Aminiya:
2025-06-15@09:35:33 GMT

APC ta ƙaryata jita-jitar sauya Shettima kafin zaɓen 2027

Published: 4th, April 2025 GMT

Jam’iyyar APC, ta musanta jita-jitar cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na shirin sauya Mataimakinsa, Kashim Shettima, kafin zaɓen 2027.

Jam’iyyar ta ce babu wata matsala tsakaninsu kuma maganar sauya Shettima ba ta da tushe.

Hakeem Baba-Ahmed ya yi murabus daga gwamnatin Tinubu Fitaccen malami Dokta Idris Dutsen Tanshi ya rasu

Daraktan Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Ƙasa, Alhaji Bala Ibrahim, ya shaida wa Aminiya cewa wasu ne ke yaɗa wannan jita-jitar don tayar da ƙura.

“Wannan jita-jita ce kawai marar tushe. Maganganu ne da bai kamata a ɗauke su da muhimmanci ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Ko da a ce akwai wani dalili da zai sa shugaban ƙasa ya sauya mataimakinsa, ba zai iya yin hakan shi kaɗai ba. Dole sai da shawarwari tare da masu ruwa da tsaki.”

Ko da yake APC ba ta bayyana aniyar Tinubu na sake yin takara a karo na biyu ba, magoya bayansa da wasu shugabannin jam’iyya sun fara neman goyon baya don ya sake tsayawa takara a 2027.

Wasu na ganin ya cancanci ya nemi wa’adi na biyu domin kammala ayyukan da ya fara.

A halin yanzu, wasu ’yan siyasa daga yankin Arewa ta Tsakiya suna kira da a ba su tikitin shugaban ƙasa ko mataimaki a zaɓe mai zuwa.

Sun ce tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a 1999, yankin bai taɓa samun shugaba ko mataimakin shugaban ƙasa ba.

Farfesa Nghargbu K’tso, wanda ya wakilci tawagar, ya ce: “Daga cikin yankuna shida na ƙasar nan, Arewa ta Tsakiya da Kudu Maso Gabas ne kaɗai ba su taɓa samar da shugaban ƙasa ko mataimaki ba cikin shekaru 26 da suka gabata. Lokaci ya yi da za a yi adalci da haɗin kai.”

Sai dai Bala Ibrahim, ya mayar da martani cewa buƙatar Arewa ta Tsakiya ba ta da tushe kuma “ta mutu tun kafin ta fara.”

Ya ce yankin bai taka gagarumar rawa a zaɓen da ya gabata ba bare ya nemi irin wannan buƙata, kuma ba yanzu ne lokacin tattauna rabon muƙamai ba, tunda Tinubu bai kammala wa’adinsa na farko ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sauya Mataimaki Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

A wata hira tare da gidan talabijin na Arise, Obi ya ce duk da cewa cire tallafin mai yana da muhimmanci, amma ya kamata a aiwatar da wannan tsari cikin tsari.

Ya ce ya amince cewa tallafin mai yana cike da ta’asa da cin hanci wanda akwai bukatar a kawo karshensa, amma ya yi suka ga hanyoyin da gwamnatin Tinubu take bi, yana bayyana su a matsayin wadanda aka yi ba bisa kwarewa ba.

Obi ya tambayi jagororin kula da kudin da aka ajiye daga cire tallafin, yana cewa, “Tun da aka ce manatallafin man fetur, ana cewa an cire ne saboda ba a so mu dunga ciyo bashi kuma kudaden za su ba da dama wajen zuba jari a muhimman ababen more rayuwa.

‘’Ina biliyoyin kudaden da aka tara? Ina aka zuba su a muhimman yankunan ci gaba? Kowa na sane da muhimman yankunan ci gaba da suka hada da ilimi, lafiya, da fitar da mutane daga talauci. Shin ko daya daga cikin wadannan abubuwan gda uku ya inganta? A’a.’’

Obi ya ce ya kamata a yi musayar farashi mai da masu ruwa da tsaki da kyau ta yadda zai rage tasirin ga matsalolin da ‘yan kasa ke ciki.

Da yake mayar da martini ga Obi, mai taimaka wa shugaban kasa kan batutuwan tsare-tsare, Daniel Bwala, ya bayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a matsayin mutum mai son kansa wanda ba ya da ilimin warware al’amuran da suka shafi tattalin arziki da shugabanci.

Bwala, a cikin wata sanarwa da ya wallafa ta shafinsa na sada zumunta na Tuwita, ya bayyana cewa ya yi mamakin yadda Obi ya yarda da manufofin tattalin arzikin Shugaba Tinubu, musamman kan cire tallafin mai da hada-hadar kudaden waje, amma ya jaddada cewa Obi sauran manyan ‘yan adawa suna neman samun iko ne kawai ko ta wani hali a wannan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • Ya Kamata Ana Kammala Shari’ar Zaɓe Kafin Rantsuwa