Kisan ma’aikatan ceto : MDD ta gargadi Isra’ila game da aikata laifin yaki
Published: 4th, April 2025 GMT
Kwamishinan kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya gargadi Isra’ila game da harin da ya yi sanadin mutuwar ma’aikatan ceto a Gaza yana mai cewa hakan zai iya kasancewa ‘lafin yaki’. Ma’aikatan agaji 15 ne suka ras arayukan a wani kazamin hari da Isra’ila ta kai kan motocin daukar marasa lafiya a Gaza wada ya fiddo a fili irin ” laifuffukan yaki da sojojin Isra’ila suka kwashe tsawon lokaci suna aikatawa a zirin Gaza”.
Kafin hakan dama hukumar kula da hakkin bil adama ta MDD ta amince da kudurin dake kira ga Isra’ila da kada ta aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.
An amince da kudurin ne ranar Laraba yayin taron hukumar na 58, bayan ya samu kuri’un amincewa 27 da na kin amincewa 4, kana kasashe 16 sun kaurace wa kada kuri’ar.
Kudurin ya kuma bayyana takaici game da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isra’ila ta yi, tare da yin kira da ta sauke nauyin dake wuyanta.
Har ila yau, kudurin ya soki yadda Isra’ila ta yi amfani da yunwa a matsayin wata dabara ta yaki a Gaza, da hana samar da agajin jin kai da kawo tsaiko ga samar da kayayyakin agaji da hana fararen hula abubuwan da suke bukata na rayuwa, kamar abinci da ruwa da lantarki da makamashi da hanyoyin sadarwa.
Ya kuma bayyana damuwa matuka game da kalaman jami’an Isra’ila da ka iya ingiza kisan kiyashi, inda ya bukaci Isra’ila ta sauke nauyin dake wuyanta bisa doka na kare aukuwar kisan kiyashi.
Bugu da kari, kudurin ya gabatar da wasu jerin bukatu ga Isra’ila, ciki har da tabbatar da samar da agajin jin kai ba tare da tangarda ba da gaggauta dawo da tsarin samar da muhimman kayayyakin bukata ga Palasdinawa a Gaza da ba Palasdinawan da suka rasa matsugunansu damar komawa dukkan yankunan zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Bugu da kari, akwai kuma masu kiwon Tarwada a gonar da sama da su 600, wadanda aka rage yawan adadinsu daga 1,327 zuwa 600, bayan bullar cutar annobar Korona, saboda kalubalen ci gaba da gudanar da sauran ayyukan gonar.
A shekarar 2024, masu kiwon Tarwadar a gonar; sun samar da Tarwadar da yawanta ya kai kimanin tan 1,700, wadda kuma aka kiyasata cewa; kudinta ya kai na Naira biliyan 4.5.
Wannan ba karamin ci gaba ba ne, musamman duba da cewa; gonar ta kasance abin koyi ga sauran kungiyoyin da ke kiwon Tarwada a daukacin fadin wannan kasa.
Bisa wannan nasarori da gonar ta samar, hakan ya nuna yadda take ci gaba da samun yabo daga kasashen duniya, cikin masu yabon har da Hukumar Bunkasa Samar da Abinci da Habaka Aikin Gona (FAO) da kuma wani yabon daga wurin sauran hukumomin kasa da kasa da ke tallafa wa fannin.
Ya zuwa yanzu, Hukumar ta FAO; ta wanzar da wani aiki na kiwon Kifi da ake kira da ‘FISH4ACP’, wanda kuma Tarayyar Turai (EU) da Gidauniyar Giz ke zuba kudade a cikin aikin, musamman domin tabatar da ganin an samar da damar samun kudade da taimakawa wajen gudanar da yin bincike a fannin.
Babban Jami’in gudanar da aikin ‘FISH4ACP’ da ke Hukumar ta FAO, Dakta Abubakar Usman ya bayyana cewa; an samu kyakkyawan sakamako a binciken da aka gudanar, wanda kuma har yanzu ake ci gaba da amfana da shi sakamakon binciken, musamman ganin cewa; bincken zai taimaka wajen rage kalubalen da ake fuskanta na tsadar abincin ciyar da Tarwadar zuwa sama da kashi 20 cikin 100.
Shi kuwa, babban shugaba a shirin nan na IDIPR, Marcus Adeniyi, a tattaunawar da aka yi da shi a gonar da ke kauyen Eriwe a Ijebu Ode, ya sanar da cewa, kungiyar ta masu kiwon Tarwadar; na kara tumbatsa ne matuka.
Ya sanar da cewa, duk yawan Tarwadar da aka sayar, ana tura kudaden cinikin ne kai tsaye zuwa ga asusun ajiyar kudade.
A cewar Adeniyi, Tarwadar da ake da ita a yanzu a gonar; ta kai ta kimanin Naira biliyan shida, inda ya kara da cewa; bisa bayanansu a zango farko na shekarar 2025, an sayar da Tarwada sama da tan 600.
“Idan har a shekarar 2024, mun samar da tan 1,700 na Tarwada, wadda kudinta ya kai kimanin Naira biliyan 4.5, a wannan shekarar ta 2025, muna sa ran adadin zai zarta wannnan; wanda zai iya kai wa kimanin Naira biliyan shida,” in ji Adeniyi.
Kazalika, ya bayyana cewa; muna sa ran samar da yawan Tarwadar da za ta kai sama da tan 2000, kafin karshen shekarar 2025.
Bugu da kari, ya bayyana cewa; kungiyar a kowane zango daya na shekara, tana shirya wa masu kiwon Tarwadar horo na musamman, inda sabbin shiga cikin kungiyar ke biyan Naira 2,500, domin yin rijista da su.
Ya ce, kungiyar na raba wa ‘ya’yanta wuraren kiwon Tarwadar, inda ake cazar su Naira 15,000.
Kazalika, bayan mai kiwon ya samar da Tarwada ta farko, kungiyar za ta ba shi, rancen Naira miliyan biyu, inda rancen zai kasance kashi 18 cikin 100 na kudin ruwa, har zuwa karshen shekara daya.
Shi kuwa, wani mai kiwon Tarwadar mai suna Oyinade Matthew Adeneye, wanda kuma yake tafiyar da Kwamin kiwon Tarwadar guda sha biyu, wanda kuma tun a shekarar 2008 yake yin kiwon a yankin ya sanar da cewa; yanzu haka; yana da sama da Tarwada 30,000 wadanda kuma suke kan matakai daban-daban.
A cewarsa, aikin na ‘FISH4ACP’, zai taimaka wajen karfafa samar da ilimin yadda za a rika kula da kiwon Tarwada da kuma magance kalubalen da masu kiwon ke fuskanta na rashin samun riba mai yawa.
Adeneye ya ci gaba da cewa, aikin zai kuma samar da sauyi a fagen kiwon na Tarwada tare kuma da samar da damar samun rancen kudaden yin kiwon.
Manufar aikin na ‘FISH4ACP’ dai, zai kasance wajen bayar da gudunmawar ci gaba da kiwon Tarwadar da kuma samun kudaden shiga.
A yanzu haka, ana gudanar da wannan aiki a kasashe sha biyu, inda ake gudanar da aikin a kasashe tara da ke Nahiyar Afirka biyu, a kuma yankin Caribbean, daya kuma a tekun Pacific, wanda aka zuba kimanin Yuro miliyan 40 tare da kuma karin wasu kudade daga Gwamnatin Kasar Jamus.
A bangaren Nijeriya kuwa, an mayar da hankali ne a fannin na kiwon Tarwada, domin samun riba; wanda kuma aka wanzar da aikin a shiyoyin siyasa shida na fadin kasar nan.
Jihohin da aka wanzar da ayyukan su ne, Jihohin Kudu Maso Yamma, inda ake wanzar da aikin a Jihar Ogun, sai kuma a Kudu Maso Kudu da ake wanzar da aikin a Jihar Delta.
Sauran su ne; Kudu Maso Gabas da kuma Arewa Ta Tsakiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp