Kisan ma’aikatan ceto : MDD ta gargadi Isra’ila game da aikata laifin yaki
Published: 4th, April 2025 GMT
Kwamishinan kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya gargadi Isra’ila game da harin da ya yi sanadin mutuwar ma’aikatan ceto a Gaza yana mai cewa hakan zai iya kasancewa ‘lafin yaki’. Ma’aikatan agaji 15 ne suka ras arayukan a wani kazamin hari da Isra’ila ta kai kan motocin daukar marasa lafiya a Gaza wada ya fiddo a fili irin ” laifuffukan yaki da sojojin Isra’ila suka kwashe tsawon lokaci suna aikatawa a zirin Gaza”.
Kafin hakan dama hukumar kula da hakkin bil adama ta MDD ta amince da kudurin dake kira ga Isra’ila da kada ta aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.
An amince da kudurin ne ranar Laraba yayin taron hukumar na 58, bayan ya samu kuri’un amincewa 27 da na kin amincewa 4, kana kasashe 16 sun kaurace wa kada kuri’ar.
Kudurin ya kuma bayyana takaici game da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isra’ila ta yi, tare da yin kira da ta sauke nauyin dake wuyanta.
Har ila yau, kudurin ya soki yadda Isra’ila ta yi amfani da yunwa a matsayin wata dabara ta yaki a Gaza, da hana samar da agajin jin kai da kawo tsaiko ga samar da kayayyakin agaji da hana fararen hula abubuwan da suke bukata na rayuwa, kamar abinci da ruwa da lantarki da makamashi da hanyoyin sadarwa.
Ya kuma bayyana damuwa matuka game da kalaman jami’an Isra’ila da ka iya ingiza kisan kiyashi, inda ya bukaci Isra’ila ta sauke nauyin dake wuyanta bisa doka na kare aukuwar kisan kiyashi.
Bugu da kari, kudurin ya gabatar da wasu jerin bukatu ga Isra’ila, ciki har da tabbatar da samar da agajin jin kai ba tare da tangarda ba da gaggauta dawo da tsarin samar da muhimman kayayyakin bukata ga Palasdinawa a Gaza da ba Palasdinawan da suka rasa matsugunansu damar komawa dukkan yankunan zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
Gwamnatin Amurka ƙarƙashin Donald Trump ta sake sanya Najeriya cikin jerin “Ƙasashe Masu Matsala ta Musamman” saboda zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.
Wannan zargi ya biyo bayan jawabin da Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya yi a taron Majalisar Ɗinkin Duniya a kwanan baya.
Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDPA lokacin taron Shettima ya bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin abin tausayawa, inda ya hi kira da a tabbatar da zaman lafiya ta hanyar kafa ƙasashe biyu masu zaman kansu.
Bayan jawabin nasa, wasu ƙungiyoyi suka fara yaɗa labarin cewa ana yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Najeriya, duk da cewa mutane da dama sun ƙaryata jita-jitar.
A ranar Juma’a, Trump ya wallafa wani rubutu a shafinsa na X, cewa Kiristoci na fuskantar barazana a Najeriya.
Ya yi iƙirarin cewar masu tsattsauran ra’ayi suna yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya .
Ya umarci ɗan Majalisar Amurka, Riley Moore da shugaban kwamitin kasafin kuɗi na Majalisar, Tom Cole, su binciki lamarin, sannan su gabatar masa da rahoto.
Shugaban ya ƙara da cewa ƙasarsa ba za ta zuba ido yayin da irin wannan “ta’addanci” ke faruwa a Najeriya da sauran ƙasashe ba.
Ya lashi takobin cewar Amurka za ta ci gaba da kare Kiristoci a duniya baki ɗaya.
Bayan wannan furuci, wasu sun zargi Trump da amfani da matsalar tsaron Najeriya don samun goyon bayan siyasa.
Har yanzu Gwamnatin Najeriya ba ta yi martani a kan lamarin ba, amma jami’an gwamnati a baya sun bayyana cewa rikice-rikicen da ake fama da su a ƙasar suna da nasaba da ayyukan ta’addanci, fashi, da rikicin ƙabilanci, ba addini ba.
Kalmar “Ƙasa Mai Matsala Ta Musamman” na nufin ƙasashen da Amurka ke ganin suna take haƙƙin ’yancin addini, kuma hakan na iya sa wa ta ƙaƙaba wa Najeriya takunkumai.
Idan ba a manta Najeriya ta fara shiga jerin irin waɗanda ƙasashe tun a shekarar 2020.