Jaridar BusinessDay tayi nazari kan manyan ayyuka biyar na Layukan Dogo da suka samar wani sauki, a zirga-zirgar Jirgin kasa a kasar nan.

1 Layin Dogo Daga Legas Zuwa Ibadan

Ingantaccen aikin layin Dogo mai tsawon kilomita 157 da ya taso daga jihar Legas zuwa garin Ibadan.

An faro aikin ne a watan Maris na 2017 aka kuma kaddamar da shi, a ranar 10 na watan Yununin 2021.

Aikin ya kasance mai tagwayen hanya biyu da ake da shi, Afrika ta Yamma.

An kammala aikin layin na Dogon ne, cikin shekaru hudu, wanda kuma aka kara fadada shi zuwa kimanin kilomita 7 domin ya hade da layin Dogo na tashar Jirgen Ruwa da ke Apapa.

Wannan layin Dogon, na bayar da gudunmawa wajen kara bunkasa hada-hadar kasuwancin yankunan da ke makwabtaka da wannan layi Dogon.

2. Layin Dogo Daga Abuja Zuwa Kaduna

Layin Dogo da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna, aiki ne, da aka yi da kaya aiki na zamani wanda kuma ya kai tsawon jimlar kilomita 186.5. Kzakila, an tsara aikin ne, yadda Jirgin kasa zai yi gudun da ya kai kilomita 150.

3. Jirgin kasa Mai Amfani Da Lantarki A Cikin Birinin Legas:

A wannan layin Jirgin kasan na na hada Legas da jihar Ogun wanda gwamnan jihar ta Ogun Dapo Abiodun, ya kara ware Naira tiriliyan daya a cikin kasarin kudi na 2025.

Kashi na farko na aikin, na da Tashoshi biyar kuma ya na yin zirga-zirgar da a ka ta tsawon kilomita 13, da aka bude a ranar 4 na watan Satumbar 2023.

Kazalika, babbar Layin Dogon, zai kasance mai tsawon kilomita 27, wanda ake sa ran a kullum zai yi jigilar fasinjoji 500,000.

4 Jirgin kasa Mai Amfani Da Lantarki A Cikin Birinin Tarayyar Abuja:

Kusan aikinsa ya kasance ne a cikin birnin Abuja, wanda kuma shi ne, Jirgin kasa na farko, mai gudu a kasar, kuma na biyu a Afirka ta Yamma.

Kashin aikin na farko, an kaddamar aikin ne a rana 12 na watan Yulin 2018 wanda zai hada tashar filin tashi da saukar Jigin sama ta Nnamdi Azikiwe, inda kuma zai tsaya a tashar Jirgin kasa da ta Idu da ta tashi daga Abuja zuwa Kaduna.

Aikin Jirgin kasa Na Fatakwal Zuwa Maiduguri:

Wannan aikin ya lashe dala biliyan 3.2 ana kuma sa ran zai hada Kudu da Arewa Maso Gabas tare da layukan rassan Owerri da Damaturu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nazari

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai

Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.

A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.

Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Yana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.

“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”

“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.

“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”

“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai