Ministocin harkokin wajen kasashen AES na gana da Rasha
Published: 4th, April 2025 GMT
Ministocin harkokin wajen kasashen kawacen sahel na AES da ya hada Mali da Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar, na wata ziyarar aiki a kasar Rasha.
Ana sa ran ministocin za su kasance a birnin Moscow a yau Alhamis da gobe Juma’a, don tattaunawa, da zurfafa hulda tsakanin bangarorin biyu, kamar dai yadda aka bayyana cikin wata sanarwar hadin gwiwarsu.
Sanarwar, ta ce shawarwarin da ministocin kasashen kungiyar ta AES za su yi tare da ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergei Lavrov, wani bangare ne na burin shugabannin kasashen uku na yankin sahel da sojoji ke mulki da kasar Rasha, na fadada hadin gwiwa a fannonin siyasa, tattalin arziki da kuma tsaro.
Har ila yau, sassan biyu za su zanta game da batutuwan da suka shafi moriyarsu, ciki har da samar da daidaito a shiyyarsu, da habaka tattalin arziki da tsaron kasashen.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce matakin da gwamnatin Isra’ila ta dauka a kan kasar tamkar shelanta yaki ne.
Araghchi ya bayyana hakan ne a cikin wata wasika da ya aikewa babban sakatare na MDD da kuma shugaban kwamitin sulhu bayan da Isra’ila ta kai munanan hare-hare kan wuraren soji da cibiyoyin nukiliya da kuma wuraren zama wanda ya yi sanadiyar mutuwar wasu manyan kwamandojin dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), masana kimiyyar nukiliya da fararen hula na iran.
“Wadannan ayyuka na zalunci ba wai kawai sun zama babban cin zarafi ne ga ‘yancin kan kasar Iran a matsayinta na mamba mai cin gashin kanta a Majalisar Dinkin Duniya ba, amma kamar yadda dokokin kasa da kasa da dokokin jin kai na duniya, ciki har da yarjejeniyar Geneva, suka tanada wannan na daga cikin ayyukan wuce gona da iri da laifukan yaki.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya sauke nauyin da ke wuyansa, ya yi kakkausar suka ga wannan ta’addanci tare da daukar matakin gaggawa kan Isra’ila.
Ya kara da cewa “Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi aiki da cikakkiyar azama wajen kare ‘yancinta, al’ummarta da kuma tsaron kasarta. Wannan wani hakki ne da ba za a iya tattaunawa da shi ba.”
Daga cikin hare-haren da ta kai, Isra’ila ta kai hari kan Cibiyar Nukiliya ta Natanz da ke tsakiyar kasar Iran, wadda ke aiki karkashin cikakken kulawar Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA), in ji shi.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi gargadin cewa hare-haren ta’addanci na gwamnatin Tel Aviv na jefa rayuwar fararen hular Iran cikin hadari tare da haifar da barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.