Kasashen Duniya Sun Yi Ta AiIka Tallafi Bayan Fashewar Bandar Abbas
Published: 27th, April 2025 GMT
Ana kara samun karin ta’aziyya da kuma tallafa daga kasashen waje bayan fashewar da ta auku a tasahr jiragen ruwa na Dr Rajai a Bandar Abbasa.
Tashar talabijin ta Press Tv ta nakalto ministan harkokin cikin gida Eskandar mumunina yana fadar haka, yana kuma cewa ya zuwa yanzu, mutane 14 aka tabbatar da mutuwarsu a yaynda wasu a yayinda wasu tsakanin 700-750 suka ji rauni.
Tankar dakon mai ce ta yi binda a cikin tashar jiragen ruwan, a jiya, ammam ba’a san musabbin fashewar ba hanyanzu. Wuta ta kona tankar ta kuma tsallaka zuwa wasu kayaki kusa da wurin.
Sannan bindigan da tankar ta tayi ya watsa wutar zuwa wasu wurare daga nesa, ya fasa gilashan mutocin da suke gewaue, da wasu gine-gine.
Banda haka kasashe da dama sun yi tayin gabatar da duk wani taimako wanda gwamnatin Iran take bukata. Daga Mosco.
Firay ministan kasar Indiya Narendra Mudi ya taya Iran bakin cikin abinda ya faru, sannan yace kasar Indiya ashieye take don gabatar da tallafi.
Sauran kasashen da suka gabatar da ta’aziyya akwai Japan, Qatar Pakisatn da sauransu, da kuma, Ammar hakim na kasar Iraki, duk sun yi wa shugaba Pezeskiyan jajen abinda ya faru tare da tayin bada tallafi idan ta bukaci haka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘YanSandan Jihar Kwara Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kwara ta ceto mutane uku da aka yi garkuwa da su ba tare da wata illa ba, a kauyen Igbonla.
A cikin wata sanarwa da Jami’ar Hulɗa da Jama’a ta rundunar, SP Adetoun Ejinre-Adeyemi, ta fitar, ta ce rundunar ta samu kiran gaggawa cewa wasu ’yan bindiga sun kutsa cikin wani gida, suna harbi a sama, sannan suka tafi da wasu daga cikin mazauna gidan.
Daga nan ne rundunar ’yan sanda tare da ’yan banga da masu farauta suka isa yankin cikin gaggawa, lamarin da ya kai ga ceto sun hada da Fatima Wasiu da Kudus Wasiu da jaririya mai watanni shida, ba tare da jin rauni ba.
Sai dai har yanzu ana ci gaba da nemo sauran mutane biyu da aka yi garkuwa da su, wato Wasiu Salihu da Abdullahi Sefiu, kuma ana ci gaba da farautar wadanda suka aikata laifin.
Rundunar ta bukaci jama’a da su ci gaba da ba da bayanai cikin lokaci, domin sauƙaƙa aikin tabbatar da tsaro a jihar.
Ali Muhammad Rabiu/Kwara