Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44
Published: 30th, July 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta ce ta kammala gyaran makarantu fiye da 1,200 a kananan hukumomi 44 na jihar a wani yunkuri na farfado da harkar ilimi.
Kwamishinan Ilimi na jihar, Dr. Ali Haruna Makoda, ne ya bayyana hakan yayin taron bitar yini guda kan kara kaimi a tsarin duba ingancin karatu, da aka gudanar a dakin taro na Cibiyar Kula da Ilimin Al’umma (CERC).
Ya ce banda gyaran manyan makarantu, gwamnatin ta ware Naira miliyan 484 domin gudanar da karin ayyukan gyare-gyare a gundumomi 484, inda kansilolin mazabu ke kula da gudanarwar ayyukan.
“A karo na farko a tarihin Kano ake aiwatar da manyan ayyukan ilimi a wannan mataki. Mun riga mun gyara makarantu sama da 1,200 kuma an fara ayyuka a matakin gundumomi.” In ji Dr. Makoda.
Kwamishinan ya kara da cewa wannan ci gaba yana cikin matakan aiwatar da dokar ta-baci da aka ayyana kan harkar ilimi a watan Mayun 2024, domin dawo da martabar fannin.
Ya ce gwamnatin ta kuma amince da Naira biliyan 3 domin gyaran makarantun kwana 13 na ’yan mata da gwamnatin da ta shude ta rufe.
Dr. Makoda ya bayyana cewa Kano na da fiye da makarantu 30,000, adadi mafi yawa a duk fadin Najeriya, kuma gwamnati na da niyyar ganin kowanne yaro ya samu ingantaccen ilimi cikin daidaito.
Taron ya horar da daraktoci, shugabannin makarantu da jami’an sa-ido, inda kwararru irin su Farfesa Ahmed Ilyasu da Bashir Sule suka gabatar da jawabai kan hanyoyin tantance darussa da dabarun inganta ilimi.
Daga Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
Kungyar Hamas ta bayyana cewa: Gmanatin mamayar Isra’ila ta ƙirƙiri ƙarya don kare kisan gillar da ta yi a Gaza
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta tabbatar da cewa: Zargin da kakakin rundunar sojin mamayar Isra’ila ya gabatar dangane da yin amfani da hasumiyai a birnin Gaza domin aikin soji ba komai ba ne illa karairayi na zahiri da suke nufin kare laifukan da ake aikatawa da kuma boye barnar da ake yi a birnin Gaza, kamar yadda a baya sojojin mamaya suka lalata garuruwan Rafah, Khan Younis, Jabaliya, Beit Hanoun, da Beit Lahiya.
A cikin wata sanarwa da kungiyar Hamas ta fitar ta bayyana cewa, zargin mamaya na cewa kungiyar Hamas na amfani da fararen hula a matsayin garkuwar dan adam tare da hana su ficewa daga Gaza, yaudara ce karara da ke nuna rashin mutunta ra’ayin al’ummar kasa da kasa tare da tabbatar da dagewar da take yi na ci gaba da kisan kiyashi kan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba da kuma raba su da muhallinsu da karfi da nufin korar su daga zirin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi: Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci