT
Allah Ya yi wa Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Muslunci a Najeriya, Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah, rasuwa.
Babban Mufti na ƙasar Yarbawa, Sheikh Daood Imran Molaasan, ne ya sanar da rasuwar Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah a cikin wata sanarwa da ya sanya hannu a kai a daren Litinin.
Sai dai bai bayar da cikakken bayani game da inda Sheikh Hadiyatullah ya rasu ko kuma lokacin da hakan ya faru ba.
Sheikh Molaasan ya bayyana cewa rasuwar marigayi Sheikh Hadiyatullah ta bar giɓi mai wuyar cikewa a shugabancin Musulunci na ƙasar.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya“An haife shi a garin Iwo a Jihar Osun kuma an san shi da dabi’u Musulunci. Sheikh Hadiyatullah ya kasance fitaccen malamin Musulunci kuma masanin shari’a, wanda an san shi da ƙoƙarinsa na neman a aiwatar da Shari’a Musulunci a tsarin mulkin Najeriya, tattaunawa tsakanin addinai, da zaman lafiya a tsakanin al’ummomin Najeriya masu bambancin addini.
“Ya yi aiki a matsayin Shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci na tsawon shekaru, inda ya jagorance ta a lokutan ƙalubalen zamantakewa da ci gaba.
“Sheikh Hadiyatullah ya fara karatun addinin Musulunci a wurin malaman gida kafin ya ci gaba da karatunsa a ƙasashen waje.
“Ya samu girmamawa a faɗin Najeriya da ma wajenta saboda zurfin ilminsa a fannin fiƙihun Musulunci da kuma salon shugabancinsa mai nutsuwa da tsayin daka kan akida,” kamar yadda Molaasan ya bayyana.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta wa Sheikh Hadiyatullah ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Shari ar Muslunci Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah Sheikh Hadiyatullah Sheikh Hadiyatullah ya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo
A ranar Asabar ne Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Rome na ƙasar Italiya bisa gayyatar da sabon Fafaroma Leo XIV ya aike masa.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya sanar da cewa, shugaba Tinubu zai yi bulaguron ne tare da manyan jagororin ɗariƙar Katolika na Najeriya domin halartar bikin rantsar da sabon fafaroman wanda shi ne na 267.
Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro An kama wasu da haramtattun buhunan takin zamani 20 a BornoA cewar Onanuga, Cardinal Pietro Parolin ya aike da goron gayyata daga Fafaroma Leo XIV, wanda ya ce bikin ya nuna “wani lokaci mai muhimmanci ga mabiyan Cocin Katolika da kuma duniya da ke fama da tashe-tashen hankula da rikice-rikice da dama”.
Fadar shugaban ƙasar ta ce cikin takardar gayyatar sabon fafaroman ya bayyana alaƙar ƙashin kai da Najeriya, yana mai cewa ”ƙasarka mai girma na da mutuƙar muhimmanci a gareni, saboda na yi aiki a majami’ar Apostolic Nunciature da ke birnin Lagos a shekarun 1980”.
A cewar sanarwar, tawagar ta shugaba Tinubu za ta haɗa da Minista a harkokin waje, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu; Archbishop Lucius Ugorji na Owerri da kuma shugaban rukunin Bishop na Katolika na Najeriya; Archbishop Ignatius Kaigama na Abuja; da Alfred Martins na Legas; da kuma Bishop ɗin Katolika na Diocese na Sokoto, Mathew Hassan Kukah.
Fafaroma Leo XIV, tsohon Cardinal Robert Francis Prevost, za a rantsar da shi a matsayin Fafaroma a ranar Lahadi, 18 ga Mayu, a dandalin St Peter’s da ke Vatican.
Fafaroma Leo, wanda shi ne Fafaroma na farko daga Amurka an zaɓe shi ne kwanaki 17 bayan mutuwar magabacinsa, Fafaroma Francis, a ranar 21 ga Afrilu. Shi ne zai jagoranci Katolika biliyan 1.4 na duniya.
Ana sa ran shugaba Tinubu zai koma Abuja ranar Talata, 20 ga watan Mayu, in ji sanarwar