Aminiya:
2025-07-08@22:06:06 GMT

Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — Wike

Published: 4th, April 2025 GMT

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya musanta jita-jitar da ake yaɗawa cewar ya yanke jiki ya faɗi har aka kai shi asibiti a ƙasar waje.

Ya ce wannan ƙarya ce da maƙiyansa na siyasa suka ƙirƙira don kawar da hankalin mutane.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta Fitaccen malami Dokta Idris Dutsen Tanshi ya rasu

Wike, ya yi wannan bayani ne a Abuja a ranar Alhamis yayin da ya kai ziyara wajen wani aiki da ake shirin ƙaddamarwa a watan gobe domin bikin cikar Shugaba Bola Tinubu shekara biyu a mulki.

A wata sanarwa da daraktan yaɗa labaransa, Anthony Ogunleye, ya fitar, Wike ya ce waɗanda ke yaɗa wannan labari suna ƙoƙarin juyar da hankalin jama’a daga batun da tsohon shugaban ma’aikatan Jihar Ribas ya fallasa na yunƙurin saka bam a majalisar dokokin jihar da kuma hari kan kadarorin gwamnati.

“Babu inda na yanke jiki na faɗi, balle har a fitar da ni zuwa ƙasar waje.

“Ko a ranar da Shugaba Tinubu ya yi buɗa-baki kan zagayowar ranar haihuwarsa na halarta.

“Haka kuma, a ranar Sallah na jagoranci mazauna Abuja zuwa taya shi barkar da sallah. Ba zan damu da irin waɗannan jita-jitar siyasa ba, kuma ba za su hana ni aiki ba,” in ji Wike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: karya Siyasa yanke jiki

এছাড়াও পড়ুন:

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

(ENT) Aikin Hanci , Makogaro da Kunne

(Dental) Hakori

(Fibroid) Qarin mahaifa,

(Urology) Aikin Mafitsara

Asibitin ya zakulo zakakuran likitoci domin gudanar da wannan ayyukan daga yau Litinin 8, ga watan Yuli 2025, ga duk masu bukatar wannan ayyukan, akan farashin kaso 50% cikin 100 shima za a biya.

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu  Asibitin Aminu Kano Ya Musanta Cire Mahaifar Mara Lafiya Ba Tare Da Izini Ba

Hakan na kunshe ne cikin wata sanar da shugaban asibitin Alh Auwal Muhd Lawal ya bayyanawa jaridar Alfijir Labarai a safiyar Litinin.

Lawal yace sun yanke wannan hukuncin ne sakamakon buƙatar da al’umma suke da ita a wannan bangarorin ga kuma yawan da mutane suka yiwa gwamnati shi yasa hukumar gudanarwar Asibitin Kwararru na Best Choice itama taga da cewar bada tata gudummawar domin kara karfafar gwamnati a wannan fannin.

Auwal ya kuma bayyana jin dadinsa ganin yadda al’umma suke ta cin gajiyar bude fiyil kyauta da rage kaso 50% ganin likita tare da manya da kananan ayyukan asibitin da yayi a satin da ya gabata.

Dukkannin waɗannan ayyuka za a fara gudanar da sune a yau Litinin, don haka ga masu irin wadannan matsaloli za su iya zuwa domin a tantancesu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Malaman firamare sun janye yajin aiki a Abuja
  • Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Neman Izinin Jinyar Yahaya Bello
  • NAJERIYA A YAU: Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC — Atiku Ko Peter Obi
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano
  • Sheikh Ibrahim Zakzaky Ya Taya JMI Murnar Nasara A Kan Mikiyanta
  • Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final
  • Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata