Kisan ma’aikatan ceto : MDD ta gargadi Isra’ila game da aikata laifin yaki
Published: 4th, April 2025 GMT
Kwamishinan kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya gargadi Isra’ila game da harin da ya yi sanadin mutuwar ma’aikatan ceto a Gaza yana mai cewa hakan zai iya kasancewa ‘lafin yaki’. Ma’aikatan agaji 15 ne suka ras arayukan a wani kazamin hari da Isra’ila ta kai kan motocin daukar marasa lafiya a Gaza wada ya fiddo a fili irin ” laifuffukan yaki da sojojin Isra’ila suka kwashe tsawon lokaci suna aikatawa a zirin Gaza”.
Kafin hakan dama hukumar kula da hakkin bil adama ta MDD ta amince da kudurin dake kira ga Isra’ila da kada ta aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.
An amince da kudurin ne ranar Laraba yayin taron hukumar na 58, bayan ya samu kuri’un amincewa 27 da na kin amincewa 4, kana kasashe 16 sun kaurace wa kada kuri’ar.
Kudurin ya kuma bayyana takaici game da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isra’ila ta yi, tare da yin kira da ta sauke nauyin dake wuyanta.
Har ila yau, kudurin ya soki yadda Isra’ila ta yi amfani da yunwa a matsayin wata dabara ta yaki a Gaza, da hana samar da agajin jin kai da kawo tsaiko ga samar da kayayyakin agaji da hana fararen hula abubuwan da suke bukata na rayuwa, kamar abinci da ruwa da lantarki da makamashi da hanyoyin sadarwa.
Ya kuma bayyana damuwa matuka game da kalaman jami’an Isra’ila da ka iya ingiza kisan kiyashi, inda ya bukaci Isra’ila ta sauke nauyin dake wuyanta bisa doka na kare aukuwar kisan kiyashi.
Bugu da kari, kudurin ya gabatar da wasu jerin bukatu ga Isra’ila, ciki har da tabbatar da samar da agajin jin kai ba tare da tangarda ba da gaggauta dawo da tsarin samar da muhimman kayayyakin bukata ga Palasdinawa a Gaza da ba Palasdinawan da suka rasa matsugunansu damar komawa dukkan yankunan zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
Kasashen duniya na ci gaba da yin tir da sabon farmakin soji da Isra’ila ta kaddamar kan Gaza.
Kasashen Biritaniya, Faransa, Italiya, Masar, Jordan, Qatar, Spain, duk sun yi tir da farmakin kan Gaza suna masu cewa zai kara dagula halin kunci da ake ciki.
Kungiyar tarayyar Turai, ta bakin Jami’ar kula da harkokin wajen ta, Kaja Kalas, ta yi kira da a sanyawa Isra’ila takunkumi domin matsa wa gwamnatin lamba ta kawo karshen hare-haren da take kaiwa Gaza, tana mai gargadin cewa al’amuran jin kai na kara ta’azzara.
“Hare-haren da Isra’ila ta kai a Gaza zasu haifar da mummunan sakamako game da halin da ake ciki da karin hasarar rayuka, da barna & hijira na jama’a,” in ji Kalas a kan X.
A jiya ne Sojojin Isra’ila suka kaddamar da sabon farmakin ta kasa mai manufar mamaye birnin Gaza bayan shafe makwanni ana kai hare-haren bama-bamai ba kakkautawa ba a kan wasu manyan gine-gine domin tilastawa Falasdinawa kauracewa gidajensu.
Farmakin ya zo ne jim kadan bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya gana da firaminista Benjamin Netanyahu a kusa da masallacin Al Aqsa da ke gabashin birnin Kudus da aka mamaye.
Tun da farko dai, wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan yankunan Falasdinawa da ke mamaye, Francesca Albanese ta yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa birnin Gaza, tana mai cewa wani bangare ne na shirin Isra’ila na shafe Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci