HausaTv:
2025-04-30@19:42:44 GMT

Kisan ma’aikatan ceto : MDD ta gargadi Isra’ila game da aikata laifin yaki

Published: 4th, April 2025 GMT

Kwamishinan kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya gargadi Isra’ila game da harin da ya yi sanadin mutuwar ma’aikatan ceto a Gaza yana mai cewa hakan zai iya kasancewa ‘lafin yaki’. Ma’aikatan agaji 15 ne suka ras arayukan a wani kazamin hari da Isra’ila ta kai kan motocin daukar marasa lafiya a Gaza wada ya fiddo a fili irin ” laifuffukan yaki da sojojin Isra’ila suka kwashe tsawon lokaci suna aikatawa a zirin Gaza”.

Kafin hakan dama hukumar kula da hakkin bil adama ta MDD ta amince da kudurin dake kira ga Isra’ila da kada ta aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.

An amince da kudurin ne ranar Laraba yayin taron hukumar na 58, bayan ya samu kuri’un amincewa 27 da na kin amincewa 4, kana kasashe 16 sun kaurace wa kada kuri’ar.

Kudurin ya kuma bayyana takaici game da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isra’ila ta yi, tare da yin kira da ta sauke nauyin dake wuyanta.  

Har ila yau, kudurin ya soki yadda Isra’ila ta yi amfani da yunwa a matsayin wata dabara ta yaki a Gaza, da hana samar da agajin jin kai da kawo tsaiko ga samar da kayayyakin agaji da hana fararen hula abubuwan da suke bukata na rayuwa, kamar abinci da ruwa da lantarki da makamashi da hanyoyin sadarwa.

Ya kuma bayyana damuwa matuka game da kalaman jami’an Isra’ila da ka iya ingiza kisan kiyashi, inda ya bukaci Isra’ila ta sauke nauyin dake wuyanta bisa doka na kare aukuwar kisan kiyashi.

Bugu da kari, kudurin ya gabatar da wasu jerin bukatu ga Isra’ila, ciki har da tabbatar da samar da agajin jin kai ba tare da tangarda ba da gaggauta dawo da tsarin samar da muhimman kayayyakin bukata ga Palasdinawa a Gaza da ba Palasdinawan da suka rasa matsugunansu damar komawa dukkan yankunan zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji