Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — Wike
Published: 4th, April 2025 GMT
Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya musanta jita-jitar da ake yaɗawa cewar ya yanke jiki ya faɗi har aka kai shi asibiti a ƙasar waje.
Ya ce wannan ƙarya ce da maƙiyansa na siyasa suka ƙirƙira don kawar da hankalin mutane.
NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta Fitaccen malami Dokta Idris Dutsen Tanshi ya rasuWike, ya yi wannan bayani ne a Abuja a ranar Alhamis yayin da ya kai ziyara wajen wani aiki da ake shirin ƙaddamarwa a watan gobe domin bikin cikar Shugaba Bola Tinubu shekara biyu a mulki.
A wata sanarwa da daraktan yaɗa labaransa, Anthony Ogunleye, ya fitar, Wike ya ce waɗanda ke yaɗa wannan labari suna ƙoƙarin juyar da hankalin jama’a daga batun da tsohon shugaban ma’aikatan Jihar Ribas ya fallasa na yunƙurin saka bam a majalisar dokokin jihar da kuma hari kan kadarorin gwamnati.
“Babu inda na yanke jiki na faɗi, balle har a fitar da ni zuwa ƙasar waje.
“Ko a ranar da Shugaba Tinubu ya yi buɗa-baki kan zagayowar ranar haihuwarsa na halarta.
“Haka kuma, a ranar Sallah na jagoranci mazauna Abuja zuwa taya shi barkar da sallah. Ba zan damu da irin waɗannan jita-jitar siyasa ba, kuma ba za su hana ni aiki ba,” in ji Wike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: karya Siyasa yanke jiki
এছাড়াও পড়ুন:
Trump ya ce zai yi shawara game da batun kafa kasar Falasdinu
Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce zai yi shawara game da yiwuwar amincewa da kafa kasar Falasdinu a matsayin masalaha a yankin Gabas ta Tsakiya.
Trump ya ce zai yi aiki tare da sauran kasashen duniya game da wannan batun.
Ya bayyana hakan ne ga ga manema labarai a kan hanyarsa ta komawa Amurka daga ziyarar da ya kai yankin Gabas ta Tsakiya ranar Litinin, domin sanya hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.
Ko a ranar Litinin ma yayin da yake tsaka da jawabi a majalisar dokokin Isra’ila, wani dan majalisa ya daga wata takarda dake bukatar Trump ya amince da kafuwar kasar Falasdinu.
To saidai jami’an tsaron Isra’ilar sukayi waje da shi daga zauren.
Bukatar kafa kasar Falasdinu na ci gaba da wanzuwa a duniya musamman a kasashen yamma inda ko a baya-bayan nan kasashen duniya da dama sun yi ta kiraye-kiyaren amincewa da kafa kasar Falasdinu a babban taron MDD karo na 80.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Islamic Jihad : jarumtakar ‘yan gwagwarmaya ce ta haifar da sako fursunonin falasdinawa October 14, 2025 Aragchi Yana Uganda Don Halattan Taron Ministocin Kungiyar NAM October 14, 2025 Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata October 14, 2025 Ma’aikatar Harkokin wajen Kasar Iran Ta Yi Tir Da Jawabin Trump A Knesset Ta HKI October 14, 2025 An Gudanar Gagarumar Zanga Zangar Goyon Bayan Falasdinawa A Australia Da Indonasia October 14, 2025 Syria: Busaina Sha’aban Ta Karyata Labaran Da Aka Danganta Ma Ta Na Ganawa Da Jami’an Iraniyawa October 14, 2025 Mahalarta Taron ‘Sherm-Sheikh” Sun Rattaba Hannu Akan Yarjejeniyar Zaman Lafiya October 14, 2025 MDD: Mutane 300,000 Su Ka Gudu Daga Sudan Ta Kudu A 2025 October 14, 2025 Iran Ta Gabatar Da Shawarar Kulla Yarjejeniyar Tausayawa A Tsakanin Matan Duniya October 14, 2025 Larijani: Gagarumar Tarbar Da Aka Yi Wa Fursunonin Falasdinawa Ta Nuna Hakikanin Wanda Ya Sami Nasara October 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci