Amurka Ta Yi Barazana Ga Ukraine A Dai-dai Lokacinda Ta Fitar Da Shirin Zaman Lafiya Da Rasha Na Karshe
Published: 25th, April 2025 GMT
Gwamnatin kasar Amurka ta gargadi kasar Ukraine a dai dai lokacinda ta gabatar da shirin zaman lafiya da kasar Rasha na karshe.
Shirin da shugaban kasar Donal Trump ya bayyana shi ne karshe dai, ya bukaci gwamnatin shugaba Volodimir Zelesky ta amince da yankin Cremea da kuma sauran yankunan hudu wadanda Rasha ta mamaye da karfi shekaru uku da suka gabata su zama mallakin kasar Rasha har’ abada.
Shawara bata yi maganar wani abu banada wadannan hudu ba, duk da cewa Ukraine tana da wasu bukatu a yarjeniyar tsagaita wuta da kuma samar da sulhu mai dorewa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa Moscow ta bukaci a tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu don samun damar tattaunawa amma gwamnatin Kiev ta ki amincewa.
Masana suna ganin wadannan al-amura suna da nauyi ga kasar ta Ukraine, amma kuma bata da zabi tunda Amurka ce ta biya mafi yawan kudaden da Ukraine ta kashe a yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Kasar Lebanon Ya Ce Kungiyar Hizbullah Bata Da Zabi Sai Abinda Gwamnati Ta fada
Shugaban kasar Lebanon Josept Aoun ya bayyana cewa gwamnatinsa tana son ta maida makamai a kasar Lebanon karkashin ikon hukuma kadai. Aoun ya ce kungiyar Hizbullah tana iya shiga harkokin siyasa na kasar Lebanon amma makamai na gwamnatin ne kadai.
Jaridar ‘The National Ta Kasar Amurka’ ta n akalto shugaban yana fadar haka a kasar Masar a ganawarsa da tokwaransa na lasar Abdulfattah Assisi a yau Litinin.
Aoun ya kara da cewa yana bukatar taimakon kasar Masar don gano ramukan da ake boye makamai a kasa. Sannan zai yi magana da shugaba Mahmood Abbas na Falasdinawa kan yadda za’a karbe makaman da suke hannun falasdinawa a sansanoninsu na yan gudun hijira da ke Ainul Helwa kusa da garin Saida na kudancin kasar Lebanon.
Da aka tambaye shi dangane da yankunan kasar Lebanon wadanda har yanzun HKI na mamayeda su da fursinonin kasar Lebanon da ke hannun HKI, Aoun ya ce yana magana da Amurkawa, don ita kadai ce za su takurawa HKI ta fice daga kasar Lebanon ta kuma saki yan kasar wadanda suke hannun HKI.
Kafin haka dai kungiyar Hizbullah ta bayyana cewa ba zata taba rabuwa da makamakanta sai randa babu wata kasa Isra’ila a yankin.