Aminiya:
2025-05-24@09:11:27 GMT

Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — Wike

Published: 4th, April 2025 GMT

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya musanta jita-jitar da ake yaɗawa cewar ya yanke jiki ya faɗi har aka kai shi asibiti a ƙasar waje.

Ya ce wannan ƙarya ce da maƙiyansa na siyasa suka ƙirƙira don kawar da hankalin mutane.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta Fitaccen malami Dokta Idris Dutsen Tanshi ya rasu

Wike, ya yi wannan bayani ne a Abuja a ranar Alhamis yayin da ya kai ziyara wajen wani aiki da ake shirin ƙaddamarwa a watan gobe domin bikin cikar Shugaba Bola Tinubu shekara biyu a mulki.

A wata sanarwa da daraktan yaɗa labaransa, Anthony Ogunleye, ya fitar, Wike ya ce waɗanda ke yaɗa wannan labari suna ƙoƙarin juyar da hankalin jama’a daga batun da tsohon shugaban ma’aikatan Jihar Ribas ya fallasa na yunƙurin saka bam a majalisar dokokin jihar da kuma hari kan kadarorin gwamnati.

“Babu inda na yanke jiki na faɗi, balle har a fitar da ni zuwa ƙasar waje.

“Ko a ranar da Shugaba Tinubu ya yi buɗa-baki kan zagayowar ranar haihuwarsa na halarta.

“Haka kuma, a ranar Sallah na jagoranci mazauna Abuja zuwa taya shi barkar da sallah. Ba zan damu da irin waɗannan jita-jitar siyasa ba, kuma ba za su hana ni aiki ba,” in ji Wike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: karya Siyasa yanke jiki

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Kara Haske kan Batun Inganta Sinadarin Uranium Da Zamanta Da Amurka

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bayyana sabbin ci gaban da aka samu a tattaunawar da aka yi a birnin Roma

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya jaddada cewa: Ana gudanar da zagaye na biyar na tattaunawa ba na kai tsaye ba tsakanin tawagar Amurka da na Iran a cikin yanayi na kwarewa.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana a yau Juma’a cewa: Tattaunawar tana gudana cikin kwarewa da kwanciyar hankali, yana mai cewa abin da ake yadawa a kafafen yada labarai hasashe ne da baya da tushe ko inganci kuma baya da bambanci da shaci fadi.

A yau Juma’a da yamma ne aka fara shawarwarin da ba na kai tsaye ba karo na biyar tsakanin Iran da Amurka a hedkwatar wanzar da zaman lafiya ta masarautar Oman da ke birnin Roma fadar mulkin kasar Italiya.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da manzon Amurka na musamman Steve Witkoff ne ke jagorantar shawarwarin da masarautar Oman ke shiga tsakani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda dilolin ƙwaya ke cin karensu ba babbaka a Abuja
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Kara Haske kan Batun Inganta Sinadarin Uranium Da Zamanta Da Amurka
  • Kotu A Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Tsohon Jami’in Kasar Kan Hannu A Kashe-Kashen Rayukan Jama’a
  • Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwadebuwa
  • Ma’aikatar Tsaro Ta Fitar da Rahoton Nasarori Karkashin Shirin “Sabuwar Fata” na Shugaba Tinubu
  • Araghchi: Iran ba za ta tattauna kan batun inganta sinadarin Uranium din ta ba
  • Sin Ta Fitar Da Fim Dake Bayyana Al’amaru Na Gaske Bisa Taken “Gajimare A Doron Kasa” 
  • Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin ZamfaraBabu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara