Gwamnatin kasar Amurka ta gargadi kasar Ukraine a dai dai lokacinda ta gabatar da shirin zaman lafiya da kasar Rasha na karshe.

Shirin da shugaban kasar Donal Trump ya bayyana shi ne karshe dai, ya bukaci gwamnatin shugaba Volodimir Zelesky ta amince da yankin Cremea da kuma sauran yankunan hudu wadanda Rasha ta mamaye da karfi shekaru uku da suka gabata su zama mallakin kasar Rasha har’ abada.

Sannan ta amince a daukewa kasar Rasha takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata tun bayan fara yakin. Sannan daga karshe ta amince ba zata shiga kungiyar tsaro ta NATO ba.

Shawara bata yi maganar wani abu banada wadannan hudu ba, duk da cewa Ukraine tana da wasu bukatu a yarjeniyar tsagaita wuta da kuma samar da sulhu mai dorewa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa Moscow ta bukaci a tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu don samun damar tattaunawa amma gwamnatin Kiev ta ki amincewa.

Masana suna ganin wadannan al-amura suna da nauyi ga kasar ta Ukraine, amma kuma bata da zabi tunda Amurka ce ta biya mafi yawan kudaden da Ukraine ta kashe a yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Roki Amurka Ta Taimake Ta A Fada Da Kasar Yemen

Tashar talabijin din “Cane” ta HKI ta bukaci Amurka da ta kafa kawance mai fadi na kasashe domin fuskantar kasar Yemen.

A yayin ziyarar da Fira ministan HKI, Benjamin Netanyahu a Amurka ne dai ya bijiro da wannan bukatar, kamar yadda rahoton tashar talabijin din ta “Cane” ya ambata.

 Rahoton ya kuma ce, Jami’an HKI sun sanar da Amurka cewa, ci gaba da hare-haren Yemen, ya tashi daga zama matsalarta ita kadai, don haka da akwai bukatar kai hare-hare na hadin gwiwa da Amurka da kuma shigar da kasashen wannan yankin da kuma wasu na duniya.”

Tun daga 2023 ne sojojin Yemen suke kai wa jiragen ruwa na HKI hare-hare a cikin tekun “Red Sea” ko kuma wadanda su ka nufi tasoshinta na jirgin ruwa. Sojojin na Yemen dai sun sha bayyana cewa ba za su daina kai hare-haren ba har sai an kawo karshen yakin Gaza, da kuma dauke takunkuman da aka kakabawa yankin.

Shugaban kungiyar Ansarullah ta Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husi ya sha bayyana matsayar kasar ta Yemen yana mai cewa; Hare-haren nasu martani ne akan laifukan yakin da HKI take  yi a  Gaza, ba kuma za su daina ba, sai an dakatar da aikata wadannan laifukan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Roki Amurka Ta Taimake Ta A Fada Da Kasar Yemen
  • FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
  • An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Aref Ya Bayyana Cewa: Iran Ba Ta San Kalmar Mika Wuya Ba A Al’adunta Da Tsaronta
  • Aragchi: Kofar Iran Ta Tattaunawa A Bude Take, Amma Amurka Sai Ta Biya Kudade Kan Kura-Kuranta
  • Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
  • Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Amince Iran ta Kai Hare-Hare Kan cibiyoyin Sojojinta Guda Biyar
  • Kasar Yemen Ta Bayyana ‘Yancin Kowa Na Walwala A Teku Amma Ban Da ‘Yan Sahayoniyya Azzalumai