Aminiya:
2025-09-17@21:52:10 GMT

Hakeem Baba-Ahmed ya yi murabus daga gwamnatin Tinubu

Published: 4th, April 2025 GMT

Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya yi murabus daga matsayin mai bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin siyasa.

Majiyoyi daga fadar shugaban ƙasa sun tabbatar da cewa ya aike da takardar murabus ɗinsa kimanin makonni biyu da suka wuce, inda ya ce dalilansa na ƙashin kai ne.

Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — Wike NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta

Har yanzu ba a tabbatar da ko fadar shugaban ƙasa ta amince da murabus ɗin ba.

An naɗa Baba-Ahmed a watan Satumban 2023 a matsayin mai bai wa mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, shawara kan harkokin siyasa.

A lokacin da yake riƙe da muƙamin, ya wakilci gwamnati a taruka da dama na ƙasa da na siyasa.

Sai dai ya sha suka a shekarar 2024, bayan da ya samu saɓani da Ƙaramin Ministan Harkokin Tsaro, Bello Matawalle, kan kalaman da suka shafi Ƙungiyar Tsofaffin Shugabannin Arewa (NEF), inda ya taɓa zama kakakinta kafin naɗinsa.

“Sukar NEF da Matawalle ya yi bai dace ba. Ya fi dacewa ya bayyana irin gudunmawar da ministocin Arewa da sauran jami’an gwamnati irina ke bayarwa wajen inganta tsaro da rage talauci a yankin,” in ji Baba-Ahmed

Matawalle ya mayar da martani da cewa: “Dukkanin wanda Shugaba Tinubu ya naɗa, ciki har da Dokta Baba-Ahmed, na da alhakin kare da kuma tallata ayyukan wannan gwamnati a fannoni daban-daban.”

Baba-Ahmed wanda ya taɓa zama Shugaban Ma’aikata na tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, sananne ne wajen tsayawa kan gaskiya da adalci a harkokin ƙasa.

Kafin naɗin nasa, ya kasance Daraktan Yaɗa Labarai na ƙungiyar dattawan Arewa.

Tsohon babban jami’in gwamnati ne daga Jihar Kaduna kuma sananne ne a matsayin dattijo mai kishin Arewa.

Murabus ɗinsa ya jawo ce-ce-ku-ce musamman a tsakanin masu bibiyar al’amuran siyasa a Arewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin tinubu Murabus Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago