Mista Fall ya jagoranci tawagar Majalisar Dinkin Duniya da ta kunshi wakilai daga UNICEF, UNESCO, UNDP, UNFPA, da mata na Majalisar Dinkin Duniya a wajen taron. Ya jaddada cewa canjin al’umma ya ta’allaka ne akan jarin dan’Adam musamman ta hanyar ilmantar da ‘ya’ya mata da karfafa wa mata.

 

Ya kara da cewa, “tare da gwamnati da abokan huldarmu, mun himmatu wajen kawar da duk wani cikas da ke hana yara, musamman ma masu rauni damar samun ilimi”.

 

Fall ya gano muhimman abubuwan da ke kawo cikas ga ilimi a Nijeriya, da suka hada da rashin tsaro, tabarbarewar tattalin arziki, sauyin yanayi, da kuma ka’idojin zamantakewa da al’adu. Ya yi kira da a kara himma wajen inganta daidaiton jinsi da karfafa hadin kan al’umma a matsayin muhimman hanyoyin samun ci gaba mai dorewa.

 

Malala, wacce ta isa Abuja a ranar 26 ga watan Satumba don taron shekara na Hukumar Kula da Malala Fund, ta nanata rawar da Nijeriya ke takawa a dabarun duniya na Malala Fund na 2025 zuwa 2030.

 

“Nijeriya kasa ce mai fifiko ga Malala Fund, tun daga shekarar 2014, mun zuba jarin sama da dala miliyan 8 ga kungiyoyin hadin gwiwa na Nijeriya da ke kokarin dakile hana yara mata zuwa makaranta,” in ji ta.

 

Ta zayyana dabaru na Malala Fund a Nijeriya, wadanda suka hada da: tabbatar da cewa ‘yan mata masu aure da masu juna biyu za su iya komawa makaranta; habaka tallafin ilimi da tabbatar da biyan bukatun ‘yan mata; da kuma amfani da ilimi a matsayin hanyar warware matsalar auren yara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka

Wasu masu ibadar Umara 42 sun mutu bayan da motarsu ta yi taho-mu-gama da wata tankar mai a kusa da birnin Madina da ke kasar Saudiyya.

Dukkan masu ibadar ’yan kasar Indiya ne, kuma hatsarin ya ritsa da su ne a kan hanyarsu ta zuwa Makka bayan kammala ziyara a birnin Madina.

Ministan harkokin wajen Indiya Dakta S. Jaishankar ya bayyana cewa mutum daya daga cikin fasinjojin ya tsallake rijiya da baya a hatsarin da ya auku da tsakar daren Litinin.

Hatsarin ya auku ne a bayan da motar safa mai daukar mutum 43 da masu ibadar suke ciki ta yi karo gaba-da-gaba da wata tankar mai.

’Yan ta’adda sun sace dalibai 25 a dakunan kwanansu a Kebbi NELFUND ya raba wa ɗalibai tallafin karatu na Naira Biliyan 116 

A sakon ta’azaiyyarsa ga iyalan mamatan, Ministan harkokin wajen Indiya, ya bayyaan cewa ofisoshin jakadancin kasar ke Saudiyya, na bayar da cikakken tallafi ga masu Umarar da hatsarin ya rusta da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas
  • Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi
  • Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
  • Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16
  • A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
  • Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika
  • Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola