Kasashen Duniya Sun Yi Ta AiIka Tallafi Bayan Fashewar Bandar Abbas
Published: 27th, April 2025 GMT
Ana kara samun karin ta’aziyya da kuma tallafa daga kasashen waje bayan fashewar da ta auku a tasahr jiragen ruwa na Dr Rajai a Bandar Abbasa.
Tashar talabijin ta Press Tv ta nakalto ministan harkokin cikin gida Eskandar mumunina yana fadar haka, yana kuma cewa ya zuwa yanzu, mutane 14 aka tabbatar da mutuwarsu a yaynda wasu a yayinda wasu tsakanin 700-750 suka ji rauni.
Tankar dakon mai ce ta yi binda a cikin tashar jiragen ruwan, a jiya, ammam ba’a san musabbin fashewar ba hanyanzu. Wuta ta kona tankar ta kuma tsallaka zuwa wasu kayaki kusa da wurin.
Sannan bindigan da tankar ta tayi ya watsa wutar zuwa wasu wurare daga nesa, ya fasa gilashan mutocin da suke gewaue, da wasu gine-gine.
Banda haka kasashe da dama sun yi tayin gabatar da duk wani taimako wanda gwamnatin Iran take bukata. Daga Mosco.
Firay ministan kasar Indiya Narendra Mudi ya taya Iran bakin cikin abinda ya faru, sannan yace kasar Indiya ashieye take don gabatar da tallafi.
Sauran kasashen da suka gabatar da ta’aziyya akwai Japan, Qatar Pakisatn da sauransu, da kuma, Ammar hakim na kasar Iraki, duk sun yi wa shugaba Pezeskiyan jajen abinda ya faru tare da tayin bada tallafi idan ta bukaci haka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara
Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwo na Gargajiya ta Afirka (CORET) tare da haɗin gwiwar ECOWAS sun hada matasan da aka horar da su da manyan abokan holda don bunkasa kiyo da bunkasa yawan madara a jihohin Kaduna da Jigawa.
A yayin zaman karawa juna sani a Kaduna, Koodinetan Aikin na CORET Dr. Umar Ardo Abdul, ya ce an shirya wannan zama ne domin haɗa matasan da aka horar da su da masu ruwa da tsaki a harkan kiyo da bunkasa yawan madara na gwamnati da masu zaman kansu, domin a horas da su hanyoyin samun aikin yi da kuma bunkasa yawan madara.
Wannan shiri na daga cikin Aikin ECOWAS na karfafa samar da ayyukan yi ga matasa da kuma bunkasa darajar madara, wanda yake ɗaukar tsawon shekaru uku, kuma an kaddamar da shi ne domin koya wa matasa ƙwarewar aiki tare da samar musu damar samun kuɗin shiga a cikin fannin kiwo.
Koodinetan Aikin, Dr. Umar Ardo Abdul, ya bayyana cewa an yi wa matasa 1,350 rajista a Kaduna da Jigawa.
A cewarsa, matasa 26 daga jihohin Kaduna da Jigawa yanzu an haɗa su da masana waɗanda za su tallafa musu a ayyukan yin allurar rigakafi da taimakon lafiyar dabbobi da aikin yaɗa ilimi, da kuma samar da kayan kiwo.
Ya yi bayani cewa zaman ya haɗa kwararrun likitocin dabbobi, ma’aikatan yaɗa ilimin kiwo, masu yin dasa ramin maniyyi da masu sarrafa abincin dabbobi da sauran masu ruwa da tsaki a kiwo domin gina ƙaƙƙarfan cibiyar ayyuka.
Dr. Umar Ardo ya ce manufar ita ce a tabbatar matasan sun yi amfani da ƙwarewar da suka samu wajen ba da muhimman ayyukan kiwo, samun kuɗin shiga, da kuma tallafawa makiyaya da manoma a yankunansu.
Yace ma’aikatar aikin gona ta Jihar Kaduna da Cibiyar Binciken Samar da Dabbobi ta Ƙasa (NAPRI) a matsayin muhimman abokan aikin gwamnati, yana mai cewa NAPRI cibiyar bincike ce da a ke dogaro da ita wajen binciken kiwo, samar da rigakafin dabbobi da kuma kayayyakin kiwo.
Koodinetan ya ce gwamnati na da muhimmiyar rawa ta tsare-tsare a fannin kiwon lafiya na dabbobi, rigakafi da kuma samar da kaji, yayin da kamfanonin masu zaman kansu ke taka rawa wajen samar da magungunan dabbobi da kayan kiwo, waɗanda suka zama ginshiƙai ga masu cin gajiyar shirin.
Dr. Umar Ardo ya jaddada cewa CORET, a matsayinta na ƙungiyar haɗin kan masu kiwo ta nahiyar Afirka, ta kuduri aniyar cike gibin da ke tsakanin hukumomin gwamnati, cibiyoyin bincike, kamfanoni masu zaman kansu da matasan da aka horar domin inganta harkar kiwo da bunkasa madara.
A nasa jawabin, wakilin Hukumar Ilimin Makiyaya ta Ƙasa, Abubakar Lawal Boro, ya ce tsarin PPP (Haɗin Gwiwar Gwamnati da Masu Zaman Kansu) shi ne ginshiƙin cigaban kiwo mai ɗorewa, domin gwamnati na samar da tsarin aiki da jagoranci, yayin da kamfanoni ke samar da muhimman kayayyaki.
Ya yi kira ga iyalan makiyaya su bai wa ilimi muhimmanci ta hanyar mayar da ‘ya’yansu makaranta, yana nuna damuwa kan yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta da tasirin rashin tsaro ga yunkurin wayar da kai.
Ɗaya daga cikin mahalarta, Anas Ibrahim, ya bayyana wannan horo a matsayin mai matuƙar amfani kuma ya zo a kan lokaci.
Ya ce zaman ya kasance cikin tsari kuma yana ɗaya daga cikin mafi inganci da suka halarta, inda ya faɗaɗa musu fahimtar lafiyar dabbobi, kula da abincin kiwo, da hulɗa da masu samar da ayyukan kiwo.
Wani mahalarta kuma, Rabiu Adamu daga Ladugga, ya yaba wa CORET da abokan aikinta bisa samar da dandalin da ya bai wa masu kiwo damar samun damar magungunan dabbobi masu inganci, abincin kiwo, da iri na kiwo da za su inganta kiwon madara.
COV: Adamu Yusuf