Aminiya:
2025-05-30@23:43:33 GMT

Hakeem Baba-Ahmed ya yi murabus daga gwamnatin Tinubu

Published: 4th, April 2025 GMT

Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya yi murabus daga matsayin mai bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin siyasa.

Majiyoyi daga fadar shugaban ƙasa sun tabbatar da cewa ya aike da takardar murabus ɗinsa kimanin makonni biyu da suka wuce, inda ya ce dalilansa na ƙashin kai ne.

Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — Wike NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta

Har yanzu ba a tabbatar da ko fadar shugaban ƙasa ta amince da murabus ɗin ba.

An naɗa Baba-Ahmed a watan Satumban 2023 a matsayin mai bai wa mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, shawara kan harkokin siyasa.

A lokacin da yake riƙe da muƙamin, ya wakilci gwamnati a taruka da dama na ƙasa da na siyasa.

Sai dai ya sha suka a shekarar 2024, bayan da ya samu saɓani da Ƙaramin Ministan Harkokin Tsaro, Bello Matawalle, kan kalaman da suka shafi Ƙungiyar Tsofaffin Shugabannin Arewa (NEF), inda ya taɓa zama kakakinta kafin naɗinsa.

“Sukar NEF da Matawalle ya yi bai dace ba. Ya fi dacewa ya bayyana irin gudunmawar da ministocin Arewa da sauran jami’an gwamnati irina ke bayarwa wajen inganta tsaro da rage talauci a yankin,” in ji Baba-Ahmed

Matawalle ya mayar da martani da cewa: “Dukkanin wanda Shugaba Tinubu ya naɗa, ciki har da Dokta Baba-Ahmed, na da alhakin kare da kuma tallata ayyukan wannan gwamnati a fannoni daban-daban.”

Baba-Ahmed wanda ya taɓa zama Shugaban Ma’aikata na tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, sananne ne wajen tsayawa kan gaskiya da adalci a harkokin ƙasa.

Kafin naɗin nasa, ya kasance Daraktan Yaɗa Labarai na ƙungiyar dattawan Arewa.

Tsohon babban jami’in gwamnati ne daga Jihar Kaduna kuma sananne ne a matsayin dattijo mai kishin Arewa.

Murabus ɗinsa ya jawo ce-ce-ku-ce musamman a tsakanin masu bibiyar al’amuran siyasa a Arewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin tinubu Murabus Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

OPEC+ Ta Fara Shirin Ayyana Yawan Man Fetur Da Zata Haka Zuwa Sekara Ta 2027

Kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kuma kawayenta a wajen kungiyar sun gudanar da taro a birnin Riyad na kasar Saudia inda suka tattauna kan yawan man fetur da zasu haka daga shekara da ta 2027.

Shafin yada labarai na tanar gizo na kasar Saudia Arab News ya bayyana cewa wannan yana daga cikin abinda kasashe suka amince a bayan kuma a halin yanzu kungiyar ta rika ta tsara yawan man da ko wace kasa zata haka daga shekara ta 2022 har zuwa shekara ta 2026.

Labarin ya kara da cewa kungiyar tana da tsare tsaren haka man fetur har guda uku biyu suna tafiya kamar yadda suka tsara a yayinda daya kuma sun warewa kasashe 8 daga cikinsu su aiwatar da shi. Wannan tsarin yana daga cikin tsare tsaren kungiyar na dogon zango.

A halin yanzu dai farshin man yana kan $60 a cikin watan Afrilun da ya gabata, Sannan shi ne farashi mafi karanci tun shekaru 4 da suka gabata, kuma sana diyyar kara kudaden fiton da Trump yayi farashin ya tashi zuwa $65 kan ko wace ganga.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23
  • Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
  • ’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna
  • Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
  • OPEC+ Ta Fara Shirin Ayyana Yawan Man Fetur Da Zata Haka Zuwa Sekara Ta 2027
  • Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
  • Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
  • Amurka za ta hana ‘’visa’’ ga daliban dake sukanta a shafukan sada zumunta
  • Tinubu ya ɗaga darajar Kwalejin Kimiyya  ta Kabo Zuwa Jami’ar Fasaha ta Tarayya